
30/08/2025
Tarihi ya maimaita kanshi
🤔🤔🤔🤔🤔🤔🤔🤔🤔
Yadda tarihi ke maimaita kansa. 😱😞
Mahaifin Dan Damisa ya rasu a irin wannan hali, an kashe shi aka bar shi cikin jini bayan ya addabi mutanen zamaninsa. Kamar yadda shima dan damisa ya zamo sanadiyyar rasa rayukan mutane da yawa ta hanyar dabanci ,wasu suna kiran sa dan zaki a dalilin baban sa wasu kuma dan damisa .
Dabi’ar shahara ta rashin kirki da ta sauka ga ɗansa. Mahaifinsa ya mutu a ranar da aka haifi Dan Damisa, yaci wannan sunan ne after his father ,
bai taɓa ganin mahaifinsa da rai ba. Abin mamaki kuma a cikin juyin al’amura, matarsa ta haifi jaririya, kwana hudu kafin a tabbatar da rasuwarsa , yar sa za ta taso itama bata san mahaifinta ba kenan.
Ubangiji Allah ya raya yarinyar ya shirya ta akan tafarkin maaiki rasulullah .
Wannan abin tsoro ne.
Masu cewa itama zata gaji uban ta .
Bama fatan hakan shi yasa muke nema mata addu'ar mutane , wata kila baki mai albarka zai iya cewa amin.