Yan uwa na irar dambatta

Yan uwa na irar dambatta Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Yan uwa na irar dambatta, Media, layi tafasa, Dambatta.

Makafi Sunyi Waliman Cika Shekaru 12 Da Sheikh Ibrahim Zakzaky Yasiya Musu Gida Yau Asabar 20/1/2024 , Sarkin Makafin Tu...
23/01/2025

Makafi Sunyi Waliman Cika Shekaru 12 Da Sheikh Ibrahim Zakzaky Yasiya Musu Gida

Yau Asabar 20/1/2024 , Sarkin Makafin Tudun Wadan Zariya ,yakira kwarya kwaryan walima na cikan shekaru 12 da Sheikh Zakzaky yasiya musu Gida .

Tunda farko madakin Makafin Tudun Wadan yayi ma mahalata tuni dacewa a wancan Lokacin sun sha kai komo na niman wanda zai saya musu gida amma s**a rasa, shi dakan shi yarabama mutane takardan niman taimakon sama da mutum talatin na asiya musu gidan dazasu zauna amma hakan bai samu ba.

Shima Marafan Makafin yace bazai taba manta randa Sarkin Makafin yajagorancesu zuwa ga Sheikh Zakzaky a Gidan sa dake Gyallesu kuma cikin girmawa da karramawa, Sheikh Zakzaky ya karbesu hannu biyu ya amsa bukatun su ya siya musu gidan.

Anasa jawabin Sarkin Makafin Tudun Wadan Zariya Malam Dauda yace saboda Wannan abin alheri da faranta zukatan su da sheikh Zakzaky yayi ne, yau Shekaru 12 dai dai s**a shirya walima don nuna godiyyr su ga Malam . Yakara dacewa duk da basuda abinda zasu baiwa Sheikh Zakzaky saidai addu'a, yace hatta lokacin waki'ar Buhari s**an hadu lokaci bayan Lokaci sunaiwa Malam Zakzaky addu'a.

Sarkin Makafin yace yayi burin wannan walima das**a shirya akwai Farfesa Abdullhi Dalladi saboda bazasu manta randa shine Sheikh Zakzaky ya aiko da kudin siyan Gidan ba.

Wakilin yan uwa Musulmai Almajiran Sheikh Zakzaky na Tudun Wadan Zariya Alaramma Malam Sani, wanda aka bukaci yace wani abu a wurin yace lallai bazai manta Lokaci das**aje s**a fadiwa Sarkin Tudun Wada marigayi Sarki Bulaki cewa Sheikh Zakzaky yasiwa makafi gida ba . inda yayi murna kwarai yakara dacewa antabin mutane masu hali su taimaki makafin su siya musu gida abin yaci tura..

Andai addu'a sosai ga su sheikh Zakzaky na Allah yakara musu lafiya da kariya , akarshe aka raba walima aka sallami jama'a, Andai gabatar da Waliman ne a Gidan nasu dake Dikko Road (layin makafi) Tudun Wada Zariya kuma da damansu sun halarta .

Sayyid Ibraheem Zakzaky Office
20/1/2024.

Wanan shine jirgin saman da ake zargin na Sojoji ne ya jefa Bom kan masu taron Maulidin Annabi Muhammadu SAW jiya a kauy...
04/12/2023

Wanan shine jirgin saman da ake zargin na Sojoji ne ya jefa Bom kan masu taron Maulidin Annabi Muhammadu SAW jiya a kauyen Tudun Biri da ke ƙaramar hukumar Igabi Jihar Kaduna. Ana fargabar rasa rayukan mutane da dama Yau An yi jana'izar mutane 78 da s**a rasu sak**akon harin da jirgin sama ya kai kan masu taron maulidi a garin Tudun Biri a Karamar Hukumar Igabi a Jihar Kaduna

Yadda aka gabatar da taron tunawa da Shahadar Ƴar Annabi Muhammad (S), wato Nana Fadima a harabar Ƙabarin Sayyidina Ali,...
30/11/2023

Yadda aka gabatar da taron tunawa da Shahadar Ƴar Annabi Muhammad (S), wato Nana Fadima a harabar Ƙabarin Sayyidina Ali, Annabi Adam da Nuh dake garin Najaf a ƙasar Iraqi.

