TNC Hausa

TNC Hausa TNC Hausa na kawo muku labarai da rahotanni na gaskiya a fadin duniya

17/02/2026

ABIN MAMAKI BAYA KAREWAđŸ„±

DATTI ASSALAFIY âœđŸ»

Wadannan wasu gungun ‘yan bindiga ne da ke boye a cikin gari, suna gayyatar fulanin daji ‘yan bindiga a kan su zo su sayi mak**an ta'addanci a gurinsu

Har ma suna tallata wa cewa ga bindiga kirar AA (makamin harbo jirgin sama) da alburusai, sannan kuma ga bindiga kirar AK-47 samfurin Rasha, a cikin dakin da suke sayar da mak**an har da fankoki suna kadawa suna basu iska

Subhanallah, wani irin abu ne wannan? Lallai wadannan mutanen dole suna da masu daukar nauyi da ke mara musu baya

Na ga k**ar hasken rana ya shiga cikin wannan bidiyo da 'yan ta'adda s**ayi, idan bincike za'ayi ta sanadin hasken rana da ya shiga bidiyon za'a gano inda wannan gini yake ta hanyar amfani da digital forensics gadgets

‘Yan bindiga na amfani da manyan bindigogi irinsu AA da AK a lokaci guda wasu daga cikin jami'an tsaron mu na amfani da kananun bindigogi wanda da zaran an fara musayen wuta sun dau zafi sun dena aiki sai sun huce

Akwai bindigogi da tankokin yakin da akayi amfani da su tun lokacin yakin Biafra har zuwa yanzu ba'a canzasu daga hannun jami'an tsaron Gwamnati ba, a lokacin da wani dan siyasa shi kadai ya saci kudin da sun haura Naira biliyon dari kuma yana yawon kamfe ba abinda za'a masa

Batun tsaro ya koma siyasa da kasuwanci, Allah Ka dai ne zai iya ceto yankin mu na Arewa

Ubangiji Allah Ka mana maganin abinda ya fi karfin mu

Fiye da Mutum 12 Sun Mutu a Hare-haren Bama-bamai da Harbe-harbe a Arewa maso Yammacin PakistanFiye da mutum goma sha bi...
17/02/2026

Fiye da Mutum 12 Sun Mutu a Hare-haren Bama-bamai da Harbe-harbe a Arewa maso Yammacin Pakistan

Fiye da mutum goma sha biyu, ciki har da jami’an tsaro 11 da yaro guda, sun mutu sak**akon hare-haren bama-bamai biyu da musayar wuta a lardin Khyber Pakhtunkhwa na ƙasar Pakistan.

Harinsa mafi muni ya faru a gundumar Bajaur, inda wata mota dauke da bama-bamai ta tarwatse kusa da shingen tsaro, ta haddasa rushewar gini. A Bannu kuma, fashewar wata babur mai makare da abubuwan fashewa ta kashe mutum biyu tare da jikkata da dama.

Rahotanni sun ce rikicin ya yi sanadin karin mutuwa uku a Shangla yayin artabu da ‘yan tawaye. Hukumomi na zargin kungiyar Tehrik-i-Taliban Pakistan da hannu a yawaitar hare-haren da s**a karu tun 2021.

TNC Hausa

Mataimakin Kakakin Majalisar Wakilai, Benjamin Kalu, ya yi kira ga al’ummar Jihar Abia da su marawa Bola Tinubu baya a z...
16/02/2026

Mataimakin Kakakin Majalisar Wakilai, Benjamin Kalu, ya yi kira ga al’ummar Jihar Abia da su marawa Bola Tinubu baya a zaben 2027

TNC Hausa

Wata mata mai suna Sonia Cristal Jimenez, mai shekaru 38, na fuskantar tuhuma a jihar New Mexico bayan ana zarginta da t...
16/02/2026

Wata mata mai suna Sonia Cristal Jimenez, mai shekaru 38, na fuskantar tuhuma a jihar New Mexico bayan ana zarginta da tsunduma jaririyarta a cikin tankin bandakin (toilet ) bayan ta haihu.

