06/05/2026
Matasan jihar Katsina su shar; Gwamnatin Katsina Ta Tallafa Da Naira Miliyan 50, A Lokacin Fara Shirin Horar Da Matasa 500 Sana’o’in Hannu
A ranar Laraba, 6 ga watan Mayun 2026, Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda, PhD, CON, ya halarci bikin yaye matasa 500 da s**a kammala horo kan sana’o’in hannu daban-daban na tsawon wata biyu. Shirin, wanda tsohon Ministan Gidaje da Raya Birane, Arc Ahmad Musa Dangiwa, ya shirya, ya gudana ƙarƙashin haɗin gwiwar Family Homes Fund da Bankin Raya Afirka (African Development Bank).
A yayin bikin, Gwamnatin Jihar Katsina ta bayyana bayar da tallafin Naira miliyan 50 a lokacin fara shirin domin ƙara ƙarfafa shirin da tabbatar da nasarar sa a tsakanin matasa.
Da yake jawabi, Arc Ahmad Musa Dangiwa ya bayyana cewa an zaɓi matasan ne ta hanyar shugabannin ƙananan hukumomi 34 na jihar Katsina, domin tabbatar da adalci, gaskiya da daidaito wajen shigar da wanda za su amfana da shirin.
Ya ƙara da cewa manufar shirin ita ce ƙarfafa matasa su dogara da kansu ta hanyar koyon sana’o’in da za su zama hanyar samun abin dogaro da kai, maimakon jira aikin gwamnati kaɗai.
A wajen taron, an kuma karrama matasa biyu, mace da namiji da s**a fi ƙwazo na kowane fanni cikin fannoni shida da aka horas da kyautar Naira 250,000 kowanne, a matsayin karfafa guiwar ƙwazon da s**a nuna a lokacin horon.
Bayan kammala shirin, an raba wa dukkan matasan kayan fara sana’a. Sana’o’in da aka koya musu sun haɗa da fenti, kafinta, gyaran lantarki, aikin famfo (plumbing) da sauran sana’o’in hannu.
A nasa jawabin, Gwamna Malam Dikko Umaru Radda ya jaddada cewa gwamnatin sa ta mayar da hankali sosai wajen bunƙasa matasa ta hanyar basu ƙwarewa da damar dogaro da kai.
Ya bayyana “Muna son matasan mu su zama masu samar da ayyukan yi, ba masu neman aiki kawai ba. Wannan gwamnati za ta ci gaba da buɗe musu ƙofofin dama a dukkan fannoni na rayuwa. Duk inda aka samu aikin gwamnati, za mu tabbatar matasan mu sun taka rawar gani.”
Gwamnan ya kuma tabbatar da cewa gwamnati za ta haɗa waɗannan matasa da masu kwangilar ayyukan gwamnati domin su samu damar aiki da amfani da horon da s**a samu.
Haka kuma, ya bayyana cewa za a ci gaba da amfani da su a manyan ayyukan gine-ginen gidaje da za a gudanar a Kankia da Radda, domin ƙara samar da ayyukan yi da inganta rayuwar jama’a a jihar Katsina.
MS Ingawa
SSA, Media & Strategy
Katsina State Government
May 6, 2026.