LDD Hausa

LDD Hausa TASHA DOMIN SAMUN LABARAN DUNIYA

INNALILLAHI WAINNA ILAIHIRAJIUN...Allah ya yiwa mahaifiyar Malam Nasir El-Rufai tsohon Gwamnan jihar Kaduna Rasuwa.
27/03/2026

INNALILLAHI WAINNA ILAIHIRAJIUN...

Allah ya yiwa mahaifiyar Malam Nasir El-Rufai tsohon Gwamnan jihar Kaduna Rasuwa.

Gwamnan Bauchi Bala Mohammed na shirin komawa APCRahotanni sun nuna cewa gwamnan jihar Bauchi kuma shugaban ƙungiyar gwa...
15/03/2026

Gwamnan Bauchi Bala Mohammed na shirin komawa APC

Rahotanni sun nuna cewa gwamnan jihar Bauchi kuma shugaban ƙungiyar gwamnonin jam’iyyar PDP, Bala Mohammed, na shirin sauya sheka zuwa jam’iyyar APC a cikin makon nan, idan har tattaunawar da ake yi ta yi nasara inji rahotan Arise News.

Majiyoyi sun bayyana cewa gwamnan ya gana da Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu da shugabannin APC, inda ya nuna sha’awarsa ta shiga jam’iyyar mai mulki.

Ana kuma tattaunawa kan sharuddan sauya shekar tasa.

Rahotanni sun ce daga cikin abubuwan da ake tattaunawa akwai ba shi tikitin takarar Sanata, amma ba za a ba shi cikakken iko da tsarin jam’iyyar APC a jihar Bauchi ba, kuma ba zai iya zabar wanda zai gaje shi a matsayin gwamna ba.

An kuma ce an bukaci gwamnan ya ba da hakuri ga Seyi Tinubu, bayan wani rikici da ya faru a bara lokacin da dansa ya soki rabon tallafin Ramadan da Seyi ya yi a Bauchi.

A bangaren Seyi Makinde da wasu jiga-jigan PDP kuwa, an bayyana takaici kan wannan shiri, suna mai cewa sauya shekar shugaban gwamnonin PDP zai iya kara raunana jam’iyyar adawa a kasar.

DAGA GARIN DAMBAM: Almajiran Shiekh Ibrahim zakzaky sun nuna damuwa da kuma tausaya wa irin halin ƙunci da wahala da Yah...
13/03/2026

DAGA GARIN DAMBAM: Almajiran Shiekh Ibrahim zakzaky sun nuna damuwa da kuma tausaya wa irin halin ƙunci da wahala da Yahudawan s**a jefa al’ummar Falasɗinu ciki. Tun kimanin shekaru 77 da s**a gabata, bayan kafuwar ƙasar Isra’ila da goyon bayan Amurka, al’ummar Falasɗinu s**a shiga cikin gwagwarmaya mai tsawo domin kare ƙasarsu da hakkokinsu.

Saboda haka, a duk shekara a Juma’ar ƙarshe ta watan Ramadan, suna gudanar da irin haka a sassa daban-daban na duniya kan gudanar da jerin gwano domin nuna goyon baya ga Falasɗinu, tare da kira ga duniya da ta duba halin da suke ciki, a kuma samar da adalci da zaman lafiya.

DA ƊUMI-ƊUMI: Kotun Ƙoli Za Ta Yanke Hukunci Kan Rikiciɲ Masarautar KanoKotun Ƙolin Najeriya na shirin yanke hukunci kan...
11/03/2026

DA ƊUMI-ƊUMI: Kotun Ƙoli Za Ta Yanke Hukunci Kan Rikiciɲ Masarautar Kano

Kotun Ƙolin Najeriya na shirin yanke hukunci kan rikicin da ya daɗe ana ta muhawara a kansa dangane da masarautar Kano, shari’a da ta jawo hankalin jama’a sosai tare da ƙara zafafa rikicin siyasa da na al’ada a jihar.

