LDD Hausa

LDD Hausa TASHA DOMIN SAMUN LABARAN DUNIYA

19/10/2025

Da dumi-dumi

Gwamnatin Nijeriya ta ce cin jarabawar lissafi “Mathematics” wajibi ne ga daliban Sakandare kafin kammalawa

Labari mai daɗin ji ga ɗaliban NijeriyaA gyare-gyaren da gwamnatin tarayya ke yi game da tsarin shiga jami'o'i da Kwalej...
15/10/2025

Labari mai daɗin ji ga ɗaliban Nijeriya

A gyare-gyaren da gwamnatin tarayya ke yi game da tsarin shiga jami'o'i da Kwalejojin ilimi, ma'aikatar Ilimin Nijeriya ta sanya tsarin yanzun idan dalibi na da credits 5 yana da English, zai iya zuwa jami'a kai tsaye ba dole sai da Math ba, amma ga ɗaliban Art zallah

Lissafi ya zama dole ne ga ɗaliban kimiyya da fasaha da yan social science.

Najeriya a yanzu ta wuce lokacin rashin daidaituwar tattalin arziki — Kashim ShettimaMataimakin Shugaban Ƙasa, Sanata Ka...
09/10/2025

Najeriya a yanzu ta wuce lokacin rashin daidaituwar tattalin arziki — Kashim Shettima

Mataimakin Shugaban Ƙasa, Sanata Kashim Shettima, ya tabbatar wa da masu zuba jari cewa yanzu ne lokacin da ya fi dacewa su zuba jari a Najeriya, domin ƙasar ta fice daga halin rashin daidaiton tattalin arziki.

Ya bayyana haka ne a wajen taron ‘Bauchi Investment Summit 2025’, inda ya ce gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu ta kawar da manyan cikas da s**a hana ci gaban tattalin arzikin ƙasa.

Shettima ya bayyana cewa, a yanzu kudaden da ake kashewa wajen biyan bashi sun sauka zuwa ƙasa da kashi 50 cikin ɗari daga sama da kashi 100, yayin da tattalin arzikin ƙasar (GDP) ya karu zuwa kashi 4.23 cikin ɗari.

Sanata Shettima ya ce an samu ƙaruwa mai yawa a fannin haraji da kudaden shiga da ba na mai ba, wanda ya tashi da kashi 411 cikin ɗari cikin shekara guda. Ya ƙara da cewa ajiyar kudin ƙasar a ƙasashen waje ya kai dala biliyan 43 a watan Satumba 2025, yana mai cewa, “Najeriya ta fita daga halin rashin tabbas, don haka yanzu ne lokacin da ya fi dacewa masu zuba jari su zabi Najeriya.”

Ya bayyana cewa gwamnatin Tinubu ta dauki matakan cire tallafin mai da daidaita tsarin musayar kuɗi domin samar da dawwamammen ci gaba da kwanciyar hankali a harkokin tattalin arziki.

A nasa jawabin, Gwamnan Jihar Bauchi, Sanata Bala Mohammed, ya gode wa Mataimakin Shugaban Ƙasa bisa halartar taron tare da tabbatar da cewa gwamnati za ta aiwatar da shawarwarin da aka cimma a taron. Haka kuma, Sarkin Musulmi, Alhaji Abubakar Sa’ad III, ya yi kira ga gwamnoni da shugabanni na Arewa da su mayar da hankali wajen aiwatar da sak**akon irin waɗannan taruka, yana mai cewa Arewa na da isassun albarkatu da za su iya fitar da yankin daga matsalolin tattalin arziki idan aka yi amfani da su yadda ya k**ata.

Daga  jihar Gombe, wasu matasa sun gudanar da wankan farin ciki da murnar cikar Najeriya shekaru 65 da samun ’yancin kai...
01/10/2025

Daga jihar Gombe, wasu matasa sun gudanar da wankan farin ciki da murnar cikar Najeriya shekaru 65 da samun ’yancin kai daga turawan mallaka, inda s**a fito cikin annashuwa suna watsa ruwa tare da ɗaukar hotuna da bidiyo domin tunawa da wannan rana ta tarihi, alamar kishin ƙasa da nuna soyayya ga darajar ’yanci da Najeriya ta samu.

DA DUMI DUMI: GWAMNAN JIHAR BAUCHI YA SAUKE KWAMISHINAR MATA ZAINAB BABAN TAKKO. An sauke Kwamishinar Harkokin Mata da C...
29/09/2025

DA DUMI DUMI: GWAMNAN JIHAR BAUCHI YA SAUKE KWAMISHINAR MATA ZAINAB BABAN TAKKO.

An sauke Kwamishinar Harkokin Mata da Ci gaban Kananan Yara ta Jihar Bauchi, Hajiya Zainab Baban Takko, daga mukaminta na kwamishina kuma memba a majalisar zartarwa ta jiha.

Lamarin ya samu amincewar Gwamnan Jihar, Sanata Bala Abdulkadir Mohammed, k**ar yadda sanarwa daga mai ba Gwamna shawara na musamman kan harkokin yada labarai, Kwamared Mukhtar Gidado ya sanya ta bayyana, kuma aka rabawa manema labarai a safiyar Litinin.

