09/10/2025
Najeriya a yanzu ta wuce lokacin rashin daidaituwar tattalin arziki — Kashim Shettima
Mataimakin Shugaban Ƙasa, Sanata Kashim Shettima, ya tabbatar wa da masu zuba jari cewa yanzu ne lokacin da ya fi dacewa su zuba jari a Najeriya, domin ƙasar ta fice daga halin rashin daidaiton tattalin arziki.
Ya bayyana haka ne a wajen taron ‘Bauchi Investment Summit 2025’, inda ya ce gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu ta kawar da manyan cikas da s**a hana ci gaban tattalin arzikin ƙasa.
Shettima ya bayyana cewa, a yanzu kudaden da ake kashewa wajen biyan bashi sun sauka zuwa ƙasa da kashi 50 cikin ɗari daga sama da kashi 100, yayin da tattalin arzikin ƙasar (GDP) ya karu zuwa kashi 4.23 cikin ɗari.
Sanata Shettima ya ce an samu ƙaruwa mai yawa a fannin haraji da kudaden shiga da ba na mai ba, wanda ya tashi da kashi 411 cikin ɗari cikin shekara guda. Ya ƙara da cewa ajiyar kudin ƙasar a ƙasashen waje ya kai dala biliyan 43 a watan Satumba 2025, yana mai cewa, “Najeriya ta fita daga halin rashin tabbas, don haka yanzu ne lokacin da ya fi dacewa masu zuba jari su zabi Najeriya.”
Ya bayyana cewa gwamnatin Tinubu ta dauki matakan cire tallafin mai da daidaita tsarin musayar kuɗi domin samar da dawwamammen ci gaba da kwanciyar hankali a harkokin tattalin arziki.
A nasa jawabin, Gwamnan Jihar Bauchi, Sanata Bala Mohammed, ya gode wa Mataimakin Shugaban Ƙasa bisa halartar taron tare da tabbatar da cewa gwamnati za ta aiwatar da shawarwarin da aka cimma a taron. Haka kuma, Sarkin Musulmi, Alhaji Abubakar Sa’ad III, ya yi kira ga gwamnoni da shugabanni na Arewa da su mayar da hankali wajen aiwatar da sak**akon irin waɗannan taruka, yana mai cewa Arewa na da isassun albarkatu da za su iya fitar da yankin daga matsalolin tattalin arziki idan aka yi amfani da su yadda ya k**ata.