Yan uwa na irar dambatta

Yan uwa na irar dambatta Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Yan uwa na irar dambatta, Media, layi tafasa, Dambatta.

Da'irar Kano da kewaye ta Tara naira na gugan nairai har miliyan ashirin da biyar  (25,000,000) cash a kan Littafin Jago...
18/05/2025

Da'irar Kano da kewaye ta Tara naira na gugan nairai har miliyan ashirin da biyar (25,000,000) cash a kan Littafin Jagorana Sayyid Ibraheem Zakzaky (h) na 'Rayuwata.'
Idan alqaluma s**a qaru daga baya za a ji!
#

AN KADDAMAR DA LITTAFIN “RAYUWATA” A ABUJADaga Ofishin Sayyid Ibraheem Zakzaky (H)Ranar Asabar 28 ga Shawwal 1446 (26/4/...
29/04/2025

AN KADDAMAR DA LITTAFIN “RAYUWATA” A ABUJA

Daga Ofishin Sayyid Ibraheem Zakzaky (H)

Ranar Asabar 28 ga Shawwal 1446 (26/4/2026) aka kaddamar da littafin tarihin Jagoran Harkar Musulunci, Shaikh Ibraheem Zakzaky, wanda ya bayar da kansa mai suna “RAYUWATA”.

A yayin jawabinsa a wajen taron, Shaikh Ibraheem Zakzaky ya bayyana cewa: “Na fadi wani abu a takaice (a gabatarwan littafin), cewa, wannan littafi sakamako ne na tunani da ya zo mana da muke tsare bayan waki’ar da aka sanya ma suna waki’ar Buhari, sai muka ga Allah Ta’ala ya bar mu da rai, tunda sun zo kisa ne kawai, ba yadda za a ce ma an rayu a wannan hali, amma dai da yake Allah ne me raya wa. Kamar yadda nace, Allah da ya kai Musa (AS) hannun Fir’auna, ya raine shi, sai ya kai mu hannunsu kuma, suna so su kashe amma kuma sai suna kula da mu.

“Sai muka ga to tunda dama ta samu, bari mu fadi wani abu wanda watakila in ba mu muka fada ba ba za a sani ba. Ita Malama sai ta yi rubutu; ita ta rubuta ne, ta saka da Ingilishi ‘A brief history of the Islamic movement.’ Ni kuma sai na yi bayani da baki, ina fada tana sajjalawa, muna yi kamar muna magana ne, kamar ma tana min tambayoyi ne ina amsawa, sai dai da aka rubuta littafin ba a sa tambaoyin nata ba, sai aka mai da shi littafi. Amma kamar muna magana ne, idan mutum ya saurari sautin zai ji muna magana ne.” Inji Jagora.

Ya kara da cewa: “Kusan duk abin da na fada duk a takaice ne kuma a gurguje, domin kowane bangare na rayuwar zai zama akwai magana mai tsawo wanda shi kansa zai iya zama littafi. Alal misali, da zan ce zan bayar da labarin karatuna na zaure ne kawai, to ai zan yi littafi ne, amma kawai sai na fada a gurguje kawai. Haka karatun nizamiyya, shima zai iya zama littafi, amma shima sai ya tafi a gurguje. Kuma gidajen yari kowanne littafi ne.”

Shaikh Zakzaky ya yi tsokaci akan wasu daga kusa-kuran da aka samu daga aikin rubuta littafin daga ‘audio’ din bayanan, kamar amfani da kalmar ‘na yi’ maimakon ‘in yi’, da kuma yadda aka rubuta sunayen wasu m

😂😂🤣🤣😂kwalelen wani 😄🤣😄🤣
29/04/2025

😂😂🤣🤣😂kwalelen wani 😄🤣😄🤣

Hisbah ta rushe wajen da aka ce sawun Ma'aiki ya fito a jihar Kano Hukumar Hisbah ta kai samame tare da rushe wani tarin...
25/04/2025

Hisbah ta rushe wajen da aka ce sawun Ma'aiki ya fito a jihar Kano

Hukumar Hisbah ta kai samame tare da rushe wani tarin taɓo da aka ce an ga sawun Annabi Muhammadu Sallallahu alaihi Wasallama a wajen a jihar Kano.

