20/08/2026
Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, kuma ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar ADC, Atiku Abubakar, ya yi alƙawarin dawo da tallafin man fetur a Najeriya idan ya lashe zaɓen shugaban ƙasa na shekarar 2027.
Atiku ya bayyana hakan ne yayin wani zaman Facebook Live, inda yake amsa tambayoyi kan cire tallafin man fetur da kuma tasirin matakin ga al’ummar ƙasar.
Ya ce da farko bai yi adawa da cire tallafin man fetur ba, amma daga baya ya sauya matsayinsa, yana mai tambayar yadda aka yi amfani da kuɗin da aka samu sakamakon cire tallafin.
Ya ce: “Da farko ban yi adawa da cire tallafin man fetur ba. Amma yanzu da aka cire shi, ina kuɗin yake? Ina aka kashe kuɗin tallafin? Shin an yi amfani da shi wajen inganta kiwon lafiya, ilimi ko tsaro?”
Atiku ya ƙara da cewa, “Idan na lashe zaɓen shugaban ƙasa, zan dawo da tallafin man fetur. Kuma duk wanda ya sace kuɗaɗen tallafin Najeriya, dole ne ya dawo da su.”
Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya sanar da cire tallafin man fetur a ranar 29 ga Mayu, 2023, a lokacin rantsar da shi a matsayin shugaban ƙasa.
Matakin ya haifar da ƙarin farashin man fetur, wanda kuma ya jawo tashin farashin sufuri, abinci da sauran kayayyaki da ayyuka.
Shugaba Tinubu ya kare matakin, yana mai cewa tallafin ya yi tsada sosai ga ƙasar, kuma gwamnati ba za ta iya ci gaba da ɗaukar nauyinsa ba.