02/05/2026
ANA WATA GA WANA..
Wata sabuwa: Shahararren mawaƙin siyasa nan watau Alhaji Dauda Adamu Kahutu Rarara ya gabatar tare da ƙaddamar da Hon. Yusuf Jika a matsayin Ɗan Takarar Ɗan majalisar tarayya mai wakiltar Bakori/Danja a Jihar Katsina.
Har ma ya sayo masa takardar shedar tsayawa takara watau (Form), yana ƙaddamar da shi a matsayin Dan takarar Dan majalisar tarayyar mai wakiltar Bakori da Danja da yake goyon baya, yake ƙaddamar dashi a ranar yau asabar 2/5/2026, a garin Kahutu dake cikin ƙaramar hukumar Danja.
Bayan kuma kwamitin sasanta 'yan takara na shiyyar Funtua da Gwamnan Jihar Katsina Malam Dikko Umar Radda ya naɗa ya bayyana Ɗan majalisar tarayyar maici Hon. Abdullahi Balarabe Dabai a matsayin Ɗan takara, wanda zai yima jam'iyyar Apc takara a zaɓen shekara ta 2027.
Abun jira mugani dai ko ya zata kasance akan wannan takaddama da ta kunno kai a cikin Jam'iyyar Apc a Jihar Katsina, musamman a wannan mazaba ta Bakori da Danja duba da shahararren mawaƙin Dauda Adamu Kahutu Rarara yana da ƙarfin tasiri wannan Gwamnati ta shugaban ƙasa Bola Ahmad Tinubu.
Wannan mazaba ta Bakori/Danja ta samu kanta cikin rudani na siyasa tun bayan da aka bayyana Ɗan majalisar tarayya mai wakiltar Bakori/Danja Hon. Abdullahi Balarabe Dabai, a matsayin Ɗan takara, rigingimun siyasa s**a kunno kai a cikin mazabar.
Yanzu haka labarin da muke samu a halin yanzu ɗaya daga cikin wadanda s**a shiga takarar Ɗan majalisar tarayya mai wakiltar Bakori/Danja Hon. Dr. Abduljabbar Surajo Guga yana yunƙurin barin Jam'iyyar Apc, har ma ya bayyana cewa takara 2027, babu fashi.
Bayan bayyana Ɗan majalisar tarayyar maici Hon. Abdullahi Balarabe Dabai a matsayin Ɗan takara, ba tare da an basu damar shiga zaɓen fidda gwani ba, duk da ƙarfin magoya baya da gareshi.