30/07/2026
Rundunar 'Yan Sandan Jihar Bauchi ta k**a mutane uku da ake zargi da hannu a wani hari da ya yi sanadin mutuwar wani mutum mai suna Monday Chiroma, mai shekaru 51, a yankin Dandango da ke karamar hukumar Bauchi.
Kakakin Rundunar 'Yan Sandan Jihar Bauchi, SP Nafiu Habib, ya bayyana hakan cikin wata sanarwar manema labarai da ya fitar a madadin Kwamishinan 'Yan Sandan Jihar, Sani-Omolori Aliyu, inda ya ce an k**a waɗanda ake zargin ne bayan samun rahoton harin da ya faru a Dandango.
A cewar sanarwar, lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 11:30 na daren 20 ga Yulin 2026, inda wasu mutane s**a kai wa wasu mutum biyu hari bisa zargin cewa suna da hannu wajen amfani da maita tare da k**a wata matashiya mai suna Jamila Anthony, 'yar Yelwa Bango.
Rundunar ta ce Jamila Anthony mai shekaru 20 ta rasu ne yayin da take karɓar magani a wani asibiti da ke Gudun Hausawa a Bauchi.
Bayan harin, an garzaya da mutanen biyu zuwa Asibitin Koyarwa na Jami'ar Abubakar Tafawa Balewa, ATBUTH, Bauchi, domin samun kulawar likita. Sai dai Monday Chiroma ya rasu, yayin da aka yi wa Yelwa Bango magani sannan aka kwantar da shi.
Bayan samun rahoton lamarin, jami'an 'yan sanda na sashen Yelwa sun gudanar da aikin gaggawa tare da k**a mutane uku da ake zargi, su ne Danjuma Anthony mai shekaru 25, Ayuba Anthony mai shekaru 22, wanda aka fi sani da Babaru, da Christopher Adamu mai shekaru 34.
Rundunar ta ce yayin tambayoyi, waɗanda ake zargin sun amsa hannu a aikata laifin. Ana kuma ci gaba da ƙoƙarin k**a sauran waɗanda ake zargin, waɗanda har yanzu ake nema ruwa a jallo, tare da haɗin gwiwar jami'an Danga Security da al'ummar yankin.
An tura lamarin zuwa Sashen Binciken Manyan Laifuka na Jihar, SCID, Bauchi, domin gudanar da zurfafa bincike da gurfanar da waɗanda ake zargin a gaban kotu.