Dambam Emirate Connect

Dambam Emirate Connect Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Dambam Emirate Connect, Media/News Company, Damban.

Dambam Emirate Facebook Connect is a non-profit community-based organization established to promote cultural heritage, peace, youth empowerment, education, humanitarian services, and community development through digital communication and social engagemen

GYARA KAYAN KAWannan hoto dake kasa na hanyar RUWA ne dake Unguwar Kallamu (Ung Bayi) wadda a yanzu haka wani bangare na...
15/08/2025

GYARA KAYAN KA

Wannan hoto dake kasa na hanyar RUWA ne dake Unguwar Kallamu (Ung Bayi) wadda a yanzu haka wani bangare nasa ya ruguje ( Kwalbatin Gidan gona).

Hakan ya faru ne sabida wucewar wata babbar motar daukan yashi waddai bai kamata ache sunbi wannan waje ba.

Muna kira da Shugabanni da mutanen anguwa dasu tashi tsaye don ganin an Saka wadda s**a Bata wannan waje su gyara...
....BAI ZAMA SAUKE MU RABA BA.

MU SAN MAGABATAN MU DAMBAM EMIRATE
11/06/2025

MU SAN MAGABATAN MU

DAMBAM EMIRATE

MAI GIRMA GWAMNAN DAN GIRMAN ALLAH A SANYA MASARAUTAR DAMBAM DOMIN CIKA WANNAN BABBAN ALKAWARI - :Assalamu Alaikum wa Ra...
11/06/2025

MAI GIRMA GWAMNAN DAN GIRMAN ALLAH A SANYA MASARAUTAR DAMBAM DOMIN CIKA WANNAN BABBAN ALKAWARI - :

Assalamu Alaikum wa Rahmatullahi wa Barakatuh.

BUKATAR BADA SANDAR GIRMA GA MASARAUTAR DAMBAM

Da fari muna miƙa godiya ta musamman gare ka bisa irin jagorancin ka nagari da kokarin ci gaba da kake yi domin walwalar al’ummar Jihar Bauchi gaba ɗaya. Lallai ka cancanci yabo da addu’ar alheri a kowane lokaci bisa irin alkhairan da ka dora jihar a kai.

Masarautar Dambam na ɗaya daga cikin tsofaffin masarautu masu tarihi da daraja a Jihar Bauchi. Wannan masarauta ta taka gagarumar rawa a fannin adana al’adu, wanzar da zaman lafiya, da kuma ƙarfafa haɗin kai tsakanin jama’a. Har ila yau, tana da muhimmiyar rawa da take takawa wajen cigaban al’umma da bunƙasar zamantakewa.

Mai girma Gwamna, muna rubuto wannan wasika ne domin neman alfarmarka da kuma gabatar da bukatar mu ta a ba Masarautar Dambam Sandar Girma. Wannan sandar girma za ta ƙara tabbatar da martaba da kima ga masarautar, tare da bunƙasa al’adu da kyakkyawar mu’amala tsakanin gwamnati da jama’ar wannan yanki.

Muna fatan wannan kira namu zai samu karɓuwa a zuciyar Mai Girma Gwamna, wanda aka sani da ƙauna da girmamawa ga al’adun gargajiya da masarautun jihar.

A ƙarshe, muna roƙon Allah ya ci gaba da ƙara wa Mai Girma Gwamna lafiya, jagoranci nagari, da nasarori a dukkan ayyukan ci gaba da kake aiwatarwa a faɗin Jihar Bauchi.

Wassalamu Alaikum wa Rahmatullah.

Mai neman alfarmarka:
QS ABDULSALAM YUSUF BAKUM
A madadin Masarautar Dambam, Jihar Bauchi

MU SAN MAGABATAN MUHUJJOJI NA KARA BAYYANA GAME DA SAMUWAR DAMBAM EMIRATE A SHEKARUN 1800-1915
11/06/2025

MU SAN MAGABATAN MU

HUJJOJI NA KARA BAYYANA GAME DA SAMUWAR DAMBAM EMIRATE A SHEKARUN 1800-1915

MU SAN MAGABATAN MUKadan Daga cikin Hotunan Rubutun da aka AJIYE Dake nuni da Samuwar DAMBAM EMIRATE
11/06/2025

MU SAN MAGABATAN MU

Kadan Daga cikin Hotunan Rubutun da aka AJIYE Dake nuni da Samuwar DAMBAM EMIRATE

Taron Dambam LG Facebook Connect na Shekarar 2025 Ya Samu halartar Manya Baki Daga karamar hukumar Dambam.An Fara wannan...
09/06/2025

Taron Dambam LG Facebook Connect na Shekarar 2025 Ya Samu halartar Manya Baki Daga karamar hukumar Dambam.

