Labarun Kasar Dukku

Labarun Kasar Dukku Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Labarun Kasar Dukku, Media/News Company, Dukku.

21/2/2026LABARUN KARSHEN MAKO A DUKKU, GOMBEA cikin takaitattun labarun mu na karshen wannan mako, za ku ji cewa:1- Waki...
21/02/2026

21/2/2026
LABARUN KARSHEN MAKO A DUKKU, GOMBE

A cikin takaitattun labarun mu na karshen wannan mako, za ku ji cewa:

1- Wakilin Gombe ta Arewa a majalisar Dottijen tarayyar Najeriya Sen. Ibrahim Hassan Dankwambo OON (Talban Gombe) ya fara aikin tonon Rijiyar Burtsatse (Borehole) a unguwar Dugge a cikin garin Dukku.

2- Wakilin Dukku/Nafada a majalisar tarayyar Najeriya Hon. Abdullahi El-Rasheed ya gudanar da aikin jinya kyauta (Medical Outreach) na tsawon kwana uku (3) a General Hospital Dukku.

3- Dan majalisar jiha, mai wakiltar Dukku ta Kudu a majalisar jihar Gombe Hon. Adamu Umar Aminu (A.C) ya gina kawataccen masallacin Juma'a, a unguwar Bakari a cikin garin Dukku.

4- Shugaban karamar hukumar Dukku Hon. Adamu Mohammed Waziri (Wazirin Dukku) ya yi kira ga 'yan social media dasu zama masu tantance zance kafin wallafawa a zaurukan sada zumunta.

5- Sabon shugaban hukumar samar da tsabtaceccen ruwan Sha (RUWASSA) na jihar Gombe Engr Muhammad Ahmed Jibrila ya Sha alwashin ci gaba da tonon Rijiyar Burtsatse (Borehole) a cikin karamin Asibitin Dukku, bayan an samu tsaiko a cikin aikin.

6- Digacin Dugge/Shabewa Mal. Rabi'u Faruku ya amince da nada Mal. Abdul'Aziz Salama a matsayin sabon mai unguwar Bariki, bayan rasuwar mahaifin su (Salaman Dukku)

7- Kungiyar Izalatul Bidi'a mai helkwata a Jos ta yi godiya ga Ministan Sifirin tarayyar Najeriya Sen. Sa'idu Ahmed Alkali (Sarkin Gabas Dukku) bisa saya ma babban masallacin Izala dake unguwar Nayelwa sabuwar Sola, tare sabunta marafen masallacin.

8- Komitin Sharan makabartar Dukku ta yi godiya ga Wazirin Dukku bisa daukar dawainiyar jigilar masu Shara, tare da sayan kayan aiki domin saukake aikin.

9- Anyi yabo da jinjina ga Shugaban karaman hukumar Dukku Hon. Adamu Moh'd Waziri (Wazirin Dukku) ya sabunta ofishin Civil Defence na Dukku, da gyara Lantarkin Gombe Abba, da Kunde.

10- 'Yan sintirin yawon gadin unguwanni cikin dare a Dukku sun cabke Barayin Tumaki misalin karfe 3na dare a unguwar Balu a cikin garin Dukku.

11- Anyi tofin Alatsine akan Barayin da s**a sace Lagireto, da wasu kayayyakin Motar daukar Gawa. Bayan anyi addu'ar alkairi ga duk cikar wadan da s**a bada gudummawa wajen gyara motar.

12- Jam'iyyar APC a karamar hukumar Dukku ta gudanar da bikin sabunta Shugabancin jam'iyya (CONGRESS) a matakin gundumomi, da karamar hukuma.

13- Jam'iyyar PDP tana ci gaba da rasa magoya baya, bayan ficewar Hon. Bala Kelly a jam'iyyar. Sai dai wasu jiga-jigan tafiyar Kelly basu bar jam'iyyar PDP ba.

14- Uwar gidan Ministan Sifirin tarayyar Najeriya Haj. Zainab Sa'idu Alkali (Zinariyar Funakaye) ta aiko ma al'ummar Dukku tallafin abinci albarkacin watan Ramadan.