Ana sa ran babbar kotun za ta yanke hukunci kan ƙorafe-ƙorafen da s**a taso daga sauye-sauyen da aka yi wa tsarin masarautar, da kuma batun mayar da wasu sarakuna kan kujerunsu tare da amincewa da su.

Majiyoyin da s**a san yadda shari’ar ke gudana sun shaida wa jaridar Kano Times cewa hukuncin zai tantance ko sauya tsarin masarautar ya halatta a doka, sannan kuma ya fayyace ikon Gwamnatin Jihar Kano kan harkokin masarautu.

Menene ra'ayinku?

09/03/2026

Goɓe muna da babban baƙo a cikin shirin mu na shiyasa rigar ƴanci.

LDD HAUSA 🎤🎤🎤

A yayin da azumin bana ya taho gangara yanayin zafin rana na ci gaba da ƙaruwa a wasu sassan Arewacin Najeriya musamman ...
08/03/2026

A yayin da azumin bana ya taho gangara yanayin zafin rana na ci gaba da ƙaruwa a wasu sassan Arewacin Najeriya musamman birnin Kano da jihohin da ke maƙwabtaka da jihar. Yaya yanayin yake a yankunanku?

ƊUMI-ƊUMIƘaramar Hukumar Dambam Ta Kare Kasafin Kuɗi Na Naira Biliyan 8.5 Na Shekarar 2026.Tawaga daga Ƙaramar Hukumar D...
06/03/2026

ƊUMI-ƊUMI

Ƙaramar Hukumar Dambam Ta Kare Kasafin Kuɗi Na Naira Biliyan 8.5 Na Shekarar 2026.

Tawaga daga Ƙaramar Hukumar Dambam ta bayyana a gaban Kwamitin Kasafi da Kason Kuɗi na Majalisar Dokokin Jihar Bauchi domin kare kasafin kuɗin shekarar 2026 da ya kai Naira Biliyan 8.5.

Zaman wanda Hon. Wanzam Mohammed, mai wakiltar Mazabar Sakwa, ya jagoranta ya mayar da hankali kan nazarin yadda za a yi amfani da kuɗaɗen wajen bunƙasa bangarorin ilimi, lafiya, noma, hanyoyi da walwalar al’umma.

Majalisar ta jaddada muhimmancin gaskiya da rikon amana wajen aiwatar da kasafin kuɗin domin tabbatar da cigaban al’ummar Dambam.

Gobara ta tashi a layin ’yan yadi na sabuwar kasuwar garin Azare da ke jihar Bauchi wato Abubakar Tatari Ali Market  cik...
06/03/2026

Gobara ta tashi a layin ’yan yadi na sabuwar kasuwar garin Azare da ke jihar Bauchi wato Abubakar Tatari Ali Market cikin dare.

shaidun gani da ido sun tabbatar aukuwar lamarin a daren Alhamis 5 ga Maris 2026.

Rahotanni sun nuna cewa gobarar ta tashi ne a wani bangare na layin ’yan yadi na kasuwar, inda wutar ta ƙone shaguna da dama.

Masu aikin agaji da jamiʼan kwana-kwana sun kai ɗauki wurin.

Har zuwa lokacin hada wannan rahoto, ba a tantance adadin shagunan da gobarar ta shafa ba.

SOJOJI SUN KWATO KAUYEN MANSUR A ALKALERI, SUN FATATTAKI ’YAN TA’ADDA. Dakarun Rundunar Sojin Najeriya karkashin Divisio...
05/03/2026

SOJOJI SUN KWATO KAUYEN MANSUR A ALKALERI, SUN FATATTAKI ’YAN TA’ADDA.

Dakarun Rundunar Sojin Najeriya karkashin Division ta 3 sun sake tabbatar da ƙwarewarsu bayan sun kwato kauyen Mansur da wasu ƙauyuka da ke kewaye da shi a ƙaramar hukumar Alkaleri ta Jihar Bauchi.

