Labaran Duniya - News

Labaran Duniya - News Wanna page ne da zai rika kawo maku labarai da abubuwan yau da kullum

Wasu ’yan majalisar dokokin ƙasar Amurka ƙarƙashin jagorancin ɗan majalisa Riley Moore sun miƙa wa Fadar White House rah...
25/02/2026

Wasu ’yan majalisar dokokin ƙasar Amurka ƙarƙashin jagorancin ɗan majalisa Riley Moore sun miƙa wa Fadar White House rahoto na musamman kan halin da ake ciki a Najeriya, musamman dangane da zargin tauye ’yancin kiristoci.

Rahoton ya buƙaci gwamnatin Amurka ta sake sanya Najeriya cikin jerin ƙasashen da ake zargi da take hakkin addini, tare da kakaba takunkumi kan duk wanda aka samu da hannu wajen cin zarafin mabiya addinai, ciki har da hana su biza.

’Yan majalisar sun kuma nemi a duba yiwuwar dakatar da shigo da wasu kayayyaki daga Najeriya, ciki har da naman shanu, domin matsa lamba ga masu tayar da hankali su ajiye makamansu.

Haka kuma, tawagar ta ba da shawarar cewa Najeriya ta daina sayen makamai daga Rasha, maimakon haka ta koma sayen makaman Amurka a matsayin wani ɓangare na ƙarfafa alaƙar tsaro tsakanin ƙasashen biyu.

Bugu da ƙari, rahoton ya buƙaci gwamnatin Najeriya ta soke wasu dokoki da s**a haɗa da na shari’a da na ɓatanci, waɗanda a cewarsu ana amfani da su wajen gallaza wa wasu mabiya addini.

BABBAR MAGANA: ANA SHIRIN YIWA IXRA'ILA JEKA KA MUTU Yau Kasar Amurka ta baiwa Ix'ra'ila jiragen F-22 domin kare kanta d...
25/02/2026

BABBAR MAGANA: ANA SHIRIN YIWA IXRA'ILA JEKA KA MUTU

Yau Kasar Amurka ta baiwa Ix'ra'ila jiragen F-22 domin kare kanta daga harin iran , bayan ganin wadda yau Iran ta saya daga wurin China

To wane jirgi ne F-22?

Tabbas jiragen F-22 jirage ne masu hatsari na gaske kuma suna da matukar sauri ,amma ku sani ko kusa bai kai rabin Mi-302 da China ta sayar ma Iran ba .

Hasalima a tarihin duniya Jasar Ir'an ce kasa daya tilo da a tarihi ta taba harbo jirgin F-22 a yakin sati biyu da s**a yi da Iran a kwanakin baya .

Wato ni abin da na gani shine Amurka na son yiwa Ixra'ila jeka ka mutu ne, saboda Amurka na da gaggan mahaukatan kayan yaki

Misali

F-15 super eagle

Versatile F-35 lighting

Super Hornet

Fighting Falcon

Wadannan duka na zamani ne amma ba ta basu ko daya ba sai ta zabi F-22 kuma ta san Ir'an na da makamin harbo ta .

Muje zuwa dai Allah zai nuna mana komai

Zargin cin hanci: Shari'ar Malami ta koma hannun sabon alƙaliBabban alƙalin kotun tarayya, John Tsoho, ya mayar da shari...
24/02/2026

Zargin cin hanci: Shari'ar Malami ta koma hannun sabon alƙali

Babban alƙalin kotun tarayya, John Tsoho, ya mayar da shari’o’i biyu da EFCC ta shigar kan Abubakar Malami ga Mai Shari’a Joyce Abdulmalik, wadda ta sanya ranar 27 ga Fabrairu domin fara sauraro.

Matakin ya biyo bayan janyewar Mai Shari’a Obiora Egwuatu daga shari’ar saboda dalilai na ƙashin kai da kuma muradin adalci.

EFCC na tuhumar Malami da laifuffuka 16 da s**a shafi badakalar kuɗi, inda ta ce ta gano kadarori da darajarsu ta kai Naira biliyan 212 a Kebbi, Kano da Abuja.

An gurfanar da shi tare da ɗansa da matarsa, amma sun musanta zarge-zargen.

Haka kuma, ana ci gaba da wata shari’a daban da ke gaban kotu kan zargin tallafa wa ta’addanci da mallakar makamai ba bisa ka’ida ba.

24/02/2026
24/02/2026

Ka Daina Siyasantar Da Harkokin Tsaron Kasa ~ Martanin Nigerian Unite Ga Atiku Abubakar — Mustapha Basiru

Mustapha Nasiru ya bayyana cewa Kalaman Atiku Abubakar na cewa idan wani abu ya samu tsohon gwamnan jihar Kaduna Nasir El-Rufai gwamnatin tarayya za a ɗorawa laifi ko alhakin haka, ya nuna wani salo na siyasa da muka saba gani a Najeriya, siyasar neman tausayin jama'a domin kauce wa fuskantar shari’a. Irin wannan magana kamar yunƙuri ne na matsa lamba ga hukumomi, maimakon a bar doka ta yi aikinta.