15- Kungiyar Zakka, da Sadakoki (Charity and Magerity Association Dukku) tana ci gaba da girka abincin buda baki ga marayu, da masu kananan karfi a cikin garin Dukku.

16- Tausayin al'ummar karkara masu Zirga-zirgar diban ruwa a Kogin Dole zuwa kauyukan su ya shiga zukatan al'umma. Bisa karewar tafkunan su, wanda hakan ya tilasta musu safarar neman ruwa a cikin garin Dukku.

17- Tsohon Sakataren din-dindim na jihar Gombe Alh. Abubakar Adamu Sarkin Ruwa (Kawanyan Dukku) ya tsara Social Media din gidan sa, tare da baima 'yan Media takardun shaidar amincewa suyi masa aikin sadarwa a siyasar 2027.

18- Farashin kayan miya ya fadi warwas a Dukku, inda buhun Albasa ya koma Dubu Takwas (8k) a maimakon Dubu Sha uku (13k)

19- Yawan samun Lantarki a Dukku ya karya kasuwar Kankara, da Ruwan sanyi a watan Azumin 1447 a Dukku.
Sai dai masu Kunun sayarwa basu gano dalilin rashin cinikin Kunu a Ramadan din bana ba!

Rahoto
Umar Babagoro Dukku
Gambo Usman Digambus
Shetiman Nakuja

10/2/2026LABARUN BARKA DA SAFIYA A DUKKU, GOMBE A cikin takaitattun labarun mu na safiyar yau Talata 10/2/2026, za ku ji...
10/02/2026

10/2/2026
LABARUN BARKA DA SAFIYA A DUKKU, GOMBE

A cikin takaitattun labarun mu na safiyar yau Talata 10/2/2026, za ku ji cewa:

1- Mai martaba Sarkin Dukku HRH Alh. Haruna Rashid || CON ya yi kira ga al'ummar gundumomin kasar Dukku dasu baima hukumar zabe INEC hadin kai, a yawon gundumomi da take yi domin bin jama'a har inda suke domin yanka musu katin zabe.

2- Mai martaba Sarkin Dukku HRH Alh. Haruna Rashid || CON ya nanata bukatar sauran jam'iyyun siyasa na Dukku suyi koyi da jam'iyyar APC wajen zage Damtse domin ganin jam'iyyun su sunyi karfi. Domin daukaka Dukku a tsakanin kananan hukumomin tarayyar Najeriya.

3- Digacin cikin garin Dukku Alh. Mustafa Umar Marafa ya ziyarci unguwar Tudun Wada a cikin garin Dukku. Domin sada zumunci, tare da gaisawa mutanen unguwa.

4- Hukumar Zabe ta kasa INEC ta kammala kwana biyar (5) a gundumar Gombe Abba na yanka ma al'ummar Gombe Abba katin zabe (PVC) kyauta.

5- Wakilin Dukku ta Arewa a majalisar jihar Gombe Engr. Nasiru Abdulkarim (Barden Arewan Dukku) ya ziyarci garin Wuro Tale domin yankan katin jam'iyyar APC.

6- Makarantar koyar da aikin jinya, da tsabtar muhalli Haruna Rashid Health Science and Technology Dukku ta gudanar da bikin daukar sabbin Dalibai (Matriculation)

7- An yi jana'izar Matashin Dan kasuwa (Mal. Maikudi Usman Mai Manja) wanda mota ta buge shi a kwanan Hashidu, dake hanyar Darazo.

8- Komitin sintirin tabbatar da zaman lafiya ta damke mutanen da ake zargi da lalata da karamar yarinya a Dashi, tare da damkasu hannun jami'an tsaro domin ci gaba da bincike.

9- An yabi kokarin Arch Jamilu Alkali (H.O.D Works and Hounding) bisa tarewa a Kogin Gombe Abba domin ginin ruwan Pompo ya dawo a cikin garin Dukku.

10- Al'ummar garin Bozomshulwa sun kaddamar da fara aikin yashe babban Tafkin garin su. Tare da bude Kokon barar taimakon hukumomi, da masu hannu da shuni.

