ZT Kebbi News

ZT Kebbi News An bud'e wannan kafa ce domin samar muku da LABARAI Sahihai, hirarraki dama bayanan abinda duniya take ciki. Contact:07066688836

SHIRIN RANA• Hukumomi a Najeriya sun fara kafa na’urorin inganta tsaro na CCTV a birnin Jos, babban birnin Jihar Filato,...
27/08/2026

SHIRIN RANA

• Hukumomi a Najeriya sun fara kafa na’urorin inganta tsaro na CCTV a birnin Jos, babban birnin Jihar Filato, domin yaki da ‘yan ta’adda.

• A daidai lokacin da aka fara yakin neman zabe a Najeriya, al’ummar Nijar, wadda ke makwabtaka da Najeriya, sun fara tofa albarkacin bakinsu kan bambancin da ke tsakanin mulkin dimokuradiyya da mulkin soja a kasarsu.

• A kasar Ghana, masu ruwa da tsaki sun bukaci a fara aiwatar da dokar haramta bangar siyasa, shekaru bakwai bayan rattaba hannu kan dokar.

• A Jamhuriyar Dimokuradiyyar Kwango, dalibai na cikin zullumi game da komawa karatu bayan dogon hutu, sak**akon barkewar cutar Ebola.

Muna tafe da shirin Siyasa da Al’adu, Wasiku da kuma Ra’ayoyinku. Khadijah Ahmad Rufai ce za ta jagoranci gabatar da shirin.

Harshen Hausa ya kusan mamaye duka fannonin sadarwa a yankin arewacin Najeriya.Ana magana da harshen a ƙauyuka da garuru...
27/08/2026

Harshen Hausa ya kusan mamaye duka fannonin sadarwa a yankin arewacin Najeriya.

Ana magana da harshen a ƙauyuka da garuruwa da kasuwanni da makarantu da kafafen yaɗa labarai da sauran hulɗoɗin yau da kullum.

Wannan ya sanya Hausa ta zama harshe mafi rinjaye da mutane daga ƙabilu daban-daban ke amfani da shi wajen mu'amala da juna wanda hakan ya saka wasu ƙananan harsunan asali da dama ke fuskantar barazanar ɓacewa daga gare shi.

Dalilin haka ne BBC ta tuntuɓi Dakta Ibrahim Ahmed Birnin Gwari, malami a shashen nazarin harsunan Najeriya da kimiyyar harshe a jami'ar Kaduna domin samun ƙarin haske kan wannan batu.

Da Dumi Dumi: Bazan Goyi Bayan Atiku Abubakar ba Saboda Inada Tabbacin Zai Dawo Da Tallafin Man Fetur Din Kamar yadda Ya...
27/08/2026

Da Dumi Dumi: Bazan Goyi Bayan Atiku Abubakar ba Saboda Inada Tabbacin Zai Dawo Da Tallafin Man Fetur Din Kamar yadda Ya Fadi Koda Ko Menene Zaifaru, Nasanshi Farin Sani, Mutum ne Wanda Baida Tsoro, Nikuma Nasan Dawo Da Tallafin Man Fetur Zai Karya Attajirai Da Dama, Kuma Talakawa Suna Amfana Dasu~ Inji Obasanjo.

Abdulnasir Abubakar Silami

A yau jahar Kebbi Ta Cika Shekaru 35.A ra’ayinka, wace gwamnati ce ta kawo wa Jihar Kebbi ci gaba mafi yawa?Ku rubuta ma...
27/08/2026

A yau jahar Kebbi Ta Cika Shekaru 35.
A ra’ayinka, wace gwamnati ce ta kawo wa Jihar Kebbi ci gaba mafi yawa?

Ku rubuta mana sunan gwamnatin a Comment Section. 👇

Daga Nagari fm

Uwargidan Shugaban Ƙasa, Sanata Oluremi Tinubu, ce ta ƙaddamar da shirin a ranar Laraba, 26 ga Agusta, 2026, a Fadar Shu...
27/08/2026

Uwargidan Shugaban Ƙasa, Sanata Oluremi Tinubu, ce ta ƙaddamar da shirin a ranar Laraba, 26 ga Agusta, 2026, a Fadar Shugaban Ƙasa da ke Abuja.

