Labaran Duniya - News

Labaran Duniya - News Wanna page ne da zai rika kawo maku labarai da abubuwan yau da kullum

Wani matashi mai suna Abubakar Dan Ædo, dan asalin jihar Kano daga karamar hukumar Garin Malam, ya mika saƙonsa ga shuga...
09/11/2025

Wani matashi mai suna Abubakar Dan Ædo, dan asalin jihar Kano daga karamar hukumar Garin Malam, ya mika saƙonsa ga shugaban Amurka Donald Trump yana roƙonsa da ya janye kalamansa kan zargin kisan Kiristoci a Najeriya.

Matashin ya bayyana cewa kalaman Trump na iya haifar da rikice-rikice, yana mai cewa “ko da bayan shekaru dubu uku, idan irin wannan zargi ya ci gaba, ransa ba zai yi daɗi ba.”

Shin wannan kira daga matashin zai ja hankalin shugaban Amurka ya sake duba furucinsa?

Gwamnatin Najeriya ta sanar da cewa, daga 1 ga Janairu, 2026, babu wanda zai iya buɗe ko gudanar da asusun banki ba tare...
09/11/2025

Gwamnatin Najeriya ta sanar da cewa, daga 1 ga Janairu, 2026, babu wanda zai iya buɗe ko gudanar da asusun banki ba tare da Lambar Shaida ta Haraji (Tax Identification Number – TIN/Tax ID) ba.

Hukumar Haraji ta Kasa ta bayyana cewa wannan sabon tanadi zai shafi bankuna, kamfanonin inshora, dillalan hannayen jari, da sauran cibiyoyin kuɗi a ƙasar.

A cewar hukumar, duk wanda bai nemi Tax ID da kansa ba, hukumar na da ikon yi masa rajista ta hanyar da ta dace domin ya samu lambar.

Babban sakamakon wannan doka:

Ba za a buɗe sabon asusun banki ba ga waɗanda ba su da Tax ID.

Masu asusun banki na yanzu za su buƙaci haɗa asusun nasu da Tax ID kafin ci gaba da yin mu’amala.

Bankuna da sauran cibiyoyin kuɗi za su sabunta tsarin ayyukansu domin bin wannan doka.

Gwamnati ta ce matakin zai taimaka wajen inganta tsarin biyan haraji da kuma tsabtace mu’amalar kuɗi a ƙasar.

Hukumar ta yi kira ga al’umma da su fara shirin samun Tax ID domin gudun wani tsaiko a mu’amalarsu ta banki nan gaba.

Tushen labari: Hukumar Haraji ta Kasa

09/11/2025

Gwamnatin Birtaniya ta fitar da sabon gargadi ga ’yan ƙasarta, tana shawartar su da su guji tafiya zuwa wasu jihohin Najeriya saboda ƙaruwar rashin tsaro, satar mutane, da ayyukan ta’addanci.

One News Hausa, ta ruwaito inda Ofishin harkokin wajen Birtaniya ya bayyana cewa jihohin da abin ya fi shafa sun haɗa da Borno, Yobe, Adamawa, Gombe, Katsina da Zamfara, inda yake cewa akwai barazanar B0k0 Haram da 1SWAP musamman a wajen taruka da wuraren ibada.

Haka kuma, an gargadi ’yan ƙasar da su guji tafiya marar muhimmanci zuwa jihohin Kaduna, Kano, Niger, Plateau, da Taraba, da kuma wasu unguwannin Abuja, saboda yawaitar satar mutane da tashin hankali.

Gwamnatin ta kuma shawarci ’yan ƙasar da ke Najeriya da su kula da tsaronsu, su guji taron jama’a, tare da sabunta shirin tsaro, tana mai cewa halin rashin tsaro a Najeriya yana ƙara ta’azzara sakamakon ta’addanci, fashi da rikicin kabilu.


09/11/2025

Majalisar dattawa ta bayyana dalilin dakatar da tabbatar da nadin da Mai girma Bola Tinubu ya yi wa Abdullahi Ramat don shugabantar hukumar NERC - Karin bayani a sashen sharhi.

