Kitabu Wassunnah

Kitabu Wassunnah Disussion about islamic view using Quran and hadith

“ Na rantse muku da ALLAH guda ɗaya, babu wani ɗan adam guda ɗaya a duniya, da yayi kwatankwaci, ko ya isa a kamanta shi...
13/06/2026

“ Na rantse muku da ALLAH guda ɗaya, babu wani ɗan adam guda ɗaya a duniya, da yayi kwatankwaci, ko ya isa a kamanta shi, ko wurin zama, ko karatun sa, ko majalisin sa, ko ɗabi'arsa, ace wai iri ɗaya ne da na Manzon ALLAH (ﷺ), babu wannan, saidai ayi koyi dashi (ﷺ). ”

_Dr. Abdallah Usman Gadon Kaya_
( Hafizahullah )

*🟤Ibnul Qayyim R.A yace : Alamar nasara ya zama aiyukan bawa masu kyau yana sakasu a gadon bayansa,amma yana qurawa muna...
13/06/2026

*🟤Ibnul Qayyim R.A yace : Alamar nasara ya zama aiyukan bawa masu kyau yana sakasu a gadon bayansa,amma yana qurawa munanan ayyukansa idanu, Alamun rashin nasara kuma ya sanya munanan ayyukansa a gadon bayansa, yana qurawa kyawawan ayyukansa idanu.🟤*

Allah Ya Tsare Mu.

_🌹🌹Manzon Allah S.A.W yace : Wasu mutane za su zo, wadanda shaidan dayansu take rigayar rantsuwarsa, kuma rantsuwarsa ta...
13/06/2026

_🌹🌹Manzon Allah S.A.W yace : Wasu mutane za su zo, wadanda shaidan dayansu take rigayar rantsuwarsa, kuma rantsuwarsa take rigayar shaidarsa.🌹🌹_

Bukhari

*☘️Ya Ubangiji Ina Roqonka Ka Shiryeni Izuwa Ga Gaskiya Da Izininka, Cikin Abinda Akayi Sa6ani Akansa, Domin Kai Mai Shi...
13/06/2026

*☘️Ya Ubangiji Ina Roqonka Ka Shiryeni Izuwa Ga Gaskiya Da Izininka, Cikin Abinda Akayi Sa6ani Akansa, Domin Kai Mai Shiryarda Wanda Kaso Ne Izuwa Tafarki Madaidaici.🤲*

_🌹🌹An kar6o daga Jabir bn Abdillah R.A, haqiqa Annabi S.A.W yace : Idan mutum yazama sanda yake yin wata magana ya yi waiwaye, to wannan abinda zai fada amana ce.🌹🌹_

Abu Dawud.

_💦Allah S.W.T yace :  {Da 'Yan Gaba Dai Gaba Dai,Wadannan Sune Makusanta}💦_  Alwaaqi'ah...10 - 11. *▶️Ana nufin 'yen gab...
13/06/2026

_💦Allah S.W.T yace : {Da 'Yan Gaba Dai Gaba Dai,Wadannan Sune Makusanta}💦_

Alwaaqi'ah...10 - 11.

*▶️Ana nufin 'yen gaba dai gaba dai wajan aikata alkhairi a duniya, su ne 'yen gaba dai gaba dai wajan shiga aljannah a lahira.*

Assi'idy.

_*🌒بسم الله الرحمن الرحيم🌒*__*Darasinmu na yau, hadisin da ke da ala'ka da Illar Kafirci 01 cikin 03.*_°°_*{Manzon Allaa...
13/06/2026

_*🌒بسم الله الرحمن الرحيم🌒*_
_*Darasinmu na yau, hadisin da ke da ala'ka da Illar Kafirci 01 cikin 03.*_
°
°
_*{Manzon Allaah (ﷺ) ya ce; NI INA BARRANTA DAGA KO WANE MUSULMI WANDA YAKE ZAMA A TSAKANIN ARNA.}*_°
°
```[Sahih Sunani abi Dawud;2645]```
==
==
_Allaah Ya sa mudace. Allaahu a'alam._
~~
~~
```Zaku samemu a shafukanmu na Facebook da whatapp ta adireshin da ke 'kasa👇```
"" ""
"" ""
https://www.facebook.com/sakonninmanzonallah/?referrer=whatsapp
==
==
https://whatsapp.com/channel/0029Vas7BYA4yltUazb8Ni0J
***
***

13/06/2026

A Zamanin Fir'auna A Ƙasar Masar, An Tara Fitattun Masu Sihiri Daga Ko'ina Cikin Daular Domin Su Ƙalubalanci Annabi Musa (AS).

