21/02/2026
21/2/2026
LABARUN KARSHEN MAKO A DUKKU, GOMBE
A cikin takaitattun labarun mu na karshen wannan mako, za ku ji cewa:
1- Wakilin Gombe ta Arewa a majalisar Dottijen tarayyar Najeriya Sen. Ibrahim Hassan Dankwambo OON (Talban Gombe) ya fara aikin tonon Rijiyar Burtsatse (Borehole) a unguwar Dugge a cikin garin Dukku.
2- Wakilin Dukku/Nafada a majalisar tarayyar Najeriya Hon. Abdullahi El-Rasheed ya gudanar da aikin jinya kyauta (Medical Outreach) na tsawon kwana uku (3) a General Hospital Dukku.
3- Dan majalisar jiha, mai wakiltar Dukku ta Kudu a majalisar jihar Gombe Hon. Adamu Umar Aminu (A.C) ya gina kawataccen masallacin Juma'a, a unguwar Bakari a cikin garin Dukku.
4- Shugaban karamar hukumar Dukku Hon. Adamu Mohammed Waziri (Wazirin Dukku) ya yi kira ga 'yan social media dasu zama masu tantance zance kafin wallafawa a zaurukan sada zumunta.
5- Sabon shugaban hukumar samar da tsabtaceccen ruwan Sha (RUWASSA) na jihar Gombe Engr Muhammad Ahmed Jibrila ya Sha alwashin ci gaba da tonon Rijiyar Burtsatse (Borehole) a cikin karamin Asibitin Dukku, bayan an samu tsaiko a cikin aikin.
6- Digacin Dugge/Shabewa Mal. Rabi'u Faruku ya amince da nada Mal. Abdul'Aziz Salama a matsayin sabon mai unguwar Bariki, bayan rasuwar mahaifin su (Salaman Dukku)
7- Kungiyar Izalatul Bidi'a mai helkwata a Jos ta yi godiya ga Ministan Sifirin tarayyar Najeriya Sen. Sa'idu Ahmed Alkali (Sarkin Gabas Dukku) bisa saya ma babban masallacin Izala dake unguwar Nayelwa sabuwar Sola, tare sabunta marafen masallacin.
8- Komitin Sharan makabartar Dukku ta yi godiya ga Wazirin Dukku bisa daukar dawainiyar jigilar masu Shara, tare da sayan kayan aiki domin saukake aikin.
9- Anyi yabo da jinjina ga Shugaban karaman hukumar Dukku Hon. Adamu Moh'd Waziri (Wazirin Dukku) ya sabunta ofishin Civil Defence na Dukku, da gyara Lantarkin Gombe Abba, da Kunde.
10- 'Yan sintirin yawon gadin unguwanni cikin dare a Dukku sun cabke Barayin Tumaki misalin karfe 3na dare a unguwar Balu a cikin garin Dukku.
11- Anyi tofin Alatsine akan Barayin da s**a sace Lagireto, da wasu kayayyakin Motar daukar Gawa. Bayan anyi addu'ar alkairi ga duk cikar wadan da s**a bada gudummawa wajen gyara motar.
12- Jam'iyyar APC a karamar hukumar Dukku ta gudanar da bikin sabunta Shugabancin jam'iyya (CONGRESS) a matakin gundumomi, da karamar hukuma.
13- Jam'iyyar PDP tana ci gaba da rasa magoya baya, bayan ficewar Hon. Bala Kelly a jam'iyyar. Sai dai wasu jiga-jigan tafiyar Kelly basu bar jam'iyyar PDP ba.
14- Uwar gidan Ministan Sifirin tarayyar Najeriya Haj. Zainab Sa'idu Alkali (Zinariyar Funakaye) ta aiko ma al'ummar Dukku tallafin abinci albarkacin watan Ramadan.
15- Kungiyar Zakka, da Sadakoki (Charity and Magerity Association Dukku) tana ci gaba da girka abincin buda baki ga marayu, da masu kananan karfi a cikin garin Dukku.
16- Tausayin al'ummar karkara masu Zirga-zirgar diban ruwa a Kogin Dole zuwa kauyukan su ya shiga zukatan al'umma. Bisa karewar tafkunan su, wanda hakan ya tilasta musu safarar neman ruwa a cikin garin Dukku.
17- Tsohon Sakataren din-dindim na jihar Gombe Alh. Abubakar Adamu Sarkin Ruwa (Kawanyan Dukku) ya tsara Social Media din gidan sa, tare da baima 'yan Media takardun shaidar amincewa suyi masa aikin sadarwa a siyasar 2027.
18- Farashin kayan miya ya fadi warwas a Dukku, inda buhun Albasa ya koma Dubu Takwas (8k) a maimakon Dubu Sha uku (13k)
19- Yawan samun Lantarki a Dukku ya karya kasuwar Kankara, da Ruwan sanyi a watan Azumin 1447 a Dukku.
Sai dai masu Kunun sayarwa basu gano dalilin rashin cinikin Kunu a Ramadan din bana ba!
Rahoto
Umar Babagoro Dukku
Gambo Usman Digambus
Shetiman Nakuja