Cutar diphtheria mai nasaba da numfashi ta kashe yara a KanoMajalisar Dokokin Jihar Kano ta yi kira ga Gwamna Abba Yusuf...
27/08/2026

Cutar diphtheria mai nasaba da numfashi ta kashe yara a Kano

Majalisar Dokokin Jihar Kano ta yi kira ga Gwamna Abba Yusuf da ya ɗauki matakin gaggawa don dakile barkewar cutar diphtheria mai nasaba da numfashi da yanzu haka ta kashe yara da ba a san adadinsu ba a yankin ƙaramar Hukumar Rano a jihar ta Kano.

Wallafawa ranar: 27/08/2026 - 11:09
Chanzawa ranar: 27/08/2026 - 11:27

Ko me ya sa batun tallafin man fetur ya janyo cece-kuce a yakin neman zaben Najeriya na 2027?
27/08/2026

Ko me ya sa batun tallafin man fetur ya janyo cece-kuce a yakin neman zaben Najeriya na 2027?

Mutumin da ake zargi da kitsa harin ranar 11 ga watan Satumban 2001 a Amurka, Khalid Sheikh Mohammed zai gurfana a gaban...
27/08/2026

Mutumin da ake zargi da kitsa harin ranar 11 ga watan Satumban 2001 a Amurka, Khalid Sheikh Mohammed zai gurfana a gaban ƙuliya a watan Yunin 2028, fiye da shekara 25 bayan abin da gwamnatin Amurka ta kira ''harin ta'addanci mafi muni da aka kai cikin ƙasar a tarihi''.

Alƙalin kotun sojin ya yanke hukuncin cewa za a fara shari'ar ne nan da shekara biyu domin buƙatar masu gabatar da ƙara ta neman a fara shari'ar a 2027 ya yi kusa sosai.

Khalid Mohammed ya nemi a cimma yarjejeniyar da za ta bashi damar amsa laifin da ake zargin shi da aikatawa yayin da shi kuma za a bashi tabbacin samun hukuncin da ba zai haɗa da kisa ba, amma wata kotun ɗaukaka ƙara ta tarayya ta yi watsi da wannan buƙatar. A 2003 aka k**a shi, yayin da aka tsare shi a sansanin Guantanamo Bay tun daga watan Satumban 2006.

A baya, Khalid Sheikh Mohammed ya taɓa amsa cewa shi ne ya kitsa harin ranar 11 ga watan Satumban 2001 tun daga farko har ƙarshe.

Shugaban Hukumar Yaƙi da Cin Hanci da Rashawa ta Najeriya (EFCC), Ola Olukoyede, ya ce hukumar za ta ɗaukaka ƙara kan hu...
27/08/2026

Shugaban Hukumar Yaƙi da Cin Hanci da Rashawa ta Najeriya (EFCC), Ola Olukoyede, ya ce hukumar za ta ɗaukaka ƙara kan hukuncin kotu da ya yi watsi da ƙoƙarin ƙwace wasu kadarori tara da ake dangantawa da tsohon Babban Lauyan Gwamnatin Tarayya, Abubakar Malami.

Olukoyede ya bayyana hakan ne ranar Laraba yayin da yake gabatar da jawabi a wani taro a Jami’ar Cambridge da ke Birtaniya.

Ya ce binciken EFCC ya gano kadarori 57 da ake dangantawa da Malami. A cewarsa, kotu ta amince da ƙwace 48 daga cikin kadarorin, yayin da ta yi watsi da buƙatar ƙwace sauran tara da ke jihohin Kebbi da Kaduna.

Shugaban EFCC ya ce hukumar ba za ta tsaya nan ba, domin za ta ɗaukaka ƙara domin neman ƙwace sauran kadarorin tara.

