ZANEN ZABO TV

ZANEN ZABO TV Domin Samun ingatattun sahihannin labarai daga tushe da Dumi-duminsu kuyi following din page namu.

24/05/2026

CONFIRMED✅ Tinubu Zai Zaɓi Wanda Zai Masa Mataimaki A Zaɓen 2027

@

Nan wace anguwa ce a garin Daura?
14/05/2026

Nan wace anguwa ce a garin Daura?

04/05/2026
Masu Abin da abinsu yanzu Ahmed Kabiru Ak change yayi signing din nomination form din Mr. President for second term.
03/05/2026

Masu Abin da abinsu yanzu Ahmed Kabiru Ak change yayi signing din nomination form din Mr. President for second term.

ANA WATA GA WANA..Wata sabuwa: Shahararren mawaƙin siyasa nan watau Alhaji Dauda Adamu Kahutu Rarara ya gabatar tare da ...
02/05/2026

ANA WATA GA WANA..

Wata sabuwa: Shahararren mawaƙin siyasa nan watau Alhaji Dauda Adamu Kahutu Rarara ya gabatar tare da ƙaddamar da Hon. Yusuf Jika a matsayin Ɗan Takarar Ɗan majalisar tarayya mai wakiltar Bakori/Danja a Jihar Katsina.

Har ma ya sayo masa takardar shedar tsayawa takara watau (Form), yana ƙaddamar da shi a matsayin Dan takarar Dan majalisar tarayyar mai wakiltar Bakori da Danja da yake goyon baya, yake ƙaddamar dashi a ranar yau asabar 2/5/2026, a garin Kahutu dake cikin ƙaramar hukumar Danja.

Bayan kuma kwamitin sasanta 'yan takara na shiyyar Funtua da Gwamnan Jihar Katsina Malam Dikko Umar Radda ya naɗa ya bayyana Ɗan majalisar tarayyar maici Hon. Abdullahi Balarabe Dabai a matsayin Ɗan takara, wanda zai yima jam'iyyar Apc takara a zaɓen shekara ta 2027.

Abun jira mugani dai ko ya zata kasance akan wannan takaddama da ta kunno kai a cikin Jam'iyyar Apc a Jihar Katsina, musamman a wannan mazaba ta Bakori da Danja duba da shahararren mawaƙin Dauda Adamu Kahutu Rarara yana da ƙarfin tasiri wannan Gwamnati ta shugaban ƙasa Bola Ahmad Tinubu.

Wannan mazaba ta Bakori/Danja ta samu kanta cikin rudani na siyasa tun bayan da aka bayyana Ɗan majalisar tarayya mai wakiltar Bakori/Danja Hon. Abdullahi Balarabe Dabai, a matsayin Ɗan takara, rigingimun siyasa s**a kunno kai a cikin mazabar.

Yanzu haka labarin da muke samu a halin yanzu ɗaya daga cikin wadanda s**a shiga takarar Ɗan majalisar tarayya mai wakiltar Bakori/Danja Hon. Dr. Abduljabbar Surajo Guga yana yunƙurin barin Jam'iyyar Apc, har ma ya bayyana cewa takara 2027, babu fashi.

Bayan bayyana Ɗan majalisar tarayyar maici Hon. Abdullahi Balarabe Dabai a matsayin Ɗan takara, ba tare da an basu damar shiga zaɓen fidda gwani ba, duk da ƙarfin magoya baya da gareshi.

Dan Takarar Daura, Sandamu Mai’adua,  Hon. Yusuf Muhammadu Buhari  ya sayi form dinshi na sha'awar tsayawa Takara  a zab...
01/05/2026

Dan Takarar Daura, Sandamu Mai’adua, Hon. Yusuf Muhammadu Buhari ya sayi form dinshi na sha'awar tsayawa Takara a zabe mai zuwa 2027.

Wani Fatan ku ke me shi?

01/05/2026

Dandazon jama'a Kanan yayin shigowar Dan takardar senator Ahmed Kabiru AK change garin Daura.

INNALILLAHI WA'INNA ILAIHI RAJI'UN: Shahararren Mawaƙin Gargajiya, Alhaji Surajo Mai Asharalle Ya Rasu A Katsina Cikin D...
01/05/2026

INNALILLAHI WA'INNA ILAIHI RAJI'UN: Shahararren Mawaƙin Gargajiya, Alhaji Surajo Mai Asharalle Ya Rasu A Katsina Cikin Daren Jiya Alhamis

Allah Ya Jikansa Da Rahama!

Daga Jamilu Dabawa, Katsina

Rudu Na Neman Shiga Cikin Sasancin Shiyyar Daura..... A dai-dai lokacin da aka gudanar da sasancin fitar da dan takarar ...
29/04/2026

Rudu Na Neman Shiga Cikin Sasancin Shiyyar Daura.....

A dai-dai lokacin da aka gudanar da sasancin fitar da dan takarar Sanata na Shiyyar Daura, an hangi Akitat Ahmed Kabiru Abdullahi ya yanki tikitin tsayawa takarar kujerar a Shalkwatar jam'iyyar APC ta Kasa da ke Abuja.

Kamar yadda rohotanni ke nunawa, sasancin da aka yi ya fito da Shugaban Majalissar Dokoki ta Jihar Katsina Honorabul Nasir Yahaya Daura, a matsayin dan takarar Sanata na Shiyyar.

Sai dai kuma, duk da sasancin an hangi dan takarar ya garzaya Birnin Tarayya Abuja, inda ya yanki tikitin tsayawa takarar.

Alhaji Ahmed Kabiru Abdullahi dai na hannun damar Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu ne, kuma ya rike mukamin Kwamishina a Jihar Legas, duk da cewa shi dan asalin Jihar Katsina ne.

Me Zaku Ce Akan Wannan?

Katsina Teachers Recruitment Gwamnatin Katsina ta amince da daukar Malaman Makaranta 2,158 aiki a fadin jihar. Zaa dauki...
30/03/2026

Katsina Teachers Recruitment

Gwamnatin Katsina ta amince da daukar Malaman Makaranta 2,158 aiki a fadin jihar.

Zaa dauki malamai 1,500 na Primary sai 658 na Secondary.

Masu shaawa sai su ziyarci shafin yanar gizo https://katsinasemis.com/jobs don cikewa.

Address

Daura

Telephone

+2347046484946

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when ZANEN ZABO TV posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share