Amincin Allah ya tabbata a gare ki ya Mamar Hassan da Hussain, Shuwagabannin samarin gidan Aljannah.

😭😭😭

Hotunan Yanda akayi Rakiyan Gwaranzan Shahidai Guda biyu  Zuwa Makwancinsu  Wanda Sukayi Shahada Gurin Muzaharan Nuna  G...
21/11/2023

Hotunan Yanda akayi Rakiyan Gwaranzan Shahidai Guda biyu Zuwa Makwancinsu Wanda Sukayi Shahada Gurin Muzaharan Nuna Goyan Baya Ga Yan Uwanmu Musulmai Al-ummar Palastine
An Rufesu ne a Makwancin Shuhada Shurafa Dake Darur Rahma Zaria

Allah yabamu Albarkacin Shuhada 😭😭😭✌️✌️✌️🤲🤲🤲🤲

.

By al MAHADI SALISU AL AMEEN

Wasu daga cikin Zaratan Dakarun Allah da s**a bada rayuwar su wurin hana Dakarun Shaidan shiga zirin Gaza.Allah ya ƙara ...
31/10/2023

Wasu daga cikin Zaratan Dakarun Allah da s**a bada rayuwar su wurin hana Dakarun Shaidan shiga zirin Gaza.

Allah ya ƙara daukaka ambaton ku, ya yalwata zuriyar ku. Shuhada zaɓin Allah Alfaharin Annabi Muhammad (S).

Al mahadiyu salisu al ameen

Freedom for falastine
24/10/2023

Freedom for falastine

23/10/2023

Jawabin sayyid ali da hassan nassarulla

13/10/2023

Jawabin malam a iran

13/10/2023

95 likes, 6 comments. Check out JANNATUL MAAWA󱢏's video.

Alhamdu lilla malam ya isah lpy
13/10/2023

Alhamdu lilla malam ya isah lpy

aduk lokacin dazan ambaci Allah sai nace Annabi innace Annabi sai nace Fadima innace Fadima sai nace Husain 💕💓💔♥️
23/09/2023

aduk lokacin dazan ambaci Allah sai nace Annabi innace Annabi sai nace Fadima innace Fadima sai nace Husain 💕💓💔♥️

Kashi Na 13:WAƘI’AR TATTAKI 2016 A YANKIN KANOWaƙi'ar Tattakin Arba’in ɗin Imam Hussain (AS) na yankin Kano, ta auku ne ...
02/09/2023

Kashi Na 13:

WAƘI’AR TATTAKI 2016 A YANKIN KANO

Waƙi'ar Tattakin Arba’in ɗin Imam Hussain (AS) na yankin Kano, ta auku ne a ranar Litini 14/11/2016, inda ‘yan sanda s**a tare kan t**i a daidai lokacin da masu tattakin s**a zo wani gari da ake kira Karfi a jihar Kano, s**a buɗe wuta nan take s**a kashe mutane 25 ba.

Jami’an tsaron sun sace gawarwakin waɗanda s**a kashe sun je sun bizne su a ƙabarin bai-ɗaya a lokacin, in banda mutum 8 da aka iya samun gawarwakinsu, wanda Shaikh Sunusi Abdulƙadir ya jagoranci yi musu janaza a garin Kano. Cikin wanda s**a kashe har da jaririya ‘yar kimanin watanni 8 da haihuwa mai suna Zainabul Kubrah.

