Abu Safwan Tsafe

Abu Safwan Tsafe Allah kasa mu rabu da mahaifanmu lafiya

26/02/2025

Majalisar Dattawan ta umarci Ahmad Isah, wanda aka fi sani da "Ordinary President" na Brekete Family, da ya gurfana a gabanta a ranar 27 ga Fabrairu, 2025.

Dubban yan Najeriya na cigaba da sukan gayyatar, ciki har da Sanata Shehu sani.

Shehu Sani ya ce, “Kiran Ahmed Isah, Shugaban Brekete Radio, zuwa Majalisar Dattawa ba shi da wata amfani kuma abin ƙasƙanci ne.”

An yi wannan kiran ne a daidai lokacin da ake rikici game da hatsaniya da ta ɓarke tsakanin Sanata Akpoti-Uduaghan da Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio, kan matsayinta a zauren majalisa.

Sanatar Kogi ta yi zargin cewa shugabancin majalisar na shirin dakatar da ita bayan da ta nuna rashin jin daɗinta kan yadda aka sauya mata wurin zama ba tare da sanar da ita a gaba ba.

Rigimar ta ƙara tsananta ne lokacin da ta dage sai ta ci gaba da zama a wurin da aka cire ta, lamarin da ya sa Babban Mai Tsawatarwa na Majalisar, Tahir Monguno, ya ambato Sashe na 6(1) na Dokokin Majalisar Dattawa, wanda ke bai wa Shugaban Majalisar ikon tsara wuraren zama.

A lokacin da takaddamar ke ƙaruwa, an ruwaito cewa Akpabio ya kashe maƙirfon ta tare da bayar da umarnin a fitar da ita daga zauren majalisa.

Bayan afkuwar lamarin, Akpoti-Uduaghan ta bayyana ƙorafinta yayin wata hira da ta yi a gidan rediyon Brekete Family, an kira Akpabio don jin ta bakinsa amma lamarin ya gagara.

08/12/2024

*TAMBIHI NE*

Ka Daina Tak**a Da Çewa Kai Dan Wane ne Ko Jikan Wane ne, Domin Babu Gudumuwarka A Cikin Kasancewarka Haka, Kayi Kokari Kaima Ka Zama Wane.

05/12/2024

*TAMBIHI NE*

"Nasara da dacewar da kake nema a duk tsawon rayuwar ka, kullum tana kiran ka har sau biyar a kowace rana, (itace sallah, idan ka kiyaye ta, sai ta zamto maka nasara a duniya da kuma lahira)"

06/11/2024

*TAMBIHI NE*

"Duk lokacin da ka ga baka ƙyamatan zunubi, to da alama zuciyarka ta mutu ko bata da lafiya."

SIFFOFIN MACE TA GARI GUDA SABA'IN (70) 🧕1 mai biyayya ga mijinta.2 mai jin tsoron Allah3 mai biyayyah wa iyayyen ta4 ma...
03/11/2024

SIFFOFIN MACE TA GARI GUDA SABA'IN (70) 🧕

1 mai biyayya ga mijinta.
2 mai jin tsoron Allah
3 mai biyayyah wa iyayyen ta
4 mai kula da addinin ta
5 mai nutsuwa
6 mai kamun kai da rike darajar ta 'ya mace
7 mai gaskiya da rikon amana
8 mai taimako
9 mai tausayi
10 mai tarbiyyatar da yaranta
11 mai aiki da iliminta
12 bata yaudara
13 bata karya
14 mai kiyaye kanta
15 mai gudun aikata sabon Allah
16 mai gudun zina
17 mai yarda da kaddara
18 mai son zaman lafiya
19 mai hakuri
20 mai taimakon iyayenta
21 mai shiga tak**ala
22 mai iya lafuza mai kyau
23 mai kunya
24 bata da masifa
25 bata da hayaniya
26 duk maganar dazata fada takan fadi mai amfani
27 mai kula da hakkin mijinta
28 bata daga muryarta wa mijinta
29 bata maganar da bashi da amfani.
30 mai ilimi
31 mai godiya ga mijinta duk abinda yabata.
32 mai yiwa mijinta addu'a
33 mai yiwa mutane fatan alkhairi
34 mai zama da mutane da zuciya daya,
35 mai nufar mutum da kyakkyawar zuciya na alkhairi
36 batayin hassada
37 bata yin kwadayi
38 batayin dogon buri
39 mai kamun kai a duk inda tashiga
40 mai son taimako
41 mai kula da mutuncin kanta
42 batayin wulakanci
43 bata kula wasu samarika masu s*x chart
44 mai rufawa mijinta asiri
45 mace tagari batayin zagin 'ya'yanta idan sun bata mata rai takan masu nasiha
46 mai daukar rayuwa a sauwake
47 mai yawan tunawa da akwai mutuwa
48 bata gulma ko munafurci
49 mai yawaita istigifari
50 mai yawaita salati ga manzo
51 mai yawaita karatun Al'qur'ani mai girma
52 bata canja halittan (bleaching)
53 mai godiya ga Allah
54 bata daura wa mijinta nauyin abinda bai dashi tace sai ya mata.
55 mai tausayin mijinta
56 mai kula da hakkin makwaftanta
57 mace tagari bata bin bokaye ko 'yan tsubbu
58 mai son farantawa mijin ta rai
59 mai kaunar danginta
60 mai kaunar dangin mijinta
61 mai kaunar iyayen mijinta
62 mai kaunar kishiyarta da zuciya daya
63 mai son sada zumunta
64 mace tagari akwai tsafta
65 mace tagari bata son ganin fushin mijinta
66 mace tagari mai kiyaye dokokin Allah
67 mace tagari bata mummunan kishin haukan dawasu matan keyi
68 mai son ya'yan mijinta
69 mai hankali da nutsuwa
70 mai tarbiyya da cikar k**ala

