LDD Hausa

LDD Hausa TASHA DOMIN SAMUN LABARAN DUNIYA

Kasar Nijar zata fara sayan taki daga Jihar Bauchin Nigeria....inji Kwamishinan Noma na jahar Bauchi.
31/08/2025

Kasar Nijar zata fara sayan taki daga Jihar Bauchin Nigeria....inji Kwamishinan Noma na jahar Bauchi.

DA ƊUMI-ƊUMI: Shugaban Kamfanin Manga Automobile Ya Baiwa Nafisa Abdullahi Aminu Kyautar Ƙuɗi N500,000Wane fata zaku yi ...
29/08/2025

DA ƊUMI-ƊUMI: Shugaban Kamfanin Manga Automobile Ya Baiwa Nafisa Abdullahi Aminu Kyautar Ƙuɗi N500,000

Wane fata zaku yi masa?

“Ku ƙarasa mana wannan karin maganar da Bahaushe yake cewa: Birgimar Hankaka.”
26/08/2025

“Ku ƙarasa mana wannan karin maganar da Bahaushe yake cewa: Birgimar Hankaka.”

Albarkacin Ranar Hausa ta Duniya ku bayyana mana wace shekara aka gina Fadar Daurama wadda ake ganin Ita ce Fada ta fark...
26/08/2025

Albarkacin Ranar Hausa ta Duniya ku bayyana mana wace shekara aka gina Fadar Daurama wadda ake ganin Ita ce Fada ta farko da aka fara ginawa a ƙasar Hausa.

Mu haɗu a kwaments sekshon

Shugaban Burkina Faso Ya Dakatar Da Bill Gates A Yunƙurin Sa Na Kai Musu TallafiShugaban mulkin soji na ƙasar Burkina Fa...
23/08/2025

Shugaban Burkina Faso Ya Dakatar Da Bill Gates A Yunƙurin Sa Na Kai Musu Tallafi

Shugaban mulkin soji na ƙasar Burkina Faso, Ibrahim Traore, ya dakatar da hamshaƙin attajirin duniya “Bill Gates” wajen yunƙurinsa na kai wa ƙasar tallafin maganin cutar cizon sauro, inda shugaban ya bayyana masa cewar ƙasar sa ba ta yi lalacewar haka ba, na ko'in kula da lamarin kiwon lafiyar 'yan ƙasar ba.

Gwamna Bala Mohammed Ya Isa Gusau Tare da Wasu Gwamnonin PDP Domin Taron Gwamnonin PDPGwamnan Jihar Bauchi kuma shugaban...
23/08/2025

Gwamna Bala Mohammed Ya Isa Gusau Tare da Wasu Gwamnonin PDP Domin Taron Gwamnonin PDP

Gwamnan Jihar Bauchi kuma shugaban gwamnonin jam’iyyar PDP, Sanata Bala Abdulkadir Mohammed, ya isa Gusau, Jihar Zamfara tare da wasu gwamnonin jam’iyyar PDP.

Gwamnonin sun isa jihar ne kafin babban taron PDP Governors’ Forum da za a gudanar gobe.

Ana sa ran taron zai zama dandalin tattaunawa kan muhimman matsalolin kasa, ƙarfafa hadin kan jam’iyya, da tsara tsare-tsare na ingantaccen mulki a jihohinsu da ƙasar baki ɗaya.

A matsayinsa na shugaban gwamnonin, Gwamna Bala Mohammed zai jagoranci tattaunawa kan yadda PDP za ta ci gaba da zama ƙwararriyar jam’iyyar hamayya tare da fitar da manufofin da za su taɓa rayuwar ’yan Najeriya kai tsaye.

Zuwansu Gusau kuma na nuna goyon baya da hadin kai ga gwamnati da mutanen Jihar Zamfara, tare da ci gaba da al’adar gudanar da taron a jere a dukkan jihohin da ke karkashin jam’iyyar.

Ronaldo ya bude sabon babin tarihi da zura kwallo ta 100 a kungiyar Al Nassr da ke Saudiyya, yayin da yawan kwallayensa ...
23/08/2025

Ronaldo ya bude sabon babin tarihi da zura kwallo ta 100 a kungiyar Al Nassr da ke Saudiyya, yayin da yawan kwallayensa ya kai 939 a tarihi

Shin kuna ganin dan wasan zai kafa tarihin zura kwallo guda 1000 nan gaba kafin ya aje takalminsa?