Jaridar Leadership ta rawaito cewa wajen, a unguwar dakata, an share ne domin aikin layin dogo da zai bi ta wajen, amma sai mutane su ka maida shi wani waje mai tsarki na ibada saboda an ga idon ruwa ya na tsatsafowa a daidai wajen wani tarin ƙasa.

An ga wani faifen bidiyo da ya karade kafofin sadarwa, inda mutane ke ta tururuwa su na kallo, wasu kuma na duban ruwan lanufin cewa ruwa ne mai tsarki da za su samu albarka da kuma tafiyar zunubi da samun lafiya tunda wai sawun Annabi ne a wajen.

Sai dai kuma tuni hukumar ta Hisbah, ta bakin Mataimakin Kwamandan hukumar, Malam Mujahideen Aminuddeen ya ce an rushe wajen kuma an kori mutane.

A cewar sa, shirme ne da kuma jahilci, duba da cewa Annabi Sallallahu alaihi Wasallama bai taba taka nahiyar Afrika ba.

Malam Mujahideen ya ce irin wannan ta'adar kan janyo Musulmi ya rasa imanin da, inda yayi kira ga masu aikata hakan su yi gaggawar tuba

INNA LILLAHI WA INNA ILAIHIL RAJI'UNRahotanni da muke samu Yanzu na Cewa An Samu Haɗari Mota Kan Hanyar Abuja Zuwa Kadun...
20/04/2025

INNA LILLAHI WA INNA ILAIHIL RAJI'UN

Rahotanni da muke samu Yanzu na Cewa An Samu Haɗari Mota Kan Hanyar Abuja Zuwa Kaduna Kusan Mutum 100 Sun Rasu.

Yanzu Muke Samu Rahoton Wani Mummunan Hadari Ya Faru Inda Wata Mota Tayi taho mugama da Babbar Motar daukar Shanu a Kan hanyar Kaduna Zuwa Abuja Birnin Tarayyar Najeriya.

Ana hasashen mutune kusa 100+ sun mutu, Da kuma Shanu Masu yawa da s**a mutu.

Allah Ya Jikan Waɗanda S**a Rasu Masu Raunuka Allah Ya basu Lafiya Ameen

Makafi Sunyi Waliman Cika Shekaru 12 Da Sheikh Ibrahim Zakzaky Yasiya Musu Gida Yau Asabar 20/1/2024 , Sarkin Makafin Tu...
23/01/2025

Makafi Sunyi Waliman Cika Shekaru 12 Da Sheikh Ibrahim Zakzaky Yasiya Musu Gida

Yau Asabar 20/1/2024 , Sarkin Makafin Tudun Wadan Zariya ,yakira kwarya kwaryan walima na cikan shekaru 12 da Sheikh Zakzaky yasiya musu Gida .

Tunda farko madakin Makafin Tudun Wadan yayi ma mahalata tuni dacewa a wancan Lokacin sun sha kai komo na niman wanda zai saya musu gida amma s**a rasa, shi dakan shi yarabama mutane takardan niman taimakon sama da mutum talatin na asiya musu gidan dazasu zauna amma hakan bai samu ba.

Shima Marafan Makafin yace bazai taba manta randa Sarkin Makafin yajagorancesu zuwa ga Sheikh Zakzaky a Gidan sa dake Gyallesu kuma cikin girmawa da karramawa, Sheikh Zakzaky ya karbesu hannu biyu ya amsa bukatun su ya siya musu gidan.

Anasa jawabin Sarkin Makafin Tudun Wadan Zariya Malam Dauda yace saboda Wannan abin alheri da faranta zukatan su da sheikh Zakzaky yayi ne, yau Shekaru 12 dai dai s**a shirya walima don nuna godiyyr su ga Malam . Yakara dacewa duk da basuda abinda zasu baiwa Sheikh Zakzaky saidai addu'a, yace hatta lokacin waki'ar Buhari s**an hadu lokaci bayan Lokaci sunaiwa Malam Zakzaky addu'a.