Mutum takwas ɗin da aka samu gawarwakinsu a lokacin sun haɗa da; Shahida Zainab Abubakar, Shahida Fatima Umar Maiduguri, Shahid Usman Bello Dogo, Shahid Ammar Usman, Shahid Ali Hassan, Shahid Mubarak Hassan, dukkansu an bizne su a maqabartar Rijiyar Lemo, Ramin Tifa a Kano. Sai kuma Shahid Ahmad Ahmad Rangaza da Shahid Husaini Gano, waɗanda aka bizne kowannensu a garinsu.

Sai a ƙarshen shekarar 2020 ne ‘yan uwa s**a gano inda ‘yan sanda s**a bizne ragowar Shahidai 17 da s**a shahadantar a yayin Tattakin s**a je s**a bizne su ɓoye. An gano cewa ‘yan sandan sun bizne su ne a maƙabartar Kalibawa a gefen garin Kano.

Sunayen Shahidai 17 ɗin sune; Shahida Bara’atu Rabilu, Shahid Ibraheem Abubakar, Shahid Mus’ab Sani, Shahid Mujahid Husaini, Shahid Muhammad Sani, Shahid Abdulwaheed Saleh Gantsa, Shahid Ibrahim Shahid Ayuba, Shahid Bilal Haruna, Shahid Baqir Adam Wase, Shahid Hamza Sharu Idris, Shahid Muhammad Lamfalu, Shahid Mustapha Salisu, Shahid Ammar Usman, Shahid Ibrahim Sani Gano, Shahid Ibrahim Idris Adam, Shahid Sahabi Abdullahi Kantama da Shahida Sukaina Isa.

A wannan waƙi’ar, ‘yan sandan sun kuma k**a mutane kusan 90 a farko, s**a ba da belin ƙananan yara daga baya, a yayin da kusan mutum 50 s**a shafe tsawon watanni bakwai a Kurkukun Kano, kafin kotu ta ba da belinsu.

A ranar 5/3/2017 ne gwamnan jihar Kano, Abdullahi Uma

*DAGA TASKAR SA'EED AHMED SA'EED*👇🏻*ASALIN KANO*(Fassarar Tarihin asalin Kano k**ar yadda ya fito daga tsohon kundi mai ...
02/09/2023

*DAGA TASKAR SA'EED AHMED SA'EED*👇🏻

*ASALIN KANO*

(Fassarar Tarihin asalin Kano k**ar yadda ya fito daga tsohon kundi mai suna 'TARIYK ARBAB BALADIL LAZIY MUSAMMA KANO' watau 'KANO CHRONICLE' da turanci, wanda aka gutsura shi a littafin 'HAUSAWA DA MAKWABTAN SU' littafi na biyu' )

Littafin ya soma k**ar haka:-
Wannan tarihi ne na ma'abotan wannan gari wanda ake kira Kano. Shugaban su shi ne Barbushe, shi sai kuma Dala. Shi Dala mutum ne baƙi, kakkaura, ƙaƙƙarfa, mafarauci ƙwarai. Ya kasance ya kan kashe giwa da sandar sa, ya saɓo ta a kansa, yayi tafiya da ita k**ar mil tara.
Ya zo garin nan, ba a san asalin sa ba. Da zuwan sa sai ya gina gidansa a saman dutsen Dala, ya zauna akan sa, shi kaɗai tare da matan sa da ƴaƴansa bakwai, huɗu maza uku mata.
Sunan babban ɗansa Gargaji, shine kakan Buzami.
Buzami kuwa shine uban Barbushe. Shikuwa Barbushe, shine ya gaji dukkan halayen Dala tun daga sanin tsafi har zuwa ƙarfi da sihirinsa da rinjaye ga ƴanuwansa, domin haka sai ya zamo shugaba a zamanin sa.
Ga sunayen fadawan Barbushe;
-Gunzago: gidan sa yana a ƙarƙashin Gwauron dutse daga gabas.
- Gagiwa uban Rubu wanda yake k**a giwa da igiya saboda tsabar ƙarfin sa.
-Gubanasu
-Ibrahimu
-Bardoje
-Nisau (wanda garin Panisau ya samu daga sunan sa)
- Kamfatau
- Duje
-Janberi
-Gamakora
-Safataro
-Hangugu
-Gardangi.
- Ɗan buru: wanda gidan sa yake a jigirya.
-Jan Damisa: wanda gidan sa yake a magwan. Sunan sa Ruma, kuma shine kakan Rumawa. Tun daga Guga har zuwa Salanta ana danganta su da shi, ana ce musu rumawa, su jama'a ne masu yawa.
- Hamɓarau: gidan sa yana Tanagar.
-Gunbarjado: gidan sa yana Panisau, kuma shi ɗa ne ga Nisau.
A wancan zamani na Barbushe, mutane kan taso tun daga Tuda zuwa Ɗan-baƙoshi, haka kuma tun daga Duji har zuwa Ɗankwai, dukkan su suna taruwa a wurin Barbushe a daren salla biyu, domin shine babban su cikin tsafi.
Sunan inda gunkin su yake ajiye 'Kakuwa', sunan gunkin kuwa 'Tsumburbura', domin itaciya ce da ake ambatonta 'Shamus', suna