Aliko Dangote ne mai kuɗin duniya na 88, a cewar sabon rahoton mujallar Forbes.
23/08/2025

Aliko Dangote ne mai kuɗin duniya na 88, a cewar sabon rahoton mujallar Forbes.

Wani ɗalibi a Abubakar Tatari Ali Polytechnic Bauchi Ya Rasa Ransa A Hannun Ɓ@r@y1Wani ɗalibi a Abubakar Tatari Ali Poly...
22/08/2025

Wani ɗalibi a Abubakar Tatari Ali Polytechnic Bauchi Ya Rasa Ransa A Hannun Ɓ@r@y1

Wani ɗalibi a Abubakar Tatari Ali Polytechnic (ATAP) da ke Bauchi ya rasa ransa bayan wasu da ba a san ko su waye ba sun kutsa cikin gidan ɗalibai da tsakar dare.

Rahotanni sun bayyana cewa lamarin ya faru ne a misalin ƙarfe uku na dare, inda bata-garin s**a shiga ɗakuna ɗaki-ɗaki suna kwace wa ɗalibai, kafin daga bisani su daba wa ɗalibi mai suna Samuel Mbami, ɗalibin Mass Communication a matakin ND II, wuka, wanda hakan ya yi sanadin mutuwarsa.

Rahotanni daga makarantar sunyi nuni da cewa tuni an ɗauki matakan tsaro tare da haɗa kai da hukumomin tsaro domin kwantar da hankali da kuma hana ɗalibai ɗaukar doka a hannunsu.

Wannan dai ya zo ne kwanaki kaɗan bayan wani hari makamancin haka a Federal Polytechnic Bauchi, duk da cewa ba a samu mutuwa ba a wancan lokacin.

Zamani Tv

Yadda wani bawan Allah ya zube ruwan leda (Pure water) a gefen titin Area 11 dake garin Abuja saboda bayin Allah masu bu...
19/08/2025

Yadda wani bawan Allah ya zube ruwan leda (Pure water) a gefen titin Area 11 dake garin Abuja saboda bayin Allah masu buƙata.

Wanne fata za ku yi masa?

Mun sani cewa kashe Sardaunan Sir, Amadu Bello akayi Sardaunan Sokoto a wani juyin mulkin da akeyi a Nigeriya.Tambaya: K...
19/08/2025

Mun sani cewa kashe Sardaunan Sir, Amadu Bello akayi Sardaunan Sokoto a wani juyin mulkin da akeyi a Nigeriya.

Tambaya: Ku rubuta mana sunan mutumin da ya kashe Sardaunan Sannan wace shekara ce.

‎Gidauniyar Heart to Heart Initiative Ta Raba Tallafi kuɗi Ga Marasa Lafiya a Babban Asibitin Gari Damban. ‎‎Gidauniyar ...
17/08/2025

‎Gidauniyar Heart to Heart Initiative Ta Raba Tallafi kuɗi Ga Marasa Lafiya a Babban Asibitin Gari Damban.

‎Gidauniyar Heart to Heart Initiative ta ci gaba da aikin ta na tallafawa al'umma, inda a yau ta kai ziyara babban asibitin gari domin duba marasa lafiya.

‎A yayin ziyarar, gidauniyar ta zaɓulo wasu marasa lafiya da ke kwance a asibitin kuma ta ba su tallafin kuɗi domin rage musu raɗaɗin halin da suke ciki. Waɗanda s**a amfana da tallafin sun nuna matuƙar farin cikinsu tare da yi wa gidauniyar addu'o'i na alheri.

‎Wanda ya jagoranci aikin, Muhammad Kasko, ya bayyana cewa wannan tallafi wani ɓangare ne na ayyukan alheri da gidauniyar ta saba yi. Wannan karimcin ya sanya farin ciki mai yawa a zukatan marasa lafiyar.

‎A ƙarshe, gidauniyar ta jaddada aniyarta na ci gaba da gudanar da irin waɗannan ayyuka domin tallafawa al'umma, musamman mabukata a fannoni daban-daban.

Address

Bayan Fada, Dambam
Dambam

Telephone

+2349047247172

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when LDD Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share