11- Al'ummar garin Maru sun fara sayan Durom din ruwa akan Farashi naira Dubu Biyu da Dari Biyar (2,500) bayan karewar Tafkin garin su.

Rahoto
Umar Babagoro Dukku

9/2/2026TAKAITATTUN LABARUN KASAR DUKKU, GOMBEA cikin takaitattun labarun mu na yau Litinin 9/2/2026, za ku ji cewa:1- K...
09/02/2026

9/2/2026
TAKAITATTUN LABARUN KASAR DUKKU, GOMBE

A cikin takaitattun labarun mu na yau Litinin 9/2/2026, za ku ji cewa:

1- Karamar hukumar Dukku ta cika shekara Hamsim (50) da samun yancin kai a matsayin karamar hukuma (Local Government)

2- Mai martaba Sarkin Dukku HRH Alh. Haruna Rashid || CON ya bayyana farin ciki, da jin dadi bisa hadin kan manyan 'yan siyasan Dukku, da dunkilewa a jam'iyya guda. Sannan yayi fatan hakan ya zama alkairi ga al'ummar Dukku.

3- Wakilin Gombe ta Arewa a majalisar Dottijen tarayyar Najeriya Sen. Ibrahim Hassan Dankwambo OON (Talban Gombe) ya gabatar da aikin jinya kyauta a babban Asibitin Dukku.

4-Wakilin Gombe ta Arewa a majalisar Dottijen tarayyar Najeriya Sen. Ibrahim Hassan Dankwambo OON (Talban Gombe) ya baima jam'iyyar PDP na Dukku gudummawar naira Miliyan guda (1M)

5- Dan majalisar tarayyar Najeriya mai wakiltar Dukku/Nafada Hon. Abdullahi El-Rasheed ya ziyarci Dukku. Domin yankan katin jam'iyyar APC, bayan ficewar sa daga PDP.

6- Dan majalisar tarayyar Najeriya mai wakiltar Dukku/Nafada Hon. Abdullahi El-Rasheed ya baima jam'iyyar APC na Dukku naira Miliyan 5 (5M)

7- Shugaban karamar hukumar Dukku Hon. Adamu Mohammed Waziri (Wazirin Dukku) ya tura wakilci zuwa helkwatan kenkeshe masu hidimar kasa (NYSC) dake Amada, domin bin sawu wajen ganin Dukku ta samu ingantattun masu hidimar kasa.

8- Hon. Aishatu Jibir Dukku ta amince da nada Komishinan kudi da tattalin arziki na jihar Gombe Mal. Muhammad Magaji a matsayin shugaban kyakkyawar Fata (Renewed Hope Initiative) na karamar hukumar Dukku.

9- An gudanar da bikin siyasa a Dukku ba tare da matasa sun rike wukake, ko sanduna ba! Lamarin daya jawo jam'iyyar APC tayi jinjina ga Wazirin Dukku bisa kokarin sa wajen kawar da siyasar Wukake, da sanduna a Dukku.

10- Cikusun dibar ruwan Tankuna ya fara raguwa a kamfanin Shabewa Table Water dake Waloji, bisa fara dibar ruwa a Wuro Tara.

11- Komitin kula da ruwa na karamar hukumar Dukku ta yi godiya ga Alh. Zubairu Goje bisa damar daya baima Tankuna na diban ruwan a kamfanin sa (Shabewa Table Water Waloji) domin ganin an samu saukin jidon ruwa zuwa cikin garin Dukku.

12- Bakin Tankuna sun fara zuwa Dukku domin gudanar da hada-hadar cinikin ruwa a Dukku, da wasu kauyukan dake fama da matsalar karancin ruwa.

13- Babbar mota ta bankade wani mai karamin mota cikin dare a kusa Gov't Mega College Dukku. Lamarin daya jawo lalacewar karamar motar, da karyewar mai motar.

14- Mal. Muktar Abubakar (S.A Palliative) ya biya ma Dalibai goma (10) marayu, da 'ya'yan marasa galihu kudin rijistan makaranta a Dukku Community Science Secondary School.

