09/11/2025
Wani matashi mai suna Abubakar Dan Ædo, dan asalin jihar Kano daga karamar hukumar Garin Malam, ya mika saƙonsa ga shugaban Amurka Donald Trump yana roƙonsa da ya janye kalamansa kan zargin kisan Kiristoci a Najeriya.
Matashin ya bayyana cewa kalaman Trump na iya haifar da rikice-rikice, yana mai cewa “ko da bayan shekaru dubu uku, idan irin wannan zargi ya ci gaba, ransa ba zai yi daɗi ba.”
Shin wannan kira daga matashin zai ja hankalin shugaban Amurka ya sake duba furucinsa?