Lokacin Da Taron Ya Cika, Masu Sihirin S**a Jefa Igiyoyinsu Da Sandunansu, S**a Sa Mutane S**a Ga Kamar Macizai Ne Masu Motsi Saboda Sihirinsu.

Sai Allah Ya Umarci Annabi Musa (AS) Da Ya Jefa Sandarsa.

Da Ya Jefa Ta, Sai Ta Rikide Ta Zama Babbar Macijiya Ta Gaskiya, Ba Sihiri Ba, Ba Ruɗi Ba. Nan Take Ta Fara Haɗiye Duk Abinda Masu Sihirin S**a Ƙirƙira Da Sihirinsu.

Allah Maɗaukakin Sarki Yace..

Sai Muka Yi Wahayi Zuwa Ga Musa Cewa: "Ka Jefa Sandarka." Sai Ga Shi Tana Haɗiye Abin Da Suke Ƙirƙirawa Da Ƙarya."

(Suratul A'araf, 7:117)

Da Masu Sihirin S**a Ga Wannan Mu'ujiza, Sai S**a Gane Cewa Abinda Musa (AS) Ya Zo Da Shi Ba Sihiri Bane. Sune S**a Fi Kowa Sanin Iyakar Sihiri, Don Haka S**a Fahimci Cewa Wannan Iko Ya Fito Ne Daga Allah.

Nan Take S**a Faɗi Ƙasa Suna Sujada, Suna Cewa...

"Mun Yi Imani Da Ubangijin Talikai, Ubangijin Musa Da Haruna."

(Suratul A'araf, 7:121–122)

Wannan Babban Lamari Yana Nuna Rinjayen Gaskiya A Kan Ƙarya, Da Kuma Cewa Ikon Allah Yafi Duk Wata Dabara, Yaudara, Ko Sihiri Ƙarfi.

Yana Kuma Koyar Da Mu Cewa Idan Gaskiya Ta Bayyana A Zahiri, Masu Neman Gaskiya Na Haƙiƙa Za Su Karɓe Ta, Koda Kuwa Hakan Zai Sa Su Fuskanci Tsanantawa Ko Haɗari.

Usman Abdurrazaq Gumel 🩺

13/06/2026

*ADDU'AR MU TA RANAR JUMA'A*

Mu karanta *QULHULLAHU (3)* Da Niyyar duk wanda yake da wata buqata Allah ya biya masa ita, don Alfarmar Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallam.

Mu karanta *QULHULLAHU (10)* Ko wacce da Bisimillah Da niyyar Allah ya jiqan Iyayen mu da Malaman Mu, Da Qannin Mu.

KUMA BABU MAI YWAITA YIWA IYAYENSA ADDU'A SAI SALIHIN 'DA

Kuma idan kana son 'ya'yanka su yawaita yi maka Addu'a bayan mutuwarka, to lallai ka yawaita yiwa naka iyayen Addu'a a Lokacin da kana raye.

Mu karanta *QULHUWALLAHU (10)* Ko wacce da Bisimillah da niyyar Allah ya kai ladan acikin Qaburburan mamatan mu Sababbi da wadanda s**a dade yara da manya, maza da mata.

Mu karanta *QULHUWALLAHU (10)* Ko wacce da Bisimillah Idan lokacin mu yayi Allah yasa mu cika da kalmar:
LA'ILAHA ILLALLAH MUHAMMADU RASULULLAH SALLALLAHU ALAIHI WASALLAM.

*WHATSAPP CHANNEL:*
👇👇👇👇👇👇👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaYyAZ7BFLga0zycyw0x

Address

Bauchi
700105

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Kitabu Wassunnah posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Kitabu Wassunnah:

Share