
28/04/2025
SANARWA: Gwamnatin Jihar Bauchi Ta Bude Shafin Daukar Ma’aikata da Fiye da 10,000 na Guraben Aiki
Gwamnatin Jihar Bauchi, a karkashin jagorancin Mai Girma Gwamna Sanata Bala Abdulkadir Mohammed, ta kaddamar da sabon Shafin Daukar Ma’aikata (recruitment.bauchistate.gov.ng), inda aka bude fiye da 10,000 na guraben aiki a Ma’aikatu, Sassa da Hukumomi (MDAs) daban-daban.
Ana gayyatar matasa da kwararru daga Jihar Bauchi da su ziyarci shafin domin neman guraben aiki a fannoni kamar ilimi, lafiya, gine-gine da sauransu. An tsara tsarin daukar aikin cikin gaskiya, sauri da sauki.