17/10/2025
LABARI DA DUMI DUMIN
KAUTAL PULAAKU
ƘUNGIYAR FULBE TA NAJERIYA
SANARWA GA AL'UMMA
An jawo hankalinmu kan labarin ƙarya da ake yadawa cewa tsoffin shugabannin Miyetti Allah Kautal H**e na jihohin Bauchi, Taraba da Adamawa an kore su daga mukamansu ta hannun shugaban ƙasa na Miyetti Allah Kautal H**e Bello Bodejo.
Wannan labarin na bogi ne, an shirya shi ne domin bata sunan waɗannan shugabanni da tuni sun yi murabus da kansu sun bar Kautal H**e, kuma sanarwar murabus ɗin nasu an wallafa ta a shafukan sada zumunta na ƙungiyar Kautal Pulaaku Fulbe Association of Nigeria.
Shugabannin uku da s**a sauka daga mukamansu sun kuma shiga Kautal Pulaaku Fulbe Association nan da nan, yanzu suna mai da hankali ne kan sabbin shirye-shiryensu na ƙungiyar domin inganta tattalin arziki, zamantakewa, siyasa da tsaron Fulani marasa galihu da masu rauni a yankunansu, don ganin an ingantawa makiyaya rayuwarsu sun amfana da romon dimokoradiyya ta fannin samar masu Ruwan Sha nasu, Dana dabbobin su, inganta ilimin yayan su, koya musu kiwon Zamani da sauran su a fadin ƙasa baki ɗaya.
Kautal Pulaaku Fulbe Association of Nigeria ba ta fito don yin gaba ko yaƙi da wata ƙungiya ba. Maimakon haka, ƙungiyar za ta mai da hankali wajen haɗa kai da sauran ƙungiyoyin Fulbe da waɗanda ba Fulbe ba domin inganta rayuwar makiyaya a fadin ƙasar nan.
Sai dai, ƙungiyar ba za ta lamunci farautar mutanenta , nuna wariya, barazana ko kai hari ga membobin ta, ko mutuncin ƙungiyar ba.
Muna kira ga shugabannin Miyetti Allah Kautal H**e da su mai da hankalisu kan shirye-shiryen ƙungiyarsu maimakon shiga rikici da ƙungiyoyin Fulbe masu son zaman lafiya da cigaban makiyaya, domin irin waɗannan abubuwa na iya lalata martabar ƙungiyar da shugabancinta.
Kautal Pulaaku Fulbe Association of Nigeria na kira ga dukkan mambobinta da su ci gaba da mai da hankali, kada su bari wani mutum ko ƙungiya su karkatar da su daga hanyar da ƙungiyar ta bi don gina martaba da mutuncin Fulbe.
Haruna Idris Bayero,
P.R.O
Suleiman Dungal
Director Media
Nura shehu
Director media na bauchi state 
Kautal Pulaaku Fulbe Association of Nigeria.