27/08/2026
Malami Ya Ƙaddamar da Kwamitin Yaƙin Neman Zaɓen ADC Mai Mambobi Sama da 600 A Jihar Kebbi
Ɗan takarar Gwamnan Jihar Kebbi a ƙarƙashin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC), tsohon Babban Lauyan Tarayya kuma Ministan Shari’a, Abubakar Malami, SAN, ya ƙaddamar da Darakta-Janar da sama da mambobi 600 na kwamitin yaƙin neman zaɓen jam’iyyar a jihar.
Malami ya ƙaddamar da kwamitin ne a ranar Laraba a Birnin Kebbi, a wani taro da ya nuna fara wani sabon mataki na yaƙin neman zaɓe, haɗa kan magoya baya da kuma wayar da kan jama’a a faɗin ƙananan hukumomi 21 na jihar.
Sanarwar ƙaddamar da kwamitin ta fito ne daga Mohammed Bello Doka, Mataimaki na Musamman kan Harkokin Yaɗa Labarai na Malami.
Da yake jawabi yayin bikin, Malami ya bayyana cewa kafa kwamitin bai tsaya ga sanar da naɗe-naɗe kawai ba, sai dai mataki ne na gina ingantaccen tsari na siyasa daga tushe, wanda zai haɗa kan dukkan ’yan takarar ADC a jihar.
Ya ce kwamitin zai kasance wani tsari na haɗin gwiwa da zai mayar da hankali wajen isar da saƙon jam’iyyar ga al’umma da kuma tabbatar da cewa ’yan takarar jam’iyyar sun samu cikakkiyar damar tuntuɓar masu zaɓe a sassan jihar.
Malami ya ce an tsara tsarin kwamitin ne da gangan domin ya nuna bambancin al’ummar Jihar Kebbi, inda aka haɗa maza da mata daga ƙauyuka da garuruwa daban-daban, ƙananan hukumomi, yankunan Sanata da kuma al’ummomi masu bambancin ra’ayi da tarihi.
Ya ce hakan na nuna ƙudurin ADC na tabbatar da cewa kowane sashe na Jihar Kebbi yana da murya kuma ana sauraron sa a cikin tafiyar siyasar jam’iyyar.
A yayin bikin, Malami ya kuma yaba wa ’yan takarar Sanata na jam’iyyar, ciki har da Janar Aminu Bande, wanda ke neman kujerar Sanata mai wakiltar Kebbi ta Tsakiya; Garba Maidoki, ɗan takarar Kebbi ta Kudu; da Chiroman Kabi, Alhaji Mera, wanda ke neman kujerar Kebbi ta Arewa.
Ya ƙara da cewa ’yan takarar Majalisar Wakilai, Majalisar Dokokin Jiha da sauran kujerun zaɓe suma suna cikin tsarin yaƙin neman zaɓen ADC a jihar.
Tsohon Ministan Shari’ar ya buƙaci mambobin kwamitin da su guji ƙabilanci, bangaranci da kuma rikicin cikin gida, Yana mai jaddada cewa dole ne kwamitin ya kasance k**ar iyali guda na siyasa.
Malami ya ce yaƙin neman zaɓen ADC ba na mutum ɗaya ba ne ko kuma na neman wata kujera guda ɗaya, sai dai tafiya ce da ta shafi dukkan ’yan takarar jam’iyyar, tun daga kujerar gwamna har zuwa Majalisar Dokokin Jiha.
Ya buƙaci mambobin kwamitin da su yi aiki tare cikin haɗin kai, domin tabbatar da nasarar dukkan ’yan takarar ADC a zaɓen 2027.
KBC Hausa