Labbaika ya hussain from Baghdad
02/09/2023

Labbaika ya hussain from Baghdad

BASAN MIYASA IN NAYI MAGANA YANZU TO YAU ITACE KASUWAR SOCIAL MEDIA BA. Inji Sheikh Yaƙub Yahaya Katsina.______Hassan Ab...
29/08/2023

BASAN MIYASA IN NAYI MAGANA YANZU TO YAU ITACE KASUWAR SOCIAL MEDIA BA. Inji Sheikh Yaƙub Yahaya Katsina.

______Hassan Abubakar Ahmad Katsina

Ban cika son in kare kaina ba, ko ince ni kaza-kaza ba. Mutane da yawa musamman in nayi magana yanzu in nayi magana yau to itace kasuwar Social Media. To, amma muyi ma kanmu adalci, mu zama masu adalci. Kusan Shekera Arba'in Muna wannan harka, Malam ko ƙidi da rawa aka koya mana mun iya wani abu ciki. Ko ƙidi da rayawa ake koya mana a ciki ai mun iya wani abu, bamuce mun iya komi da komi ba don bamu bane Malam Hafizafullah ɗin ba. Amma mun iya wani abu.

Kuma k**ar yadda Malam Mukhutar Sahabi, Allah (Swt) ya gaggauta bayyanarshi, yake cewa, "Ko kamun kura su Malam Hafizafullah s**a koya mana to, mun isa mu kamo ɗan Kure." Kilama harda kurema mun kamoshi". Amma sai kayi magana wani yaro bisa tafin hannunka yake, wani ma kai ka ɗaura auren mahaifiyarsa, da mahaifinshi, ko kaci goron Mahaifiyarshi, ko kaje walimar Auren Mahaifiyarsa da Mahaifinsa. Yanzu Yana ganin baka iya ba. Bak**a san inda aka sa gaba ba. Akwai adalci cikin wannan? Ba adalci.

To amma basusan cewa, ba. Mu mun harbo 'JIRGIN NASU BA''. Bawani Mujaddadi bawan Allah Musilihi, face yana da 'Hawarihiin' Manzon Allah (S.a.w) yana cewa, "duk wani Annabi yana da Hawariyawa". Duk wani Annabi yana da Hawariyawa. Ma'anar Hawariyawa, 'Zaɓaɓɓaɓu na kurkusa, masu Fahimta, waɗanda sune idanun sauran Jama'a. Ba wani Annabi face yana dasu, bawani Mujaddadi face yana dasu. To, amma abun da akeso ace anan Malam Hafizafullah baya dasu waɗanda s**a san inda aka dosa, shi kaɗai ne ya sani, in baya nan shikenan, ba kowa, kuma ba wadda ya iya kaga harka tazo karshe kenan? To wannan shi ne hadafin nasu.