An Fara wannan taro Mai muhimmancin a Shekarar 2023 don Sada zumunci tare da fadakar da Matasa masu amfani da kafar sadarwa ta Facebook,

An gabatar da taron Kamar yadda aka Saba Duk Shekara,wannan shine Karo Na uku , ya Kuma Samu halartar manyan mutane Daga sassan karamar hukumar Dambam Kamar su, Mai Girma Hakimin Dambam(wadda limamin Dambam Mal Bappa ) ya wakiltar, Kwamishinan lafiya, Babban Mai Bawa gomna Shawara a Fannin mu amalar Al umma ALH UBA MAI LUMO (WAMBAN DAMBAM wadda Kuma shine Shugaban Taron Na Bana (Chairman of the occasion) , HON Sabo Bappayo (Mainan Misau) ,Iya Dambam, Majikiran Dambam,HON Auduwa Zico, HON Yariman Ibrahim, HON Haladu Dan Jebu Dag,HON Archetec Sadiq Iliya (wadda ya Samu Wakilcin Coordinator NASA)Da sauran manyan baki..

Manyan masu gabatar da makala sune Barr Mukhtar Bello Kwararren Lauya Kuma alkali , tare da Alaeamma Mal Ibrahim Salihu.

Taron Na Bana dai shine mafi kyau da yawan mahalarta,mutane akalla 150 ne s**a halarta Bayan manyan baki..

Sannan Kamar yadda aka Saba an gabatar da makaloli masu muhimmancin da tasiri GA ayyuka da Rayuwar matasan.

Daga DAY.

04/06/2025

LOKUTAN SALLAR IDI BABBA (LAYYA) NA 1446 - 2025 A MASALACEN IDI NA CIKIN GARIN DAMBAM

1. Masallacin Idi na Kofar Fada Dake Kan Hanyar Gurbana Dambam.

Lokaci:- 9:00am

2. Masallacin Idi na JIBWIS Bakin Kasuwa Dambam, dake Harabar Sakatariyar Karamar Hukumar Dambam.

Lokaci: 08:00am.

3. Masallacin JIBWIS Tsohuwar Kasuwa Dambam dake Government Day Secondary School Dambam.

Lokaci: 8:30am

NB. Idan an samu ruwan sama za'a gudanar da Sallah a masallacen Juma'a.

Allah ya Karba mana Ibadodinmu amen.

JSM DAMBAM
8/12/1446 - 4/6/2025

Muhammad Umar Zannan Misau Ya Maye Gurbin Baballe Abubakar a Matsayin Shugaban Stakeholders na APC a Dambam A wani sauyi...
30/05/2025

Muhammad Umar Zannan Misau Ya Maye Gurbin Baballe Abubakar a Matsayin Shugaban Stakeholders na APC a Dambam

A wani sauyi da aka samu a cikin jagorancin masu ruwa da tsaki na jam'iyyar APC a karamar hukumar Dambam, an nada Muhammad Umar Zannan Misau a matsayin sabon shugaban stakeholders, yana maye gurbin Hon. Baballe Abubakar.

Wannan sauyin shugabanci ya biyo bayan amincewar kaso hudu cikin biyar (4/5) na mambobin masu ruwa da tsaki na jam’iyyar a yankin, bisa bukatar samar da maslaha da kuma ci gaban jam’iyyar a matakin ƙaramar hukuma.

A cewar wasu daga cikin jiga-jigan jam’iyyar, wannan mataki na nufin kawo sabbin dabaru da kyakkyawan shugabanci domin karfafa jam’iyyar APC tare da kyautata dangantaka tsakanin membobi.

An bayyana Muhammad Umar Zannan Misau a matsayin dattijo mai hangen nesa da kwarewa, wanda ake sa ran zai taka muhimmiyar rawa wajen daidaita al’amuran jam’iyyar tare da samar da haɗin kai a tsakanin membobi.

Jama’a da dama sun bayyana fatan alheri da addu’ar Allah ya sanya wannan sauyin ya zama alheri ga jam’iyyar, mazauna Dambam, da al’umma gaba ɗaya.

Shout out to my newest followers! Excited to have you onboard! Muddasir M. Alhassan, Sadiya Muhd
28/05/2025

Shout out to my newest followers! Excited to have you onboard! Muddasir M. Alhassan, Sadiya Muhd

Ranar Yara ta Shekarar 2025Karkashin jagorancin HON YAKUBU TELA GARBA wakilin Kare-Karen Misau
28/05/2025

Ranar Yara ta Shekarar 2025
Karkashin jagorancin HON YAKUBU TELA GARBA wakilin Kare-Karen Misau

DANDALIN NISHADIMi Ranar Yara Ta duniya ta Tuna maka game da kuruciyar Ka ?
27/05/2025

DANDALIN NISHADI

Mi Ranar Yara Ta duniya ta Tuna maka game da
kuruciyar Ka ?