Sai ɗan siyasa ya gama satar dukiyar ƙasa yayin da yake karagar mulki, amma da zarar hukumomi sun fara bincikensa sai ya bijiro da rashin lafiya don kaucewa tuhuma, to wannan wasan kwaikwayon dole yazo karshe a wannan lokacin. Domin wannan kiran na ka a wannan lokacin ba komai illa neman mafaka ta siyasa don biyan bukatar kanku bakomai ba.

A ƙasarmu, ya zama ruwan dare duk lokacin da ake tuhumar ‘yan siyasa, sai su bayyana kansu a matsayin marasa lafiya domin neman beli ko sassauci. Amma da zarar sun samu damar fita, sai mu gan su suna halartar taruka, suna tafiya ko’ina cikin ƙoshin lafiya. Wannan dabi’a ta sa jama’a s**a fara tambayar gaskiyar ikirarin rashin lafiyar da ake yi a irin waɗannan lokuta.

Saboda haka, a yanzu ba daidai bane yayin da Elrufa'i ke fuskantar tuhuma daga hukumomi a bijiro da maganar rashin lafiya don nema masa bail, wannan cin dunduniyar doka ne, haka kuma kashe goben ƙasa ne.

Idan akwai tuhuma a kan El-Rufa’i, abin da ya dace shi ne ya fuskanci shari’a kamar kowane ɗan ƙasa. Babu wanda ya fi ƙarfin doka, kuma babu wanda ya kamata a ba shi kariya ta siyasa domin guje wa bincike ko tuhuma. Adalci ba ya aiki da barazana ko tausayi, yana aiki ne da gaskiya da hujja.

Lokaci ya yi da za a daina amfani da lafiyar mutum a matsayin garkuwa ta tserewa fuskantar tuhuma a gaban kuliya manta sabo. Najeriya za ta samu ci gaba ne kawai idan muka yarda cewa kowa babba ko ƙarami dole ya amsa idan an tuhume shi. Doka ta fi kowa, kuma dole ta yi aiki akan kowa.

A cikin hotunan nan dake kasa za ku ga yadda yan siyasa ke rainawa mutane hankali a duk lokacin da suke fuskantar tuhuma daga hukumomi a kasar nan.

Sa hannun
Mustapha Basiru
Shugaban Nigerian Unite

YADDA MUKAYI DA NZEOGWU BAYAN YA KASHE SARDAUNA INJE MARIGAYI SHEIKH ABUBAKAR GUMI...K**ar karfe hudu na asuba ranar jum...
24/02/2026

YADDA MUKAYI DA NZEOGWU BAYAN YA KASHE SARDAUNA INJE MARIGAYI SHEIKH ABUBAKAR GUMI...

K**ar karfe hudu na asuba ranar juma'a aka bugomun waya bayan na dauka sai naji ministan ilimi be na Arewa Alhaji Isa Kaita. Ya cemun sojoji fa sun yi Juyin mulki, har ankai ma gidan Sardauna hari kamar yadda yace mun duk manyan jami'an gwamnati sun buya. Yace mun ya yi magana da Hassan Katsina, amma Hassan dai a lokacin yace mai babu abun da zai iyayi. Hassan yace mai a wannan lokacinma yana ganawane da bujirarrun sojojin. Isa Kaita, yace mun ya kamata ni inje gidan Sardauna in ganema idanuna abunda ke faruwa.

Bayan na kintsa nayi sallar subahi, na kuma K**a hanya na nufi gidan Sardauna, naje na ishe gidan anyi kacha-kacha, da shi alamu kuma sunnuna anyi amfani da manyan makamai wurin lalata gidan. Har lokacin da na Isa gidan haryakine a turnuke. Sai wasu tsirarun sojoji ne a tsaye da bindigogi a hannunsu, ko ina tsit. Haka na wucesu na kutsa kaina cikin gidan, ina shiga naci Karo da gawar firimiya a kwance a filin da ake aje motoci na gidan.

Nan danan nace a dauki gawar a kaita gidan, Sarkin Musulmi, dage unguwar Sarki, Sardauna, da shi da uwargidansa Hafsat aka kashesu.

Bayan mun gama kintsashi, rana Kuma ta fara dagowa nine na Sallaci duka gawauwakin. Ina sane Kuma da cewa anyi babban rashi-rashin Kuma dai nan kurkusa abune mawuyace a samu kamarsa.

