19/04/2026
DALILI 16 DA DOLE SAI MUN SAKE ZAƁAR TINUBU A ZANGO NA BIYU
Ni dai kuri'a ta zan bawa Tinubu ne saboda waɗannan dalilan, kuma kaima dole ne ka zabe shi... dalili na 11 shine babban dalili na.
1.
A ranar farko da ya hau karagar mulki, ya dawo da tallafin man fetur.
2.
Ya karɓi mulki a lokacin da man fetur yake N1,400, amma sai da ya maido shi N185.
3.
Ya samu Dala tana kaiwa N1,350 zuwa N1,500, amma yanzu ya mayar da ita N460.
4.
Wutar lantarki tana nan daram, sai dai in kaga dama ka gaji ka kashe ta da kanka idan ka gama aiki.
5.
Ko ta ina manoma suna aikin gonarsu ba tare da fargabar 'yan bindiga ba.
6.
Makiyaya suna ta kiwo a cikin kwanciyar hankali ba tare da tsoron barayin daji ba.
7.
Harkar ilimi tayi nesa saboda babu wanda yake fargabar masu garkuwa da ɗalibai.
8.
Kasuwanci sai ci gaba yake yi, babu matsalar tsadar haraji ko karyewar jari.
9.
Ya tarar da kayayyakin masarufi a cikin tsada da wahala, amma ya hana idonsa bacci har sai da yasa komai yayi arha.
10.
An yi korafi akan Mulkin Muslim-Muslim Ticket, amma yanzu kowa ya gane gaskiya saboda babu waɗanda suke morar mulkin nan kamar Musulmai a ƙasar nan.
11.
Tunda ya hau mulki zuwa yau ba'a kashe kowa ba, kullum ana cikin zaman lafiya da kwanciyar hankali ko ta ina.
12.
Ya tarar da basusuka masu yawa a kan ƙasar nan, amma zuwa yau ya gama biyan komai, ko kobo ba'a bin Najeriya.
13.
Kullum Kudu shinkafa da taliya yake aika musu da shi, mu kuma Arewa kullum manyan ayyuka (Projects) yake kawo mana, wanda zuwa yanzu bamu da matsalar hanyoyi, asibitoci, ko ruwan sha.
14.
Takin noma yayi arha matuƙa, yanzu da N50,000 sai ka sayi buhu huɗu (4).
15.
Shine Shugaban Ƙasa na farko da yafi tausayin talakawa, har yayi ƙoƙarin haɗa kan Gwamnoni a jam'iyyance domin su goya masa baya don a ceto rayuwar talaka.
16.
Dadin dadawa, yanzu kowace irin hanya zaka iya bi da motarka a fadin kasar nan ba tare da fargabar masu garkuwa da mutane ba; babu batun a tare ka, a wulakanta ka, a karbe kudin fansa sannan a kar