26/05/2025

DAGA BAKIN MAI ITA

AYI GYARA DON SAMUN NASARA A ZABEN 2027

Asslm.
Kamar yadda nayi alkawari , To Allah cikin rahamarsa ya tashemu lfy.Masha Allah.bayan tsokaci da nayi kan rashin Jagora daya tilo a Jam,iyarmu (APC) a jiharmu ta Bauchi, Kowana gidan siyasa na bin Jagoransu ne kawai a matakin tafiyarsa. Misali:-Senator Shehu Umaru Buba shine jagoran APC a Jiha, saboda Jama'ar sa sunna cewa shine kadai zababbe kuma tilo a Jiha, a cewar su sauran duk nadaddu ne.

Sai gidan Amb.Yusuf Mai Tama Tugga, haka take a wajen jama,arsa shine Jagora a APC ta jihar Bauchi, dalilin su shine cikakken dan siyasa wadda kuma ya jima yana gwagwarmaya a siyasance kuma haka ya ganta (Siyasa) a gidansu don haka dan na gada yafi dan na koya.

To haka gidan Dr.Ali Pate, Shima a wajen mutanen sa shine Jagoran APC a jihar don ya jima yana gwagwarmaya sannan a siyasance kuma Shima kamar Amb Yusuf Mai Tama Tugga , yayi takara gomna a lokaci dabam-dabam a Jam,iyu dabam dabam.

Abun da kuma ya dauki hankalin mutane shine a APC summit da akayi a Abuja sai ga H.E. Dr Isa Yaguda ya Jagoranci APCn jihar Bauchi a wajen taron duk da kasancewar ministoci biyu a wajen taron, sannan ga tsohon Gomnan Jahar Bauchi H.E. Muhammad A. Abubakar SAN, tsohon Dan takarar Gomna na jam'iyar Air Marshal Sadique Baba Abubakar da Malam Ya,u Darazo (National political Adviser) duk a wajen.

A gaskiya tunda shugaban kasa ne da Kansa ke nada jagora a Jiha, to ya Kamata shugaban jam'iyar APC na kasa H.E Abdullahi Umar Ganduje ya samu shugaban kasa akan samar da Jagora a jihar mu. Idan akayi nawa ko jinkiri to abin ba Zai haifar da nasara ko zaman lfy ma jam,iyar ba, domin kowa yana da mutanen sa kuma shi kadai suke sauraro.

Matsalar jam'iyar a sama shine bata sakawa mutanen da s**a mata wahala da alheri, mutane sai bayan sunyi kowace wahala a neman zabe, amma da zaran anyi sai kaga wassu dabam ne ke samun mukamai, domin harkar ta koma ta wa Ka Sani a sama,Iya sanin mutanen ka a sama iya samun damar ka ko da kuwa kana kasar waje ne a lokacin zaben.

Abinda shugaban kasa yayi shine ,kirkiran jakadu a jihohin da ba APC ke mulki(Gomna)ba, aikinsu lura da duk aiki gomnatin tarayya da aiwatar da tsare-tsare na Gomnatin kamar a baya lokacin mulkin Shehu Shagari Idan ba haka akayi ba to gaskiya talaka a gaba zasu kaurace ma zaben shugaban kasa domin amfanin sa kadanne a wajensu, A yadda tsarin yake tafiya komai a hanun gwamnoni ake badawa to kaga jihar da bata APC ba jama'ar APC sun koma baya ba moriya.

Zamu hadu a gaba kadan don bayani kan matsalolin APC a matakin kananan hukummomi na jahar Bauchi gwargwadon Sanina da fahimtata sakamakon chudanya, Hulda, da bayanai dana tattara a wajen wasu shugabaninta na kananan hukumomin,Dambam kuwa gida ne.

Na gode sai mun hadu a rubutu na gaba.

Kar ku duk rubutun da Kuga nayi Ina turawa zuwa code na N/East zonal chman da kuma na kasa duk ta code nasu don gaskiya nake fada ba kirkire nakeyi kuma sun Sani Sarai.

Fatan mu ayi gyara,Wallahi na kasa shi yake ganin kura-kurai ,Amma manyan mu a sama bata wannan suke ba, sai dai bukatar Kai ( interest).

Idan Akwai gyara ko shawara Ina maraba dashi akan rubutun don nima har yanzu almajiri ne a fagen siyasa , don har yanzu inada Malamai a siyasance a raye wassu kuma sun mutu( Allah yaji kansu da rahama) misali-:Late. Katukan Misau, Kunce Kura na Bauchi, Shatiman Katagum da Alh. Hassan Sale Giwa (Dallatun Misau na Farko) da sauransu.
A raye kuwa Malamai na sauran hudu(4) ALH Mohd Nadada Umar, Amb.Adamu Jumba sai Alh Mohd Dalko ,sai kuma Littafi daya tilo 48-Laws of Power.

Nagode HON BALA ABDULLAHI (VASCO) Tsohon dan majalisar wakilai Kuma tsohon shugaban jam'iyar APC a karamar hukumar DAMBAM

Address

Damban

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Dambam Emirate Connect posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share