Akan hanyata ta dawowa gida daga wurin jana'izar Sadauna, na wuce gun-gun mutane sun taru sunata alhinin abunda ya faru. Bayan na samu natsuwa abubuwa sun koma kamar yadda suke ranar komawa aiki na shirya kamar kullun na tafi wurin aikina. Ina cikin ofishina da safe sai ga motar sojoji, sake da sojoji, ta shigo harabar wurin aikina. Wasu daga cikin sojojin s**a sauko a mota s**a tambayi inda ofishina yake. Bayan sun shigo ofishina s**ai mun gaisuwa irinta ta girmamawa, s**a ce anturone su tafi dani maigidansu Nzeogwu, yana son ganina.

Kuma zan shiga motarsu ne tilas su tafi dani amma zan iyasa wani cikin ma'aikatana ya bimu a baya shi sai ya dawo dani. Natashi na bisu banyi musu ba na umarci direbana ya bini da mota bayan mungama ganawa ya dawo dani. Bayan mun isa barikin sojan inda shi Nzeogwu yake. Naga sojoji dayawa suna gadin barikin kuwane soja sabe yake da bindigarsa.

Bayan munyi fakin muka sauko daga mota muka shiga cikin ofishin, cikinmu ba Wanda yaima wani magana tsakanina da wayannan sojojin. Bayan sun kaini inda Nzeogwu, yake, ya Kuma tareni cikin fara'arsa na Kuma zauna akan kujera, sai ya fara magana cikin tattausar murya.

Abunda yake son sani shine ina muka boye makaman da muka siyo? Wannan tambayar tasa tabani matukar mamaki, naga nide a rayuwata banma taba ganin Nzeogwu ba, ban Kuma taba wata alakar ta rayuwa dashi ba. Ni a tunanima shi ne ya kirani yaimun ta'aziyar rashin Sardauna, dana yi kokuma ya nuna dana saninsa akan abunda ya aikata. Dama ban yi tsammanin kalamai na banhakuri daga gareshi ko nadama akan abunda ya aikata tunda na lura yana al'afari da abunda ya aikata.

Abunda Kuma ya kara bani mamaki Wanda s**a sabi makamai s**ayi Juyin mulki wai a lokacinne suke kokarin tattara hujjojinsu ko kuma dalilan hambarar da wannan gwamnatin.

Sai nagama kafin in bashi amsar tambayarsa yakamata in nemi karin bayani daga gareshi. Sai yacemun a irin labaran daya samu an cemai mun siyo makamai masu tarin yawa munshigo dasu cikin kasa, Kuma mun siyo makaman ne daga kasashen gabas ta tsakiya. Kuma niyarmu itace mu kaddamar da jahadi akan wayanda ba musulmaiba, shiyasa yakeso in gayamai inda muka boye makaman.

Lokacin danazo bashi amsar tambayarsa na tabbatarmai cewar ni a wurinsa ma na farajin wannan maganar, na Kuma tabbatar Ina magana ne a matsayina na mashawarcin Sardauna, akan harkokin da s**a shafi addinin Musulunci. Kuma na tabbatarmai da cewa Sardauna, bai taba zuwa wata kasar labawa a matsayinsa na firimiya ba tareda daniba. Kuma bantaba ji yai maganan makamai ba a wata kasar larabawa, ballema har musiyo mu shigodasu Najeriya, da sunan wai zamu yaki wayanda ba musulmaiba.

24/02/2026

An sanya sabon lokacin ci gaba da shari'ar Malami da EFCC bayan karar ta je wurin sabon alkali - Karin bayani a sashen sharhi.

Hoto: (X), Abubakar Malami, SAN (Facebook)

01/02/2026

Troops neutralised a top Boko Haram leader and other foot soldiers during a night operation. Full details about the ambush are in the comments.
Photo credit: /X

01/02/2026

YANZU-YANZU: 'Ýàn Bìnďìga Suñ Bankawà Çocì Da Ofishiñ 'Yàn Sandà Wuta A Jihar Neja

Lamarin ya auku ne a garin Agwara, inda kuma s**a yi awon gaba da wasu mazauna yankunañ.

01/02/2026

China ta Kafa Tarihi Bayan kammala Wani babban aiki na hanyoyin sufuri a ƙarƙashin Ruwa

Mataimaki na musamman ga gwamnan Umaru Radda kan kafafen watsa labaru MS Ingawa a wata sanarwa da ya fitar, ya ce tuni a...
30/01/2026

Mataimaki na musamman ga gwamnan Umaru Radda kan kafafen watsa labaru MS Ingawa a wata sanarwa da ya fitar, ya ce tuni aka saka hannu a kan yarjejeniyar gina gidajen da wani kamfani ,mai suna COSMOS Residential City Nigeria Limited.

30/01/2026

Majalisar dokokin jihar Kano ta yi tsokaci kan batun tsige Aminu Abdulsalam Gwarzo daga kan mukaminsa - Karin bayani a sashen sharhi.

Hoto: Abba Kabir Yusuf (Facebook), Aminu Abdulsalam Gwarzo (Facebook)

Address

Bwari

Telephone

+2348024002102

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Labaran Duniya - News posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Labaran Duniya - News:

Share

Category