‘Yan sanda sun ce ta isa asibiti ba tare da jariri ba, lamarin da ya tayar da zargi. Bincike ya nuna jaririyar ta shaki sinadarin ruwa na bandakin kafin mutuwarta. Ana tsare da wannan mata ba tare da beli ba, yayin da ake ci gaba da shari’a.

Netanyahu Ya Bukaci Rushe Shirin Nukiliyar Iran Cikin Duk Wata Yarjejeniya da AmurkaFiraministan Isra’ila, Benjamin Neta...
16/02/2026

Netanyahu Ya Bukaci Rushe Shirin Nukiliyar Iran Cikin Duk Wata Yarjejeniya da Amurka

Firaministan Isra’ila, Benjamin Netanyahu, ya ce duk wata yarjejeniya tsakanin Amurka da Iran dole ta hada da rusa dukkan kayayyakin da Iran ke amfani da su wajen tace sinadarin nukiliya.

Ya bayyana hakan ne yayin da ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi, ke shirin zagaye na biyu na tattaunawar nukiliya da Amurka a Geneva. Netanyahu ya kuma bukaci a dakatar da shirye-shiryen mak**ai masu linzami tare da tabbatar da cikakken bincike mai tsauri.

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya ce har yanzu babu matsaya ta karshe, amma ya nace a ci gaba da tattaunawa. Iran ta musanta neman makamin nukiliya, tana mai cewa a shirye take ta tattauna idan za a sassauta mata takunkumi.

TNC Hausa

Majalisar gudanarwar ta jami'ar Abuja, wadda yanzu ake kira Yakubu Gowon University, ta amince da nadin sabbin Mataimaka...
15/02/2026

Majalisar gudanarwar ta jami'ar Abuja, wadda yanzu ake kira Yakubu Gowon University, ta amince da nadin sabbin Mataimakan Shugaban Jami’a biyu.

An nada Farfesa Rosemary Udeozor a matsayin Mataimakiyar Shugaba mai kula da harkokin ilimi, yayin da Farfesa Muhammad Ndagi zai rike bangaren gudanarwa. Nadin ya fara aiki daga 13 ga Fabrairu na tsawon shekaru biyu.

Majalisar ta kuma tsawaita wa’adin rikon mukamin Rajista ga Malam Sambo Mohammed har sai an yi zabe.

TNC Hausa

2027 Kudu maso Gabas Za Ta Bai wa Tinubu Kashi 90 cikin dariMinistan Ayyuka, David Umahi, ya bayyana cewa yankin Kudu ma...
15/02/2026

2027 Kudu maso Gabas Za Ta Bai wa Tinubu Kashi 90 cikin dari

Ministan Ayyuka, David Umahi, ya bayyana cewa yankin Kudu maso Gabas zai bai wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu kusan kashi 90 cikin 100 na kuri’unsa a zaben 2027.

Ya yi wannan bayani ne yayin duba aikin titin Enugu–Port Harcourt a Alaoji, inda ya ce yankin ya amfana da manyan ayyuka da nade-nade a gwamnatin yanzu. Umahi ya bukaci al’ummar yankin su rungumi siyasa domin cigaban yankinsu

TNC Hausa

Hukumar Yaki da Cin Hanci ta Kasar Ukraine (NABU) ta k**a tsohon Ministan Mak**ashi na kasar, German Galushchenko, yayin...
15/02/2026

Hukumar Yaki da Cin Hanci ta Kasar Ukraine (NABU) ta k**a tsohon Ministan Mak**ashi na kasar, German Galushchenko, yayin da yake kokarin tsallaka iyakar kasar.

TNC Hausa

Kungiyar Gwamnonin Jihohin Kudu ta jajanta wa gwamnati da al’ummar Jihar Kano bisa gobarar da ta tashi a wata babbar kas...
15/02/2026

Kungiyar Gwamnonin Jihohin Kudu ta jajanta wa gwamnati da al’ummar Jihar Kano bisa gobarar da ta tashi a wata babbar kasuwa a Kano, wadda ta lalata dukiyoyi na biliyoyin naira tare da shafar fiye da kasuwanci 1,000.