✍️. Nusaiba Taseeu Abdulraheem

ZIKIRIN SAFIYA DA MARAICEℹ️ Lokacin da ake yin zikirin safiya shine daga bayan sallar asuba zuwa kafin rana ta ɓullo.Lok...
17/09/2024

ZIKIRIN SAFIYA DA MARAICE

ℹ️ Lokacin da ake yin zikirin safiya shine daga bayan sallar asuba zuwa kafin rana ta ɓullo.

Lokacin da ake yin zikirin maraice kuma shine daga bayan sallar la'asar zuwa kafin rana ta faɗi.

Babu laifi musulmi ya yi su a bayan waɗancan lokutan da aka faɗa (ma'ana bayan lokacin da ake yin zikirin ya wuce), idan ya manta ko kuma wani uzuri ya bijiro mai sai bai samu damar yin su ba.

📘"فقه الأدعية والأذكار" للشيخ عبد الرزاق البدر.

"Fiqh Al'adeiat Wal'adhkar" Na Shaikh Abdulrazaƙ Albadri.

(1)

Karanta Ayatul-kursiyu. (sau ɗaya):

﴿اللَّهُ لَا إِلَٰهَ إِلَّا هُوَ الْحَيُّ الْقَيُّومُ ۚ لَا تَأْخُذُهُ سِنَةٌ وَلَا نَوْمٌ ۚ لَهُ مَا فِي السَّمَاوَاتِ وَمَا فِي الْأَرْضِ ۗ مَنْ ذَا الَّذِي يَشْفَعُ عِنْدَهُ إِلَّا بِإِذْنِهِ ۚ يَعْلَمُ مَا بَيْنَ أَيْدِيهِمْ وَمَا خَلْفَهُمْ ۖ وَلَا يُحِيطُونَ بِشَيْءٍ مِنْ عِلْمِهِ إِلَّا بِمَا شَاءَ ۚ وَسِعَ كُرْسِيُّهُ السَّمَاوَاتِ وَالْأَرْضَ ۖ وَلَا يَئُودُهُ حِفْظُهُمَا ۚ وَهُوَ الْعَلِيُّ الْعَظِيمُ﴾.

Allah, babu wani abin bautawa da gaskiya sai Shi, Rayayye, Mai tsayuwa da komai. Gyangyaɗi ba ya k**a Shi, wala barci. Abin da ya ke cikin sammai da abin da yake cikin kasa nasa ne. Babu mai yin ceto a wurinsa sai da izininsa. Yana sane da abin da yake gabansu (wato al’amarin duniya) da abin da yake bayansu (na al’amarin lahira). Ba sa sanin wani abu daga iliminsa, sai abin da Ya so. Kursiyyunsa (wato gadonsa) ya yalwaci sammai da ƙasa, kuma kiyaye su (sammai da ƙassai) ba ya yi masa nauyi. Shi ne kuma Maɗaukaki, Mai girma.

Da kuma karanta waɗannan surori kowace (sau uku):

﴿قُلۡ هُوَ ٱللَّهُ أَحَدٌ...﴾،
﴿قُلۡ أَعُوذُ بِرَبِّ ٱلۡفَلَقِ...﴾،
﴿قُلۡ أَعُوذُ بِرَبِّ ٱلنَّاسِ...﴾.

(2)

(أَصْبَحْنَا وَأَصْبَحَ الْمُلْكُ لِلّٰهِ)¹، وَالْحَمْدُ لِلّٰهِ، لَا إِلَهَ إلَّا اللّٰهُ، وَحْدَهُ لَا شَرِيكَ لَهُ، لَهُ الْمُلْكُ، وَلَهُ الْحَمْدُ، وَهُوَ عَلَى كُلِّ شَيْءٍ قَدِيرٌ، (رَبِّ أَسْأَلُكَ خَيْرَ مَا فِي هَذَا الْيَوْمِ، وَخَيرَ مَا بَعْدَهُ، وَأَعُوذُ بِكَ مِنْ شَرِّ مَا فِي هَذَا الْيَوْمِ، وَشَرِّ مَا بَعْدَهُ)²، رَبِّ أَعُوذُ بِكَ مِنَ الْكَسَلِ، وَسُوءِ الْكِبَرِ، رَبِّ أَعُوذُ بِكَ مِنْ عَذَابٍ فِي النَّارِ وَعَذَابٍ فِي الْقَبْرِ.