15- Makarantar Nurul Islam Dukku ta yi bikin yaye Dalibai, da saukan karatun Al-Qur'ani karo na biyar (5)

Rahoto
Umar Babagoro Dukku

Bibiya da gyara tuntuben alkalami
Comr Huzaifa Ayuba

31/1/2026LABARUN KARSHEN MAKO A DUKKU, GOMBEA cikin takaitattun labarun mu na karshen wannan mako, za ku ji cewa:1- Mai ...
31/01/2026

31/1/2026
LABARUN KARSHEN MAKO A DUKKU, GOMBE

A cikin takaitattun labarun mu na karshen wannan mako, za ku ji cewa:

1- Mai martaba Sarkin Dukku HRH Alh. Haruna Rashid || CON ya tausaya ma masu Zirga-zirga a tsakanin Dukku da Gombe bisa munin lalacewar hanya.

2- Mai martaba Sarkin Dukku HRH Alh. Haruna Rashid || CON ya yi kira ga al'ummar Dukku dasu tashi su yanki katin zabe, domin karfafa ididdigar alkaluman yawan jama'ar Dukku a hukumance.

3- Mai martaba Sarkin Dukku HRH Alh. Haruna Rashid || CON ya yi kira ga dukkan bangarorin siyasa na Dukku dasu tashi su karfafa bangarorin su, domin daukaka Dukku a tsakanin kananan hukumomin jihar Gombe.

4- Mai martaba Sarkin Dukku HRH Alh. Haruna Rashid || CON ya yabi tsarin yankan katin jam'iyyar APC na karamar hukumar Dukku bisa gudanar da aikin ba tare da samun rikici, ko tashin hankali ba.

5- Wakilin Dukku/Nafada a majalisar tarayyar Najeriya Hon. Abdullahi El-Rasheed ya samawa 'yan Dukku uku (3) gurbin aiki a gwamnatin tarayya (Federal Appointment)

6- Komishinan kudi da tattalin arziki na jihar Gombe Mal. Muhammad Gambo Magaji ya nemi hadin kai, da goyon bayan al'ummar Dukku a duk wani mukami, ko kujerar da zai nema a zangon siyasar 2027.

7- Shugaban karamar hukumar Dukku Hon. Adamu Mohammed Waziri (Wazirin Dukku) ya dauki nauyin yi ma ma Dalibai 50 rijistan jarrabawar shiga jami'a (JAMB) a karkashin Gidauniyar Jagaban Tale.

8- Dukku ta samu kwararren Likitan Hakori a babban Asibitin Dukku (General Hospital Dukku)

9- Mai baima gwamnan jihar Gombe shawari akan harkokin masarauta Alh. Damina Sardauna (Hakimin Jamari) ya jagoranci komitin jam'iyyar APC na karamar hukumar Dukku wajen zagayen rangadin wayar da kan al'umma akan muhimmancin yankan katin jam'iyyar APC.

10- An yi yabo, da jinjina ga Ministan Sifirin tarayyar Najeriya Sen. Sa'idu Ahmed Alkali (Sarkin Gabas Dukku) bisa gudummawar miliyoyin daya bayar wajen ganin Dukku ta ciri tuta a yawan masu yankan katin jam'iyyar APC.

11- Yankunan Nappe da Bozomshulwa sun tsunduma ciki matsalar rashin ruwa, bisa karewar tafkuna. Lamarin daya jawo s**a fara sayan jarkar ruwa akan #250 a halin yanzu.

12- An yi ma wasu kananan yara guda 3 bulalar ladabtarwa a cikin kasuwar Dukku, bayan an k**a su da daukar kudin batarwa a shago mai Shinkafa ba tare masaniyar mai shagon ba.

13- An bayyana dacewar jam'iyyun siyasa na karamar hukumar Dukku, da manyan 'yan siyasa su baima Wazirin Dukku goyon baya wajen hana matasa daukar wukake, da sanduna a lokutan bukukuwan siyasa.