A cikin sakon ta’aziyya, gwamnonin sun bayyana alhininsu kan asarar dukiya da kuma tasirin da lamarin ya yi ga ‘yan kasuwa da iyalansu. Sun kuma bukaci a dauki matakan da s**a dace domin tallafa wa wadanda abin ya shafa tare da inganta hanyoyin kariya daga gobara a kasuwanni.

Sun jaddada muhimmancin hadin kai tsakanin jihohi domin rage irin wadannan hadurra da kuma gaggauta farfado da harkokin tattalin arzikin da gobarar ta shafa.

TNC Hausa

Lauya Ya Bukaci DSS da ONSA Su Binciki El-Rufai Kan Zargin Satar Wayar NSAWani lauya, Pelumi Olajengbesi, ya bukaci Huku...
15/02/2026

Lauya Ya Bukaci DSS da ONSA Su Binciki El-Rufai Kan Zargin Satar Wayar NSA

Wani lauya, Pelumi Olajengbesi, ya bukaci Hukumar Tsaron Farin Kaya (DSS) da Ofishin Mai Bai wa Shugaban Kasa Shawara Kan Tsaro (ONSA) su binciki tsohon gwamnan Kaduna, Nasir El-Rufai, bisa zargin cewa ya amince da samun bayanan tattaunawar wayar NSA.

A wata hira da ya yi a shirin Prime Time na Arise Television, El-Rufai ya ce “wani ya satar” wayar Nuhu Ribadu, inda ya ji tattaunawar da ake zargin NSA din ya bayar da umarnin k**a shi.

Olajengbesi ya bayyana cewa lamarin ba batun siyasa ko cece-kuce ba ne, illa zargi ne mai tsanani da ke da alaka da tsaron kasa da kuma mutuncin tsarin gwamnati. Ya ce wajibi ne hukumomin tsaro su gudanar da cikakken bincike domin tabbatar da gaskiya.

TNC Hausa

Kungiyar Kwankwaso/Obi Ta Ce Kudirin Takunkumin Amurka Kan Kwankwaso Siyasa CeKungiyar goyon bayan Kwankwaso/Obi ta soki...
15/02/2026

Kungiyar Kwankwaso/Obi Ta Ce Kudirin Takunkumin Amurka Kan Kwankwaso Siyasa Ce

Kungiyar goyon bayan Kwankwaso/Obi ta soki wani kudirin doka a Majalisar Dokokin Amurka da ake cewa zai kakaba takunkumi kan Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, tana mai cewa matakin siyasa ne da aka tsara domin rage tasirinsa gabanin zaben 2027.

A wata sanarwa da jagoran kungiyar, Abba Sadauki Gwale, ya fitar, ya ce kudirin na neman hana masa biza ya zama katsalandan cikin harkokin siyasar Najeriya. Kungiyar ta kuma yi zargin cewa babu hujja karara da ke danganta Kwankwaso da zarge-zargen da aka ambata.

Ta bukaci kasashen waje su mutunta ‘yancin Najeriya tare da barin tsarin dimokuradiyya ya gudana ba tare da tsoma baki ba.

TNC Hausa

Hukumar Kwastam ta k**a fakiti 22 na hodar iblis wanda darajarsu ta kai kusan naira biliyan 1, a hanyar Badagry, jihar L...
15/02/2026

Hukumar Kwastam ta k**a fakiti 22 na hodar iblis wanda darajarsu ta kai kusan naira biliyan 1, a hanyar Badagry, jihar Lagos

An mika kayan ga National Drug Law Enforcement Agency a ranar Juma’a, bayan aikin da rundunar Seme ta gudanar da misalin karfe 3:00 na asubahin 10 ga Fabrairu.

Shugaban Kwastam, Adewale Adeniyi, ya ce k**a kayan ya nuna karfafa matakan sa ido da hadin gwiwar hukumomin tsaro wajen yaki da safarar miyagun kwayoyi.

TNC Hausa

Address

Bauchi

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when TNC Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share