To can s**a nufa abun da ake son a samar kenan, a koya wa Mutane raina kowa, kowa ba bakin komi yake ba. "Duk abun da yake ba dai-dai yake ba, ko da ko dai-dai ne to ba dai-dai bane". Saboda Target ɗin nasu shi ne Malam Hafizafullah, sai ya zamana babu hannun dake dafa masa. Bai da

SHIRYAYYEN MAKIRCI :  INGIZA MAI KAN TURWA A KEWA NIGERIA ! Abin da ke faruwa a Niger, abubuwa na ta canza salo. Da fark...
29/08/2023

SHIRYAYYEN MAKIRCI : INGIZA MAI KAN TURWA A KEWA NIGERIA !

Abin da ke faruwa a Niger, abubuwa na ta canza salo. Da farko wasu na ganin Faransa ce ta kitsa juyin mulkin saboda ƙudirin Bazoum akan samarwa Niger cikakken ƴanci.

Daga Baya kuma sai aka fahimci Sojojin da su kai Juyin mulkin, ba su tare Faransa.

Duk waɗannan zagaye zagaye, aje a dawo, Makircin Kacokam Nigeria aka nufo da shi. Domin a watsa ƙasar.

***
Hawan Ahmed Bola Tinubu shugabancin Nigeria ko kwanaki 100 bai cika , aka zaɓe shi shugaban ECOWAS, saboda wata boyayyen manufa da makirci.

Dalili kuwa tayaya sabon shugaba da zai mulki ƙasa mai cike da tarin matsaloli irin Nigeria a bashi shugabancin ECOWAS daga hawan sa, bayan ga sauran shuwagabannin ƙasashen Afrika ta Yamma da s**a daɗe, kuma suke da gogewa.

****
MAKIRCIN a nan shi ne, tun Bayan Juyin Mulki da aka yi, ECOWAS ta umarci Sojojin Niger su mayar da mulki ga farar hula, ko kuma su ɗauki matakan Soji.

Daga baya kuma ƙasar Nigeria , ta zama ita ke kan gaba wajen zaƙewa da nuna isa a madadin ECOWAS. Har aka ce wai Sojojin Nigeria sun ce Umarni kawai suke jira su afkawa Niger.

Wannan ingiza-mai-kan-turwa da ake wa Nigeria babbar barazana ce ga ƙasashen biyu. Domin ƙasashe ne da guda, ba tayi sai da guda.

Tinubu ba dan Arewa bane, b***e ya san irin danganta da kuma tasirin da Kasar Niger take da shi a Arewa.

Akwai Alamomin Tambayoyi sosai....
-Kashashe nawa ne akai Juyin Mulki me Yasa Sai Niger ?

-Shuwagabannin ECOWAS nawa akai, Ba a san su ba, Me yasa sai TUNIBU ?

-Me yasa ECOWAS ba ta damuwa da Ta'addanci, da Kuma matsin Rayuwar da ake fuskanta ?

Idan Har wannan makirci yayi nasara, Nigeria ta afkawa Niger tabbas abin ba zai yi kyau ba. Domin za a rusa al'umma mai al'adu da addini kusan iri ɗaya.

Garuruwan dake makwabtaka da Nigeria za su shiga cikin bala'i. Domin garuruwan za su zama Military Zones na Sojojin ECOWAS da Sojojin Ƙasashen Waje.

Sannan akwai yiyuwar Sojojin Niger su riƙa mayar da murtani. Misali Gwam

Waye zaije karbala ?
24/08/2023

Waye zaije karbala ?

24/08/2023

Address

Layi Tafasa
Dambatta

Opening Hours

09:00 - 17:00

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Yan uwa na irar dambatta posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Videos

Share

Category