13/06/2026
A Zamanin Fir'auna A Ƙasar Masar, An Tara Fitattun Masu Sihiri Daga Ko'ina Cikin Daular Domin Su Ƙalubalanci Annabi Musa (AS).
Lokacin Da Taron Ya Cika, Masu Sihirin S**a Jefa Igiyoyinsu Da Sandunansu, S**a Sa Mutane S**a Ga Kamar Macizai Ne Masu Motsi Saboda Sihirinsu.
Sai Allah Ya Umarci Annabi Musa (AS) Da Ya Jefa Sandarsa.
Da Ya Jefa Ta, Sai Ta Rikide Ta Zama Babbar Macijiya Ta Gaskiya, Ba Sihiri Ba, Ba Ruɗi Ba. Nan Take Ta Fara Haɗiye Duk Abinda Masu Sihirin S**a Ƙirƙira Da Sihirinsu.
Allah Maɗaukakin Sarki Yace..
Sai Muka Yi Wahayi Zuwa Ga Musa Cewa: "Ka Jefa Sandarka." Sai Ga Shi Tana Haɗiye Abin Da Suke Ƙirƙirawa Da Ƙarya."
(Suratul A'araf, 7:117)
Da Masu Sihirin S**a Ga Wannan Mu'ujiza, Sai S**a Gane Cewa Abinda Musa (AS) Ya Zo Da Shi Ba Sihiri Bane. Sune S**a Fi Kowa Sanin Iyakar Sihiri, Don Haka S**a Fahimci Cewa Wannan Iko Ya Fito Ne Daga Allah.
Nan Take S**a Faɗi Ƙasa Suna Sujada, Suna Cewa...
"Mun Yi Imani Da Ubangijin Talikai, Ubangijin Musa Da Haruna."
(Suratul A'araf, 7:121–122)
Wannan Babban Lamari Yana Nuna Rinjayen Gaskiya A Kan Ƙarya, Da Kuma Cewa Ikon Allah Yafi Duk Wata Dabara, Yaudara, Ko Sihiri Ƙarfi.
Yana Kuma Koyar Da Mu Cewa Idan Gaskiya Ta Bayyana A Zahiri, Masu Neman Gaskiya Na Haƙiƙa Za Su Karɓe Ta, Koda Kuwa Hakan Zai Sa Su Fuskanci Tsanantawa Ko Haɗari.
Usman Abdurrazaq Gumel 🩺