19/05/2026
DA DUMI-DUMI: Pantami Ya Janye Daga Zaben Fidda Gwani Na Takarar Gwamna A Jam’iyyar APC, Saboda Take Hakkin Tsarin Zabe Da Rashin Bin Doka
....Nan bada dadewa ba zamu sanar da matsayarmu ga magoya bayanmu.
...Kudirin tafiyar Pantamiyya na tabbatar da kyakkyawan shugabanci a jihar Gombe da Najeriya yana nan daram, haka kuma matsayinta na yaƙi da rashin adalci ta hanyar bin doka ba zai girgiza ba.
Professor Isa Ali Ibrahim Professor Isa Ali Pantami CON, PhD (Prof/Malam Pantami), ya janye daga takarar gwamnan Jihar Gombe a ƙarƙashin jam’iyyar APC domin nuna rashin amincewarsa da take haƙƙoƙin Dokar Zaɓe ta 2026 da kuma gazawar jam’iyyar wajen samar da hanyoyin sadarwa da bayanan da suke da muhimmanci domin gudanar da sahihin zaɓe.
Lokacin da Prof. Pantami ya amsa ƙiran shugabanni, matasa, mata da sauran masu ruwa da tsaki da s**a nemi ya tsaya takarar gwamnan Jihar Gombe, ya nuna cikakkiyar biyayya da aminci ga APC ta hanyar bin dukkan ƙa’idoji, cika sharuɗɗa da bin hanyoyin da aka shimfiɗa. Shi ne kaɗai ɗan takarar gwamna na APC da ya aika wakili zuwa taron yarjejeniyar zaman lafiya da Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya reshen Jihar Gombe ta shirya a ranar 14 ga Mayu, 2026. Wakilinsa ne kaɗai ya sanya hannu a yarjejeniyar zaman lafiyar a yayin taron.
Duk da irin wannan biyayya da girmamawa ga jam’iyya, an ci gaba da hana shi samun muhimman bayanai. Wasiƙun da lauyoyinsa s**a aika zuwa sassa daban-daban na jam’iyyar suna neman bayanai tare da bayyana damuwa kan yadda za a gudanar da zaɓen fidda gwani na gwamna ba su samu amsa ba ko da tabbacin karɓa ba. Har yanzu ba a magance waɗannan matsaloli ba.
A tsarin dimokuraɗiyya, doka ce ya kamata ta jagoranci komai. Rashin bin Dokar Zaɓe ta 2026 da ƙa’idojin jam’iyya ya sa wannan tsari ya zama maras inganci kuma abin tambaya. Al’ummar Jihar Gombe sun ga abin da ya faru a zaɓukan fidda gwani na Majalisar Tarayya da aka gudanar a ranakun 16 da 18 ga Mayu, 2026. Ƙarfin Prof. Pantami ya dogara ne daga ɗimbin goyon bayan jama’a musamman matasa da mata. Sai dai abin takaici, a zaɓukan da aka gudanar kwanan nan, an ware mambobin jam’iyya na matakin ƙasa (tushe) daga tsarin.
Bayan tattaunawa mai zurfi da masu ruwa da tsaki da kuma nazari kan abubuwan da suke faruwa a Jihar Gombe, Prof. Pantami ya ɗauki matakin janyewa daga zaɓen fidda gwani na gwamna da aka shirya gudanarwa ranar 21 ga Mayu, 2026, a matsayin zanga-zangar lumana. Zanga-zangar lumana wani ginshiƙi ne na dimokuraɗiyya.
Wannan mataki ya samo asali ne daga yadda aka yi watsi da tanade-tanaden Dokar Zaɓe ta 2026 da kuma gazawar shugabancin jam’iyya wajen aiwatar da tsarin da zai tabbatar da sahihin zaɓen fidda gwani. A lokacin zaɓukan fidda gwani na Majalisar Tarayya, babu sahihin zaɓe da aka gudanar a jihar. Bisa ga bayanan da wasu ‘yan takara s**a bayar, ba a sanar da wuraren gudanar da zaɓe, hanyoyin gudanarwa ko tsarin tantance wakilai da masu sa ido ba, amma daga baya aka bayyana sakamako.
Duk da cewa Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya jaddada muhimmancin gudanar da sahihin zaɓen fidda gwani cikin gaskiya da adalci, abin takaici umarninsa ba su samu aiwatarwa ba. Prof. Pantami ya nemi bayanai kan lokaci da wurin tantance wakilai da masu sa ido, hanyoyin tantancewa, kaɗa ƙuri’a da tattara sakamako, da kuma wuraren tattara sakamako. Waɗannan bayanai ya kamata a bai wa dukkan ‘yan takara ba tare da sun nema ba. Zuwa wannan lokaci, babu abin da aka bayar.
Prof. Pantami yana miƙa godiya ta musamman ga matasan da s**a haɗa kuɗi domin sayen fom ɗin nuna sha’awa da tsayawa takara a gare shi. Gudummawar da aka bayar ta fara daga naira dubu biyar zuwa miliyan huɗu, kuma an fitar da rasit tare da wallafa su a kafafen sadarwa. Haka kuma yana gode wa magoya bayansa musamman matasa da mata, da masu gudanar da aiki a rumfunan zaɓe, gundumomi, ƙananan hukumomi da faɗin Jihar Gombe, da ƙungiyar yaɗa labarai, dattawa da Kwamitin Gudanar da Yaƙin Neman Zaɓensa saboda jajircewa da fahimta da s**a nuna. Ya buƙaci dukkan magoya baya su kasance masu natsuwa da bin doka domin kare zaman lafiya da tsaro a jihar. Dimokuraɗiyya tana tafiya ne da doka, zaman lafiya da tsaro.
Tafiyar Pantamiyya za ta sanar da mabiyanta, magoya baya, masu fatan alheri da ɗaliban Prof. Pantami a Jihar Gombe da faɗin Najeriya matakan da za ta ɗauka nan gaba a lokaci mai zuwa. Ƙudirin tafiyar na tabbatar da kyakkyawan shugabanci a Jihar Gombe da Najeriya yana nan daram, haka kuma matsayinta na yaƙi da rashin adalci ta hanyar bin doka ba zai girgiza ba. Ana ƙira ga dukkan mabiyan Malam Pantami da magoya bayansa su ci gaba da kasancewa cikin haɗin kai domin tunkarar matakai masu zuwa a harkar siyasa.
Allah Ya albarkaci Jihar Gombe, Tafiyar Pantamiyya da Tarayyar Najeriya.
Barrista Ibrahim M. Attahir
(A madadin Tafiyar Pantamiyya)
19 ga Mayu, 2026