Malami Ya Ƙaddamar da Kwamitin Yaƙin Neman Zaɓen ADC Mai Mambobi Sama da 600 A Jihar KebbiƊan takarar Gwamnan Jihar Kebb...
27/08/2026

Malami Ya Ƙaddamar da Kwamitin Yaƙin Neman Zaɓen ADC Mai Mambobi Sama da 600 A Jihar Kebbi

Ɗan takarar Gwamnan Jihar Kebbi a ƙarƙashin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC), tsohon Babban Lauyan Tarayya kuma Ministan Shari’a, Abubakar Malami, SAN, ya ƙaddamar da Darakta-Janar da sama da mambobi 600 na kwamitin yaƙin neman zaɓen jam’iyyar a jihar.

Malami ya ƙaddamar da kwamitin ne a ranar Laraba a Birnin Kebbi, a wani taro da ya nuna fara wani sabon mataki na yaƙin neman zaɓe, haɗa kan magoya baya da kuma wayar da kan jama’a a faɗin ƙananan hukumomi 21 na jihar.

Sanarwar ƙaddamar da kwamitin ta fito ne daga Mohammed Bello Doka, Mataimaki na Musamman kan Harkokin Yaɗa Labarai na Malami.

Da yake jawabi yayin bikin, Malami ya bayyana cewa kafa kwamitin bai tsaya ga sanar da naɗe-naɗe kawai ba, sai dai mataki ne na gina ingantaccen tsari na siyasa daga tushe, wanda zai haɗa kan dukkan ’yan takarar ADC a jihar.

Ya ce kwamitin zai kasance wani tsari na haɗin gwiwa da zai mayar da hankali wajen isar da saƙon jam’iyyar ga al’umma da kuma tabbatar da cewa ’yan takarar jam’iyyar sun samu cikakkiyar damar tuntuɓar masu zaɓe a sassan jihar.

Malami ya ce an tsara tsarin kwamitin ne da gangan domin ya nuna bambancin al’ummar Jihar Kebbi, inda aka haɗa maza da mata daga ƙauyuka da garuruwa daban-daban, ƙananan hukumomi, yankunan Sanata da kuma al’ummomi masu bambancin ra’ayi da tarihi.

Ya ce hakan na nuna ƙudurin ADC na tabbatar da cewa kowane sashe na Jihar Kebbi yana da murya kuma ana sauraron sa a cikin tafiyar siyasar jam’iyyar.

A yayin bikin, Malami ya kuma yaba wa ’yan takarar Sanata na jam’iyyar, ciki har da Janar Aminu Bande, wanda ke neman kujerar Sanata mai wakiltar Kebbi ta Tsakiya; Garba Maidoki, ɗan takarar Kebbi ta Kudu; da Chiroman Kabi, Alhaji Mera, wanda ke neman kujerar Kebbi ta Arewa.

Ya ƙara da cewa ’yan takarar Majalisar Wakilai, Majalisar Dokokin Jiha da sauran kujerun zaɓe suma suna cikin tsarin yaƙin neman zaɓen ADC a jihar.

Tsohon Ministan Shari’ar ya buƙaci mambobin kwamitin da su guji ƙabilanci, bangaranci da kuma rikicin cikin gida, Yana mai jaddada cewa dole ne kwamitin ya kasance k**ar iyali guda na siyasa.

Malami ya ce yaƙin neman zaɓen ADC ba na mutum ɗaya ba ne ko kuma na neman wata kujera guda ɗaya, sai dai tafiya ce da ta shafi dukkan ’yan takarar jam’iyyar, tun daga kujerar gwamna har zuwa Majalisar Dokokin Jiha.

Ya buƙaci mambobin kwamitin da su yi aiki tare cikin haɗin kai, domin tabbatar da nasarar dukkan ’yan takarar ADC a zaɓen 2027.

KBC Hausa

Address

Birnin Kebbi
Birnin-Kebbi

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when ZT Kebbi News posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Shortcuts

Share

Category