Hoto: Godswill Obot Akpabio (Facebook), Engr. Abdullahi Garba Ramat (Facebook)

09/11/2025

A yayin da kwanakin rufewar gwamnatin Amurka ya kai rana ta 39, dubban jiragen sama sun fuskanci dakatarwa ko jinkiri. Wannan na faruwa ne sakamakon rashin biyan ma’aikatan da ake buƙata, ciki har da masu kula da zirga-zirgar jiragen sama, inda kashi ashirin (20) zuwa arba'in (40%) ke ƙin zuwa aiki saboda rashin albashi.

Hukumomin FAA sun umarci a rage kashi huɗu (4%) na zirga-zirgar jiragen sama a manyan filayen jirgin sama arba'in (40 ) saboda dalilan tsaro, wanda zai ƙaru zuwa kashi goma (10%) kafin 14 ga Nuwamba. A ranar Asabar kaɗai, an samu sama da jiragen sama dubu ɗaya da ɗari biyar da talatin (1,530) da aka soke da kuma jinkirin fiye da dubu shida (6,000), musamman a filayen jirgin Atlanta.

Hakan yana shafar sufurin kaya, harkokin kasuwanci, da yawon shaƙatawa, in ji Bryan Bedford na FAA.

Shin me za ku ce game da wannan?

📷/: Shugaban Amurka Donald J. Trump/: Credit [Getty Images]

Tsohon shugaban Amurka, Donald Trump, ya jefa hulɗar Najeriya da Amurka cikin sabon yanayi na cece-kuce, bayan da ya yi ...
07/11/2025

Tsohon shugaban Amurka, Donald Trump, ya jefa hulɗar Najeriya da Amurka cikin sabon yanayi na cece-kuce, bayan da ya yi barazanar cewa zai iya daukar matakin soja kan Najeriya kan yadda ake tafiyar da batun tsaron addini a kasar.

A cewar rahoton Punch, Trump ya wallafa a dandalinsa na Truth Social cewa ya umurci Ma’aikatar Tsaron Amurka ta fara nazarin yiwuwar daukar mataki, yana mai zargin cewa ana barin ‘yan kirista cikin mawuyacin hali ba tare da kariya ba.

Rasha Ta Fito Da Sanarwa

Gwamnatin Rasha ta bayyana cewa tana “kusa da sa ido” kan dukkan matakan da Amurka ke yi, tare da gargadin cewa duk wani mataki na soja dole ne ya bi tsarin kasa da kasa.

Moscow ta kuma yi kira ga Amurka da ta nisanci duk wani abu da zai iya keta ikon Najeriya da ‘yancinta na cin gashin kanta.

Martanin Najeriya

Ita kuwa Najeriyar, ta yi nuni da cewa tana maraba da taimako daga kowace kasa muddin an mutunta ikon ta na gudanar da harkokin cikin gida. Jami’an gwamnatin Najeriya sun ce batun tsaro ya shafi kowane yanki da addini, ba wai takamaimi ga wani rukuni ba.

Me Lamarin Ke Nufi?

– Barazanar Trump na iya kara tsananta tattaunawar diflomasiyya tsakanin Amurka da Najeriya.
– Tsoma bakin Rasha na nuna irin tasirin da batun ya samu a idon manyan kasashen duniya.
– Masana harkokin tsaro na ganin cewa wannan lamari zai iya kara daukar hankali, musamman ganin yadda ake kara takaddama kan tsaron addini a yankin Sahel.

Tushen Labari: Punch Newspaper (punchng.com)

07/11/2025

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya bayyana cewa, gwamnatinsa ta samu babban ci gaba wajen yaki da ta’addanci da sauran laifuffuka a cikin shekaru biyu da s**a gabata.

A cikin wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na sada zumunta ranar Juma’a, shugaban ya jaddada cewa gwamnati ba za ta yi sulhu da ’yan ta’adda ba, kuma za ta ci gaba da tabbatar da tsaro da zaman lafiya a faɗin ƙasar.

Tinubu ya bayyana cewa, gwamnatin sa na amfani da sabbin dabaru da tsare-tsare don dawo da zaman lafiya, tare da tabbatar da haɗin kan ’yan ƙasa. “Najeriya ƙasa ɗaya ce, muna tashi tare, muna ci gaba tare,” in ji shi.

