15/04/2026
Sojoji Sun Ragargaji Maboyar Yan Ta’adda a Dajin Bauchi Tare da Kamo Iyalansu
Rundunar Sojin Kasa ta Najeriya ta tsananta kai samame kan maboyar yan bindiga a jihar Bauchi, inda ta yi nasarar fatattakar sansanoninsu, kamo iyalansu, tare da lalata kayayyakin aikinsu a dajin Madam.
Wani rahoton fafatawa da aka fitar ranar Laraba a Abuja, ya bayyana cewa dakarun Birged ta 33 (33 Artillery Brigade) tare da hadin gwiwar jami’ai daga Ofishin Mashawarcin Shugaban Kasa kan Tsaro (ONSA) ne s**a gudanar da wannan gagarumin aiki.
Nasarorin da aka samu:*
Share Maboya: Sojoji sun share shahararrun sansanonin yan bindigar da s**a hada da sansanin Azuge da Hari, wadanda ke zama matattarar ayyukan masha’a a cikin dajin.
Kawar da Yan Bindiga: An kashe yan bindiga da dama yayin musayar wuta, yayin da sauran s**a raba kafa sakamakon luguden wutar da aka yi musu.
Kamo Iyalai: Jami’an tsaron sun yi ram da mutum 19 da ake kyautata zaton iyalai ne ga yan ta’addan, wadanda s**a hada da mata shida da yara 13.
Kayan da aka kwato:
Dakarun sun gano abubuwa da dama da s**a hada da Albarusan bindigar AK-47, Kwayoyin Tramadol, Kayan sarki da s**a hada da kakin yan sanda da na sojoji (na bogi), Dawakai guda biyu.
Bugu da kari, sojojin sun cinna wa baburan da yan bindigar ke amfani da su wuta domin dakile hanzarinsu da rage musu karfin gudanar da hare-hare.
Haka kuma, rahoton ya bayyana cewa an kai wani samamen na daban a yankin Mainamaji bayan hare-haren jiragen yaki da aka kai baya-bayan nan. Ko da yake ba a hadu da kowa ba, hakan na nuna cewa yan bindigar sun tsere sakamakon matsin lambar da suke fuskanta.
A halin yanzu, dakarun sojin sun mamaye dajin domin tabbatar da cewa yan bindigar ba su sake komawa ba. Rundunar ta sake jaddada kudurinta na ci gaba da matsa lamba har sai an samu cikakken zaman lafiya, tare da kira ga jama’a da su ci gaba da ba su hadin kai da bayanan sirri akan lokaci.