14- 'Yan sintirin tabbatar da zaman lafiyar unguwanni a cikin garin Dukku sun tattara kayan sautin masu rawar bata tarbiyyar yara (rawar DJ) a cikin tafkin Gawa, tare da damkasu a hannun jami'an tsaro.

15- Kungiyar DCPA ta bukaci masu aikin gyara hanya daga Dukku zuwa Zange su rinka yayyafa ruwa a hanyar, domin rage karfin kurar da take tashi a lokacin Zirga-zirgar masu ababen hawa. Domin rage yawaitar hadurra a hanyar.

16- Alh. Jamilu Ishiyaku Gwamna (Sardaunan Gombe) ya ziyarci mai martaba Sarkin Dukku, Modibbo Mal. Husaini Dugge, Khalifa Muhammadu Zabairu, da Chiroma Danladi (Sarkin Pawan Dukku)

17- Al'ummar Dukku sun bayyana tausayawa, tare da jimami bisa rasuwar Mal. Muhammad Saddam Abubakar.

Rahoto
Umar Babagoro Dukku
Huzaifa Ayuba
Gambo Usman Digambus

Bibiya da gyara tuntuben alkalami
Comr Huzaifa Ayuba

24/1/2026LABARUN KARSHEN MAKO A DUKKU, GOMBEA cikin takaitattun labarun mu na karshen wannan mako, za ku ji cewa:1- Mai ...
24/01/2026

24/1/2026
LABARUN KARSHEN MAKO A DUKKU, GOMBE

A cikin takaitattun labarun mu na karshen wannan mako, za ku ji cewa:

1- Mai girma gwamnan jihar Gombe Alh. Muhammadu Inuwa Yahaya CON (Dan Majen Gombe) ya bada kwangilar gina Ajujuwan sama da kasa, gyara makarantar Gov't Day Secondary School Dukku West, da Gyaran wasu makaranti a kasar Dukku.

2- Wakilin Gombe ta Arewa a majalisar tarayyar Najeriya Sen. Ibrahim Hassan Dankwambo OON (Talban Gombe) ya tura sakon godiya ga Wazirin Dukku bisa gyara Rijiyar Burtsatse (Borehole) daya tona a babban masallacin Juma'a na mai martaba Sarkin Dukku.

3- Mai martaba Sarkin Dukku HRH Alh. Haruna Rashid || CON ya jagoranci rantsar da sabon shugaban kungiyar Dukku Community Progressive Association (DCPA)

4- Karamar hukumar Dukku ta amince gwamnatin jihar Gombe ta Gina gidajen ma'aikata a tsohon Tiken Shanu dake unguwar Tudun Magaji a cikin garin Dukku.

5- Shugaban karamar hukumar Dukku Hon. Adamu Mohammed Waziri (Wazirin Dukku) ya badu gudummawar manyan Tociloli ga komandojin Rundunar 'yan sintirin yawon gadin unguwanni guda 17 a cikin garin Dukku.

6- Shugaban karamar hukumar Dukku Hon. Adamu Moh'd Waziri (Wazirin Dukku) ya nada Hakimin Jamari Alh. Damina Abubakar a matsayin shugaban komitin bibiyar aikin sabunta rijistan katin jam'iyyar APC, Wakilin Dokan Dukku Sakataren komiti.

7- An samu sama da 400k a Gidauniyar taimakawa iyalan tsoffin Sojojin da s**a rasa rayukan su a aikin Soja, wanda aka kaddamar a sakatariyar karamar hukumar Dukku.

8- Munate 2 sun rigamu gidan gaskiya a Hatsarin motar 'yan kasuwa na Dukku a hanyar tafiya kasuwar Dukkuyel.

9- Dongalin daya daga cikin mutanen Yola, wadan da hatsarin mota ya ritsa da su a Shuwe ya yi batan dabo a babban Asibitin Dukku (General Hospital Dukku) a lokacin da ake kokarin ceto rayuwar sa.

10- Komitin kula da ruwa na karamar hukumar Dukku ta yi jinjina ga al'ummar garin Shabewa bisa aikin tonon Rijiyar da s**a sa a gaba.