Sarkin Makafin yace yayi burin wannan walima das**a shirya akwai Farfesa Abdullhi Dalladi saboda bazasu manta randa shine Sheikh Zakzaky ya aiko da kudin siyan Gidan ba.

Wakilin yan uwa Musulmai Almajiran Sheikh Zakzaky na Tudun Wadan Zariya Alaramma Malam Sani, wanda aka bukaci yace wani abu a wurin yace lallai bazai manta Lokaci das**aje s**a fadiwa Sarkin Tudun Wada marigayi Sarki Bulaki cewa Sheikh Zakzaky yasiwa makafi gida ba . inda yayi murna kwarai yakara dacewa antabin mutane masu hali su taimaki makafin su siya musu gida abin yaci tura..

Andai addu'a sosai ga su sheikh Zakzaky na Allah yakara musu lafiya da kariya , akarshe aka raba walima aka sallami jama'a, Andai gabatar da Waliman ne a Gidan nasu dake Dikko Road (layin makafi) Tudun Wada Zariya kuma da damansu sun halarta .

Sayyid Ibraheem Zakzaky Office
20/1/2024.

Wanan shine jirgin saman da ake zargin na Sojoji ne ya jefa Bom kan masu taron Maulidin Annabi Muhammadu SAW jiya a kauy...
04/12/2023

Wanan shine jirgin saman da ake zargin na Sojoji ne ya jefa Bom kan masu taron Maulidin Annabi Muhammadu SAW jiya a kauyen Tudun Biri da ke ƙaramar hukumar Igabi Jihar Kaduna. Ana fargabar rasa rayukan mutane da dama Yau An yi jana'izar mutane 78 da s**a rasu sakamakon harin da jirgin sama ya kai kan masu taron maulidi a garin Tudun Biri a Karamar Hukumar Igabi a Jihar Kaduna

Yadda aka gabatar da taron tunawa da Shahadar Ƴar Annabi Muhammad (S), wato Nana Fadima a harabar Ƙabarin Sayyidina Ali,...
30/11/2023

Yadda aka gabatar da taron tunawa da Shahadar Ƴar Annabi Muhammad (S), wato Nana Fadima a harabar Ƙabarin Sayyidina Ali, Annabi Adam da Nuh dake garin Najaf a ƙasar Iraqi.

Amincin Allah ya tabbata a gare ki ya Mamar Hassan da Hussain, Shuwagabannin samarin gidan Aljannah.

😭😭😭

Hotunan Yanda akayi Rakiyan Gwaranzan Shahidai Guda biyu  Zuwa Makwancinsu  Wanda S**ayi Shahada Gurin Muzaharan Nuna  G...
21/11/2023

Hotunan Yanda akayi Rakiyan Gwaranzan Shahidai Guda biyu Zuwa Makwancinsu Wanda S**ayi Shahada Gurin Muzaharan Nuna Goyan Baya Ga Yan Uwanmu Musulmai Al-ummar Palastine
An Rufesu ne a Makwancin Shuhada Shurafa Dake Darur Rahma Zaria

Allah yabamu Albarkacin Shuhada 😭😭😭✌️✌️✌️🤲🤲🤲🤲

.

By al MAHADI SALISU AL AMEEN

Wasu daga cikin Zaratan Dakarun Allah da s**a bada rayuwar su wurin hana Dakarun Shaidan shiga zirin Gaza.Allah ya ƙara ...
31/10/2023

Wasu daga cikin Zaratan Dakarun Allah da s**a bada rayuwar su wurin hana Dakarun Shaidan shiga zirin Gaza.

Allah ya ƙara daukaka ambaton ku, ya yalwata zuriyar ku. Shuhada zaɓin Allah Alfaharin Annabi Muhammad (S).

Al mahadiyu salisu al ameen

Freedom for falastine
24/10/2023

Freedom for falastine

23/10/2023

Jawabin sayyid ali da hassan nassarulla

Address

Layi Tafasa
Dambatta

Opening Hours

09:00 - 17:00

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Yan uwa na irar dambatta posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share

Category