Mun wayi gari, kuma mulki ma ya wayi gari yana mai tabbata ga Allah. Dukkan yabo ya tabbata ga Allah. Babu abin bautawa da gaskiya sai Allah, mulki ya tabbata gare Shi, kuma yabo ya tabbata gare Shi, kuma Shi Mai iko ne bisa komai. Ya Ubangijina! Ina roƙonka alherin da ke cikin wannan rana, da alherin da ke bayanta. Kuma ina neman tsarinka daga sharrin da ke cikin wannan rana, da sharrin da ke bayanta. Ya Ubangijina) Ina neman tsari da Kai daga lalaci, da mummunan tsufa. Ya Ubangijina! Ina neman tsari da Kai daga azaba a cikin wuta, da kuma azaba a cikin ƙabari.

Idan da maraice ne sai ya ce:

¹(أَمْسَيْنَا وَأَمْسَى الْمُلْكُ لِلّٰهِ).

²(رَبِّ أَسْأَلُكَ خَيْرَ مَا فِي هَذِهِ الْلَيْلَةِ، وَخَيْرَ ما بَعْدَهَا، وَأَعُوذُ بِكَ مِنْ شَرِّ مَا فِي هَذِهِ الْلَيْلَةِ، وَشَرِّ مَا بَعْدَهَا).

¹ Mun shiga maraice, kuma mulki ma ya shiga maraice yana mai tabbata ga Allah.

² Ya Ubangijina! Ina roƙonka alherin da ke cikin wannan dare da alherin da ke bayansa. Kuma ina neman tsarinka daga sharrin da ke cikin wannan dare da sharrin da ke bayansa.

(3)

اللَّهُمَّ أَنْتَ رَبِّي لَا إِلَهَ إلَّا أَنْتَ، خَلَقْتَنِي وَأَنَا عَبْدُكَ، وَأَنَا عَلَى عَهْدِكَ وَوَعْدِكَ مَا اسْتَطَعْتُ، أَعُوذُ بِكَ مِنْ شَرِّ مَا صَنَعْتُ، أَبُوءُ لَكَ بِنِعْمَتِكَ عَلَيَّ، وَأَبُوءُ بِذَنْبِي، فَاغْفِرْ لِي، فَإِنَّهُ لَا يَغْفِرُ الذُّنُوبَ إِلَّا أَنْتَ.

Ya Allah! Kai ne Ubangijina; babu abin bautawa da gaskiya sai Kai. Ka halicce ni, kuma ni bawanka ne; kuma ina kan alƙawarin da na yi maka (na kaɗaitaka da bauta) da kuma alƙawarin da Ka yi mini (na shigar da wanda bai yi shirka da Kai ba gidan aljanna) gwargwadon ikona. Ina neman tsarinka daga sharrin abin da na aikata. Ina tabbatar da ni'imarka gare ni, kuma ina tabbatar da zunubi na; Ka gafarta mini, domin ba wanda yake gafarta zunubai sai Kai.

(4)

(اللَّهُمَّ بِكَ أَصْبَحْنَا، وَبِكَ أَمْسَيْنَا، وَبِكَ نَحْيَا، وَبِكَ نَمُوتُ، وَإِلَيْكَ النُّشُورُ)¹.

17/05/2024

This version of Facebook uses less data and works in all network conditions.

*«SUNNONIN RANAR JUMA'A»*--© Yin Addu'a.© Yin Salati.© Karanta Suratul-Kahfi.© Yin Wanka.© Yin Aswaki.© Sanya Turare.-Wa...
17/05/2024

*«SUNNONIN RANAR JUMA'A»*
-
-
© Yin Addu'a.
© Yin Salati.
© Karanta Suratul-Kahfi.
© Yin Wanka.
© Yin Aswaki.
© Sanya Turare.
-
Waɗannan Wasu Ne Daga Cikin Sunnonin Ranar Juma'a, Waɗanda Aƙalla Anso Kayisu Koda Ba Dukkaninsu Bane, Amma Idan Bakayi Ko Ɗaya Ba, Bakayi Laifi Ba, Saidai Kabar Ladan Aikata Sunnah Ta Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama.
-
Amma Saidai Asara Ce Babba Ace Ranar Juma'a Ko Watanta Mutum Yaƙi Yiwa Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama Salati, Domin Shi Salati Idan Kayiwa Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama Guda Ɗaya, To Kaima Allah Buwayi Zaiyi Maka Guda Goma, Musamman Ma Daren Juma'a Da Ranarta, Kaga Kuwa Asara Ce Babba Ace Rana Ta Fito Har Ta Koma Bakayi Masa Salati Ba.
-

Address

Tsafe Local Government
Chafe

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Abu Safwan Tsafe posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share