11- Kungiyar Dukku Facebook connect, ta kulle group dinta na WhatApps, bisa zargin membobin kungiyar sun kauce asalin hadafin bude group din.

12- Shugabannin kungiyar Dukku Facebook connect sun kai ziyarar jaje ga Matashin da jami'an tsaro s**a Danke, bisa zargin cin zarafi wani a social media. Sannan sun ja kunnen sa akan ya daina rubuce-rubucen da zasu jawo masa cutuwa.

13- Masu nazarin yanayin Kasuwar Buhu a Dukku sun bayyana Rogo a matsayin wanda ya dauki Kashi 40% na buhunan amfanin Gona da aka kawo kasuwar Dukku a makon daya gabata.

14- Wasu sun yi jinjina ga Umar Babagoro bisa kokarin sa a harkokin rubuce-rubuce shafukan sada zumunta na Dukku.

15- Wata kishiya ta zuba ma kishiyar ta ('yar Dukku) tafasashshen ruwan zafi a Gombe! Lamarin daya jawo konewar duk jikin 'yar Dukku, tare da kontar da ita a Asibiti domin karbar magani.

Rahoto
Umar Babagoro Dukku
Gambo Usman Digambus
Shetiman Nakuja

17/1/2026LABARUN KARSHEN MAKO A DUKKU, GOMBEA cikin takaitattun labarun mu na karshen wannan mako, za ku ji cewa:1- Mai ...
17/01/2026

17/1/2026
LABARUN KARSHEN MAKO A DUKKU, GOMBE

A cikin takaitattun labarun mu na karshen wannan mako, za ku ji cewa:

1- Mai martaba Sarkin Gombe Abubakar Shehu Abubakar ||| CRF ya ziyarci Masarautar Dukku, bayan ya kai ziyara makoncin Kakan sa (Modibbo Buba Yero) dake Gombe Abba.

2- Mai martaba Sarkin Dukku HRH Alh. Haruna Rashid || CON ya jagoranci bude Masallacin Juma'a a garin Jauro Adi dake gundumar Lafiya Tale.

3- Mai martaba Sarkin Dukku HRH Alh. Haruna Rashid || CON ya mika bukatar sabon Komishinan 'yan Sanda na jihar Gombe CP Umar Ahmed Shuso ya duba yiwuwar gyara ofishin 'yan Sanda na Dukku, bayan Boko Haram sun Kona shi a shekarun baya.

4- Wakilin Dukku/Nafada a majalisar tarayyar Najeriya Hon. Abdullahi El-Rasheed ya fara aikin tonon Rijiyar Burtsatse (Borehole) a cikin garin Zange.

5- Shugaban karamar hukumar Dukku Hon. Adamu Mohammed Waziri (Wazirin Dukku) ya bada gudummawar taburmai domin bude Masallacin Juma'a na garin Jauro Adi a gundumar Lafiya Tale. Sannan ya bada 1m domin ci gaba da aikin masallacin Bawa Zego

6-Shugaban karamar hukumar Dukku Hon. Adamu Mohammed Waziri (Wazirin Dukku) ya mika bukatar sabon Komishinan 'yan Sanda na jihar Gombe CP Umar Ahmed Shuso ya bude sabbin ofisoshin 'yan Sanda a garuruwan Jarkum, Gadum, Kamba, Bozomshulwa.

7- Sabon Komishinan 'yan Sanda na jihar Gombe CP Umar Ahmed Shuso ya yi yabo, da godiya ga Hon. Aishatu Jibir Dukku (Gimbiyar Dukku) bisa gina ma 'yan Sanda ofishi a Dukku.

8- 'Yan sintirin yawon gadin unguwanni cikin dare a Dukku sun mika sakon godiya ga Wazirin Dukku bisa saya musu manyan Tociloli karo na 2. Domin inganta aikin su na sintirin yawon gadin unguwanni.

9- Wahalar ruwan Sha ya ragu a cikin garin Dukku bisa gyara Tankunan karamar hukuma, da yawan kawo ruwan Pompo.