Aikin wanda ke gudana ƙarƙashin Operation BUGUN KARKANDA III ya samu jagorancin Manjo Janar Folusho Oyinlola, Babban Kwamandan Division ta 3 kuma Kwamandan Operation ENDURING PEACE.

Rahotanni daga majiyoyin soja sun bayyana cewa an kai farmaki cikin tsari bayan samun sahihan bayanan sirri kan motsin ’yan ta’adda a yankin. Dakarun sun fatattaki maharan tare da dawo da cikakken iko a kauyen Mansur.

Binciken da aka gudanar bayan kammala samamen ya haifar da kwato bindiga kirar AK-47, wanda jami’an tsaro s**a ce hakan zai rage barazanar tsaro a yankin.

Wannan nasara na ƙara ƙarfafa ƙoƙarin sojoji na tabbatar da zaman lafiya da tsaro ga al’ummar yankin Alkaleri da ma ɗaukacin Bauchi baki ɗaya.

Muna maku barka da shan ruwa a duk inda kuke.
04/03/2026

Muna maku barka da shan ruwa a duk inda kuke.

Gwamna Bala Ya Yi Afuwa Ga Fursunoni 73 a Bauchi, Ya Biya Tara Ta Naira Miliyan 3.8Gwamnan Jihar Bauchi, Bala Abdulkadir...
04/03/2026

Gwamna Bala Ya Yi Afuwa Ga Fursunoni 73 a Bauchi, Ya Biya Tara Ta Naira Miliyan 3.8

Gwamnan Jihar Bauchi, Bala Abdulkadir Mohammed, ya yi afuwa ga fursunoni 73 da ke zaman gidan gyaran hali a fadin jihar, inda ya yi amfani da huruminsa na kundin tsarin mulki karkashin Sashe na 212 na Kundin Tsarin Mulkin Najeriya na 1999 (da aka yi wa kwaskwarima).
Gwamnan ya sanar da hakan ne yayin wani biki da aka shirya domin sakin fursunonin, inda ya bayyana cewa yin amfani da ikon afuwa wani nauyi ne da kundin tsarin mulki ya dora masa, wanda ya ginu kan jin kai, adalci da tausayi—musamman a wannan wata mai alfarma na Ramadan.

Ya ce matakin ya biyo bayan nazari mai zurfi da kuma shawarwarin da Majalisar Ba da Shawara kan Ikon Afuwa ta jihar ta gabatar.

Bugu da kari, gwamnan ya amince da bayar da naira dubu dari (₦100,000) ga kowanne daga cikin wadanda aka yi wa afuwar domin tallafa musu wajen sake shiga cikin al’umma da kuma fara sabuwar rayuwa.

A nasa bangaren, Babban Lauyan Jihar kuma Kwamishinan Shari’a, Hassan Elyakub, ya bayyana cewa gwamnan ya kuma fitar da naira miliyan 3.8 domin biyan tara da diyya ga wasu daga cikin fursunonin da hukuncinsu ya hada da biyan kudade.
Ya kuma yi kira ga bangaren shari’a da su rika la’akari da amfani da hanyoyin hukunci na daban da ba na zaman gidan yari ba, kamar aikin al’umma, musamman ga masu kananan laifuffuka.

Shi ma Kontrolan Hukumar Kula da Gidajen Gyaran Hali ta Najeriya a Jihar Bauchi, Tade Monday, tare da wasu shugabannin addini, sun yaba da wannan mataki na jin kai da gwamnan ya dauka, tare da yin kira ga wadanda aka sako da su kasance masu bin doka da oda, tare da bayar da gudunmawa mai ma’ana ga cigaban al’umma.

04/03/2026

Ana zargin wadannan kalaman ne da Sheikh Alkali Zaria yayi s**a haddasa dakatar da shi daga ci gaba da gabatar da Tafsiri.

Address

Bayan Fada
Dambam

Telephone

+2349047247172

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when LDD Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share