24/02/2026
YADDA MUKAYI DA NZEOGWU BAYAN YA KASHE SARDAUNA INJE MARIGAYI SHEIKH ABUBAKAR GUMI...
K**ar karfe hudu na asuba ranar juma'a aka bugomun waya bayan na dauka sai naji ministan ilimi be na Arewa Alhaji Isa Kaita. Ya cemun sojoji fa sun yi Juyin mulki, har ankai ma gidan Sardauna hari kamar yadda yace mun duk manyan jami'an gwamnati sun buya. Yace mun ya yi magana da Hassan Katsina, amma Hassan dai a lokacin yace mai babu abun da zai iyayi. Hassan yace mai a wannan lokacinma yana ganawane da bujirarrun sojojin. Isa Kaita, yace mun ya kamata ni inje gidan Sardauna in ganema idanuna abunda ke faruwa.
Bayan na kintsa nayi sallar subahi, na kuma K**a hanya na nufi gidan Sardauna, naje na ishe gidan anyi kacha-kacha, da shi alamu kuma sunnuna anyi amfani da manyan makamai wurin lalata gidan. Har lokacin da na Isa gidan haryakine a turnuke. Sai wasu tsirarun sojoji ne a tsaye da bindigogi a hannunsu, ko ina tsit. Haka na wucesu na kutsa kaina cikin gidan, ina shiga naci Karo da gawar firimiya a kwance a filin da ake aje motoci na gidan.
Nan danan nace a dauki gawar a kaita gidan, Sarkin Musulmi, dage unguwar Sarki, Sardauna, da shi da uwargidansa Hafsat aka kashesu.
Bayan mun gama kintsashi, rana Kuma ta fara dagowa nine na Sallaci duka gawauwakin. Ina sane Kuma da cewa anyi babban rashi-rashin Kuma dai nan kurkusa abune mawuyace a samu kamarsa.
Akan hanyata ta dawowa gida daga wurin jana'izar Sadauna, na wuce gun-gun mutane sun taru sunata alhinin abunda ya faru. Bayan na samu natsuwa abubuwa sun koma kamar yadda suke ranar komawa aiki na shirya kamar kullun na tafi wurin aikina. Ina cikin ofishina da safe sai ga motar sojoji, sake da sojoji, ta shigo harabar wurin aikina. Wasu daga cikin sojojin s**a sauko a mota s**a tambayi inda ofishina yake. Bayan sun shigo ofishina s**ai mun gaisuwa irinta ta girmamawa, s**a ce anturone su tafi dani maigidansu Nzeogwu, yana son ganina.
Kuma zan shiga motarsu ne tilas su tafi dani amma zan iyasa wani cikin ma'aikatana ya bimu a baya shi sai ya dawo dani. Natashi na bisu banyi musu ba na umarci direbana ya bini da mota bayan mungama ganawa ya dawo dani. Bayan mun isa barikin sojan inda shi Nzeogwu yake. Naga sojoji dayawa suna gadin barikin kuwane soja sabe yake da bindigarsa.
Bayan munyi fakin muka sauko daga mota muka shiga cikin ofishin, cikinmu ba Wanda yaima wani magana tsakanina da wayannan sojojin. Bayan sun kaini inda Nzeogwu, yake, ya Kuma tareni cikin fara'arsa na Kuma zauna akan kujera, sai ya fara magana cikin tattausar murya.
Abunda yake son sani shine ina muka boye makaman da muka siyo? Wannan tambayar tasa tabani matukar mamaki, naga nide a rayuwata banma taba ganin Nzeogwu ba, ban Kuma taba wata alakar ta rayuwa dashi ba. Ni a tunanima shi ne ya kirani yaimun ta'aziyar rashin Sardauna, dana yi kokuma ya nuna dana saninsa akan abunda ya aikata. Dama ban yi tsammanin kalamai na banhakuri daga gareshi ko nadama akan abunda ya aikata tunda na lura yana al'afari da abunda ya aikata.
Abunda Kuma ya kara bani mamaki Wanda s**a sabi makamai s**ayi Juyin mulki wai a lokacinne suke kokarin tattara hujjojinsu ko kuma dalilan hambarar da wannan gwamnatin.
Sai nagama kafin in bashi amsar tambayarsa yakamata in nemi karin bayani daga gareshi. Sai yacemun a irin labaran daya samu an cemai mun siyo makamai masu tarin yawa munshigo dasu cikin kasa, Kuma mun siyo makaman ne daga kasashen gabas ta tsakiya. Kuma niyarmu itace mu kaddamar da jahadi akan wayanda ba musulmaiba, shiyasa yakeso in gayamai inda muka boye makaman.
Lokacin danazo bashi amsar tambayarsa na tabbatarmai cewar ni a wurinsa ma na farajin wannan maganar, na Kuma tabbatar Ina magana ne a matsayina na mashawarcin Sardauna, akan harkokin da s**a shafi addinin Musulunci. Kuma na tabbatarmai da cewa Sardauna, bai taba zuwa wata kasar labawa a matsayinsa na firimiya ba tareda daniba. Kuma bantaba ji yai maganan makamai ba a wata kasar larabawa, ballema har musiyo mu shigodasu Najeriya, da sunan wai zamu yaki wayanda ba musulmaiba.