Ya ƙara da cewa, gwamnati za ta ci gaba da yin aiki tukuru wajen kawar da masu aikata laifuka, tare da neman haɗin gwiwar ƙasashen abokai don ƙara ƙarfafa yaƙin da ake yi da ta’addanci a Najeriya.

Gwamnatin Rasha ta bayyana cewa tana bibiyar al’amuran da s**a shafi barazanar Donald Trump na yiwuwar kai farmaki a Naj...
07/11/2025

Gwamnatin Rasha ta bayyana cewa tana bibiyar al’amuran da s**a shafi barazanar Donald Trump na yiwuwar kai farmaki a Najeriya.

Mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen Rasha, Maria Zakharova, ta bayyana hakan a Moscow ranar Juma’a yayin ganawa da ’yan jarida, inda ta shawarci Amurka da ta mutunta dokokin ƙasa da ƙasa tare da yin taka-tsantsan kan batutuwan tsaron duniya.

Zakharova ta ce, “Muna bibiyar lamarin sosai, kuma muna kira ga duk ɓangarorin da abin ya shafa da su kiyaye dokokin ƙasa da ƙasa.”

Trump dai ya ce ya umurci Pentagon da ta tsara matakan soja da za a iya ɗauka a Najeriya don kare Kiristoci daga hare-haren ’yan ta’adda.

Zakharova ta kuma nuna damuwa game da abin da ta kira “sake keta yarjejeniyar tsagaita wuta” da ’yan ƙasar mamaya ke yi a kan iyakar Lebanon, tana mai jaddada cewa Rasha za ta ci gaba da aiki tare da ƙasashen yankin don tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a Gabas ta Tsakiya.

07/11/2025

Sheikh Ahmad Gumi ya ce ƴan bindiga ba sa kai hari babu dalili, yana mai kiran gwamnati da ta nemi sulhu da su domin samun zaman lafiya a Najeriya.

07/11/2025
BABBAR MAGANA: Shugaban Amurka, Donald Trump, ya bayyana wa manema labarai cewa a yau da yamma makaman linzami masu ɗauk...
07/11/2025

BABBAR MAGANA: Shugaban Amurka, Donald Trump, ya bayyana wa manema labarai cewa a yau da yamma makaman linzami masu ɗauke da guba da ya aika zuwa Najeriya za su isa ƙasar.

Wannan batu ya tayar da hankula matuƙa, ciki har da ƴan ƙasar Amurka da dama, inda wasu daga cikinsu s**a fito suna gudanar da zanga-zanga domin nuna rashin amincewarsu da wannan mataki.

Rahoton Jaridar Rariya Online

Kasuwar hannayen jari ta Najeriya (Nigerian Exchange – NGX) ta fuskanci mummunar asara cikin mako ɗaya kacal, inda ta ra...
07/11/2025

Kasuwar hannayen jari ta Najeriya (Nigerian Exchange – NGX) ta fuskanci mummunar asara cikin mako ɗaya kacal, inda ta rasa kimanin Naira tiriliyan 2.8, bayan da masu saka jari s**a fara sayar da hannayen jarinsu sakamakon rahotannin da ke cewa Amurka na iya kai farmaki ga Najeriya.

A ranar 7 ga Nuwamba, All-Share Index (ASI) ta sauka zuwa maki 149,524.8, bayan raguwar maki 501.7 daga zaman kasuwa na baya. Wannan ne karo na biyar a jere da kasuwar ke fuskantar faɗuwa, wanda ya nuna raguwa da kashi 2.11% a cikin makon.

Rahoton kasuwar ya nuna cewa a ranar Jumma’a, kasuwar ta sake raguwa da kashi 0.33%, inda aka yi cinikin hannayen jari miliyan 527 cikin mu’amaloli 24,637, idan aka kwatanta da miliyan 619 da aka sayar a ranar Alhamis.

Jimillar kuɗin kasuwa (market capitalization) ta faɗi daga Naira tiriliyan 95.3 zuwa Naira tiriliyan 94.9, alamar cewa yanayin faɗuwar kasuwa (bearish trend) na ci gaba.

KBC Hausa

Address

Bwari

Telephone

+2348024002102

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Labaran Duniya - News posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Labaran Duniya - News:

Share

Category