Sanarwar ta ce, an sallami Kwamishinar Harkokin Mata da Ci gaban Yara, Hajiya Zainab Baban Takko daga mukaminta nan take.”

Mukhtar Gidado ya kara da cewa, “Gwamna yana godiya ga Kwamishinar bisa hidimarta ga jihar tare da yi mata fatan alheri a ayyukanta na gaba.”

Ba a bayyana dalilin daukar matakin ba, amma ko a karshen makon nan, kwamishinar ta kasance cikin tawagar uwargidan gwamnan jihar Bauchi Hajiya Aishatu Bala Abdulkadir Muhammad a lokacin da aka karammata a babban birnin tarayya Abuja.

Inna lillahi wa inna ilaihi raji’unMun samu labarin rasuwar Shugaban Karamar Hukumar Dambam, Hon. Tela Garba Yakubu.Za a...
27/09/2025

Inna lillahi wa inna ilaihi raji’un

Mun samu labarin rasuwar Shugaban Karamar Hukumar Dambam, Hon. Tela Garba Yakubu.

Za a gudanar da sallar jana’izar marigayin da misalin karfe 2:00 na rana a gidansa dake cikin karamar hukumar Misau.

Allah Madaukakin Sarki Ya gafarta masa, Ya jikansa da rahama, Ya kyautata makwancinsa. Ameen.

LABARI DA DUMI DUMI:An Karrama RARARA da Matsayin Doctor a Jamhuriyar Panama.Gwamnoni da ministoti da manyan 'yan siyasa...
20/09/2025

LABARI DA DUMI DUMI:

An Karrama RARARA da Matsayin Doctor a Jamhuriyar Panama.

Gwamnoni da ministoti da manyan 'yan siyasa sun halarci taron karrama mawaki Rarara da digirin digirgir (Doctorate Degree) daga jami’ar European American University da ke Jamhuriyar Panama, kan tallata al’adu da zaburar da matasa da yake yi a Najeriya.

LABARI CIKIN HOTUNA: YAN ACHABA SUNJE OFISHIN VIO BAUCHI S**A YI KOKEN KAN K**A BABURA TA HANYAR ZANGÀ~ZANGÀR LUMANAA ya...
20/09/2025

LABARI CIKIN HOTUNA: YAN ACHABA SUNJE OFISHIN VIO BAUCHI S**A YI KOKEN KAN K**A BABURA TA HANYAR ZANGÀ~ZANGÀR LUMANA

A yau, daruruwan masu aikin achaba a Bauchi sun mamaye ofishin Hukumar VIO domin kai koken su kan abin da s**a kira rashin adalci a yadda ake k**a musu babura saboda plate number, body number, da kuma takardar lasisin tuki (Driver’s License).

Rahotanni sun bayyana cewa, bayan da yan achaban s**a yi cincirindo a ofishin suna bayyana damuwarsu, sai ga wani hali na tashin hankali wanda ya sa jami’an ‘yan sanda s**a shiga tsakani domin kwantar da tarzoma.

Bayan fitowarsu daga ofishin, yan achaban sun bazu cikin gari suna zagaya anguwa-anguwa domin nuna ƙorafin su da kuma neman adalci daga hukumomi.

Hotunan da muka samo sun nuna tarin yan achaba a wurare daban-daban na garin Bauchi, abin da ya jawo hankalin jama’a da ma’aikatan tsaro. Daga Zamani TV

Kasar Nijar zata fara sayan taki daga Jihar Bauchin Nigeria....inji Kwamishinan Noma na jahar Bauchi.
31/08/2025

Kasar Nijar zata fara sayan taki daga Jihar Bauchin Nigeria....inji Kwamishinan Noma na jahar Bauchi.

DA ƊUMI-ƊUMI: Shugaban Kamfanin Manga Automobile Ya Baiwa Nafisa Abdullahi Aminu Kyautar Ƙuɗi N500,000Wane fata zaku yi ...
29/08/2025

DA ƊUMI-ƊUMI: Shugaban Kamfanin Manga Automobile Ya Baiwa Nafisa Abdullahi Aminu Kyautar Ƙuɗi N500,000

Wane fata zaku yi masa?

“Ku ƙarasa mana wannan karin maganar da Bahaushe yake cewa: Birgimar Hankaka.”
26/08/2025

“Ku ƙarasa mana wannan karin maganar da Bahaushe yake cewa: Birgimar Hankaka.”

Albarkacin Ranar Hausa ta Duniya ku bayyana mana wace shekara aka gina Fadar Daurama wadda ake ganin Ita ce Fada ta fark...
26/08/2025

Albarkacin Ranar Hausa ta Duniya ku bayyana mana wace shekara aka gina Fadar Daurama wadda ake ganin Ita ce Fada ta farko da aka fara ginawa a ƙasar Hausa.

Mu haɗu a kwaments sekshon

Address

Bayan Fada
Dambam

Telephone

+2349047247172

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when LDD Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share