22/08/2026
Cikin Hotuna: Yadda Aka gudanar da Zagayen Maulidin Annabi Muhammad (S.A.W) a Funtua
An fara gudanar da Zagayen Maulidin Annabi Muhammad Sallallahu Alaihi Wasallam a garin Funtua, Jihar Katsina, inda dubban al’ummar Musulmi s**a fito domin halartar wannan gagarumin taro na tunawa da fiyayyen halitta.
Mahalarta taron sun fito cikin farin ciki da annashuwa, suna bayyana ƙauna da girmamawa ga Manzon Allah (S.A.W), tare da yin salati da yabo gare shi.
Zagayen ya kasance cikin yanayi na haɗin kai da zumunci, inda mutane daga sassa daban-daban s**a taru domin gudanar da bukukuwan Maulidi tare da tunawa da kyawawan halaye, koyarwa da tarihin rayuwar Annabi Muhammad (S.A.W).
Haka kuma, an gudanar da zagayen ne cikin yanayi na nishaɗi da farin ciki, yayin da mahalarta ke ɗauke da tutoci da alamomin Maulidi, suna bayyana farin cikinsu da kuma ƙaunar da suke yi wa fiyayyen Halitta.
Wannan zagaye ya kuma kasance wata dama ga al’umma wajen sabunta tunani kan koyarwar Manzon Allah (S.A.W), da ƙarfafa zumunci da haɗin kai tsakanin al’ummar Musulmi.