Hadi AdamuTsafe

Hadi AdamuTsafe Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Hadi AdamuTsafe, Digital creator, Mahauta Area, Chafe.

I Hadi Adamu Tsafe by name I started my primary by the year 2002 at nizzamiyya model primary school Tsafe 2007 and I joined Government Day Secondary school Tsafe Jambulo from 2007 -2013 , After 3 years I joined Federal university Gusau

Inna lil Laahi wa inna ilaiHi Raaji'un!Muna mika taaziyyar rasuwar Mai Martaba Sarkin Katsinan Gusau, the Emir of Gusau,...
25/07/2025

Inna lil Laahi wa inna ilaiHi Raaji'un!

Muna mika taaziyyar rasuwar Mai Martaba Sarkin Katsinan Gusau, the Emir of Gusau, His Highness Dr Ibrahim Bello wanda Allah Ya dauki rayuwarsa a yau.
Za'a masa Sallar Janaza da karfe 2:30pm a Babban Masallacin Jumu'ah na Kanwurin Gusau in Allah Ya yarda.

Muna ta'aziyya zuwa ga iyalansa da yan'uwansa da talakawansa, da Gwamnatin Jihar Zamfara, tare da adduar Allah Ya sa Aljannah ce makomarsa tare da iyayenmu da malamanmu da zurriyyarmu da yan'uwanmu.

MASU DUBA AYYUKAN NUKILIYA NA MAJALISAR DINKIN DUNIYA SUN FICE DAGA KASAR IRAN....Masu duba mak**an nukiliya na hukumar ...
06/07/2025

MASU DUBA AYYUKAN NUKILIYA NA MAJALISAR DINKIN DUNIYA SUN FICE DAGA KASAR IRAN....

Masu duba mak**an nukiliya na hukumar IAEA ta Majalisar Dinkin Duniya sun bar Iran ranar Juma'a bayan kasar ta dakatar da hadin kai da hukumar, sak**akon rikicin kwanaki 12 da ya faru tsakanin Iran da Isra’ila, wanda ya haifar da harin jiragen sama na Isra’ila da Amurka a wuraren mak**an nukiliyar Iran. Wannan ya janyo tashin hankali tsakanin Tehran da hukumar IAEA...

Hukumar ta bayyana cewa tawagar ta fice daga Iran lafiya, suna komawa hedkwatar hukumar a Vienna, bayan sun kasance a Tehran a lokacin rikicin soja. Daraktan IAEA, Rafael Grossi, ya jaddada muhimmancin ci gaba da tattaunawa da Iran domin sake farfado da ayyukan sa ido da tabbatarwa cikin gaggawa...

Iran ta dakatar da hadin kai da IAEA a hukumance ranar Laraba, bayan majalisar kasar ta amince da dokar da ke tabbatar da kare hakkin kasar a karkashin yarjejeniyar hana yaduwar mak**an nukiliya, musamman ma game da bunkasa sinadarin uranium....

Amurka ta soki wannan mataki na Iran, tana mai cewa ba abin karɓa bane, tare da kira ga Tehran da ta dawo kan teburin tattaunawa da aka katse sak**akon harin soja na Isra’ila a watan Yuni...

A gefe guda, Isra’ila ta yi kira ga kasashen duniya da su dauki matakan da s**a dace don tunkarar Iran, har da dawo da takunkumi kan kasar, yayin da ta yaba da nasarorin da sojojinta s**a samu a yakin kwanaki 12 da s**a gabata, duk da dai a zahiri ita Isra’ila ce tafi ɗanɗana kuɗarta...

A takaice, wannan lamari ya kara tsananta rikicin siyasa da na tsaro a yankin, tare da jefa al’amuran nukiliyar Iran cikin yanayi mai cike da rashin tabbas...

To Madallah....

06/07/2025

Namiji ba ya tausayin namiji dan'uwan shi.
Saboda haka KADA ki zama wa mijin ki namiji, kada ya kasa SON ki da TAUSAYIN ki.

AL'AJABI: An Gano Masallacin Da Ya Shekara 37 A Cikin Ruwa Bai Rushe BaWani masallaci ya bayyana, shekara 37 bayan nitse...
06/07/2025

AL'AJABI: An Gano Masallacin Da Ya Shekara 37 A Cikin Ruwa Bai Rushe Ba

Wani masallaci ya bayyana, shekara 37 bayan nitsewarsa cikin wata madatsar ruwa da ke kasar Indiya

Masallacin, wanda ake yi masa lakabi da Masjid Noori ya nitse ne a madatsar ruwar Phulwaria da ke jihar Bihar a shekarar 1985 yanzu kuma da ruwan ya janye sai ya ga shi ya bayyana bai rushe ba.

Mutanen yankin sun ce masallacin ya dade a wurin kafin a soma ginin madatsar ruwar, wanda hakan ta sa aka kwashe mutanen yankin tare da matsar da su zuwa wani wuri a 1979.

Bayan tashin jama’a an bar masallacin a yashe, a inda bayan gama aikin madatsar ruwar, ruwa ya mamaye yankin baki daya har ya shanye kan masallacin a inda nutse ba a ganin ko alamarsa.

Karancin ruwa da kuma fari da ake fama da shi a yankin a yanzu haka, ta sa madatsar ruwan ta kafe.

Wannan ya sa masallacin ya bayyana, kuma a tsaye k**ar yadda yake a da, bai kuma rushe ba.

Bayyanar masallacin ta sa mutane na ta tururuwa cikin tabo da laka zuwa ganinsa suna kuma shiga cikinsa.

An kiyasta shekarun ginin masallacin 120 a duniya la’akari da tsari da kuma yanayin gininsa, a cewar masana.

Sunan Sa ɗan Soja Dogo, ƙasurgumin ɗan t*adda Ne kuma Marar iman! Na ƙwarai, yana ɗaya daga cikin Miyagvn yan t*addan da...
06/07/2025

Sunan Sa ɗan Soja Dogo, ƙasurgumin ɗan t*adda Ne kuma Marar iman! Na ƙwarai, yana ɗaya daga cikin Miyagvn yan t*addan dake Addabar yankin Anka Bagega ta Jihar Zamfara, Muna Addu'ar Allah ta'ala ya taƙaita Kwanakin Shi tare da Tawagar Sa da Ire-iren Sa Cikin Gaggawa Amen

5/7/2025
✍️~~YARIMA BK DTM

18/06/2025
halin da birnin tel Aviv na ƙasar Isra'ila ke ciki sak**akon hare haren da ƙasar Iran ta kai a matsayin martani ga ƙasar...
15/06/2025

halin da birnin tel Aviv na ƙasar Isra'ila ke ciki sak**akon hare haren da ƙasar Iran ta kai a matsayin martani ga ƙasar Isra'ila

KARON IRAN DA ISRA'ILA Sanannen abu ne muna kin Shi'anci da ma'abutansa sabo da barnar da suke dauke da ita To amma fa s...
15/06/2025

KARON IRAN DA ISRA'ILA

Sanannen abu ne muna kin Shi'anci da ma'abutansa sabo da barnar da suke dauke da ita

To amma fa suna Kalmar shahada dan haka duk da miyagun aqidunsu sun fi mana yahudawa da s**a karyata Annabi Saw s**a yi barna Kala Kala kuma suke ci gaba da yi wanda duniya ba'a taba yin k**ar ta ba da nassin Alqur'ani da Sunnah da zahiri.

Dan haka Addurar mu Allah madaukakin sarki ya karya Israel ta hannun ko waye ma ballantana wanda ya ke Kalmar shahada

Ya yi k**a da wannan yadda Annabi (Saw) su ke yin bakin ciki da nasarar farisawa a kan rumawa kuma su ke murna da nasarar Rumawa kiristoti a kan Farisawa maguzawa a wancen lokacin sabo da su kiristoti su na dangantuwa zuwa ga littafin Attaura da Injeela sun yarda da wasu Annabawa dan haka sun fi kusa da Musulmai

Allah madaukakin sarki ya ce:

الم * غُلِبَتِ الرُّومُ * فِي أَدْنَى الْأَرْضِ وَهُمْ مِنْ بَعْدِ غَلَبِهِمْ سَيَغْلِبُونَ* فِي بِضْعِ سِنِينَ لِلَّهِ الْأَمْرُ مِنْ قَبْلُ وَمِنْ بَعْدُ وَيَوْمَئِذٍ يَفْرَحُ الْمُؤْمِنُونَ

An yi galaba a kan rumawa a makusanciyar kasa amma bayan galaba a kansu su ma za su yi galaba cikin yan shekaru, Al'amarin na Allah ne kafin haka da bayan haka kuma a wannan rana Muminai za su yi farin ciki.

Allah ka ba wa Iraniyawa Nasara a kan Israela ka tarwatsa yahudawa ka kunyata su.

✍️ Dr. Usman Ibrahim Giade (Hafizahullah)

Address

Mahauta Area
Chafe

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Hadi AdamuTsafe posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share