10- An bude ofishin kare Hakkin Dan Adam a daura da makarantar Dukku Central, a Gabas da shatale-talen tsakiyar garin Dukku.

11- Uwar gidan marigayi Alh. Umar Chiroma Balu (R.O) Haj. Zainab Umar ta kafa Sololi a layuka uku (3) a unguwannin Balu, da Bakari a cikin garin Dukku. Domin kawata gari, da taimakawa a bangaren tsaro.

12- Kungiyar Tagwaye 'yan 2 (Twins Brothers and Sisters Dukku) ta raba gudummawar Lemo ga marasa lafiya a Asibitotin Dukku.

13- Zubar Hawaye a idanun wani karamin yaro ya ankarar da jama'a cewa wata Mata ta wabce Turmin zani (Atampa) a hannun sa ta cika rigar ta da iska. Ranar Litinin da sanyi safiya a cikin kasuwar Dukku.

14- Dan Dampara ya karbi kudin ledan jini a hannun mahaifiyar karamin yaro, ya barta da jiran Gawon Shanu. A babban Asibitin Dukku.

15- Gobara ta cinye gidan PC Abubakar Adamu Abdulkadir (Officer) ba tare da an gano musabbabin tashin ta ba!

16- Gobara ta lashe rumfar tsiire, da rumfar mai Kosai a bakin babbar hanyar tafiya Gombe a Tasha, cikin garin Dukku.

Rahoto
Umar Babagoro Dukku
Muhammad Haruna Gombe Abba

3/1/2026LABARUN KARSHEN MAKO A DUKKU, GOMBEA cikin takaitattun labarun mu na karshen wannan mako, za ku ji cewa:1- Kungi...
03/01/2026

3/1/2026
LABARUN KARSHEN MAKO A DUKKU, GOMBE

A cikin takaitattun labarun mu na karshen wannan mako, za ku ji cewa:

1- Kungiyar N**S ta yi bitar wadan da s**a taimaka wajen fafutukar dawo da yara makaranta a shekarar data gabata 2025, tare da karrama komishinan kudi da tattalin arziki na jihar Gombe Mal. Muhammadu Gambo Magaji bisa zama Zakara a cikin wadan da s**a taimaka.

2- Shugaban karamar hukumar Dukku Hon. Adamu Moh'd Waziri (Wazirin Dukku) ya fara gyare-gyaren guraren da suke zubda ruwan Pompo, a cikin garin Dukku.

3- Gobara ta lashe gadaje, katifu, da shimfudi a dakunan kwanan yara. Tare da cinye kayan dakin matar Mal. Umar Talba (Bayu Talba) a unguwar Bauchi a cikin garin Dukku.

4- Gobara ta cinye Babur din Alh. Julde Maru, a hanyar sa ta dawowa Dukku, daga garin Maru.

5- Barayi sun sace woyoyin Lantarki karo na uku (3) wanda ya kai tsawon Folwaya biyar (5) a tsakanin sabon garin Hashidu da Jauro Adi, a lantarki yankin Malala.

6- Kungiyar Dokoro Progressive Association (DPA) ta gudanar da taron karshen shekara (Annual Meeting) domin tattauna muhimman batutuwa da s**a shafi ci gaban kasar Dokoro. Sannan ta bude Asusun gina Islamiyya.

7- Wasu matasan garin Wuro Waziri a gundumar Wuro Tale sun bar jam'iyyar PDP zuwa APC albarkacin Engr Nasiru Abdulkarim (Barden Arewan Dukku)

8- Makarantar DCSSS ta zo ta farko gasar Rubuta mukala Essay Writing Presentation) wanda kungiyar Dalibai (N**S) ta shirya a tsakanin makarantin sankadare na kasar Dukku.

9- Fudiyya Academy ta lashe gasar amsa tambayoyi (Quiz Competition) wanda kungiyar Dalibai (N**S) ta shirya a tsakanin makarantin sankadare na kasar Dukku.

10- Tsoffin Daliban makarantar DCSSS (class of 2014) sun gudanar da taron karshen shekara (Annual Meeting) a harabar makarantar. Domin sada zumunci, da tattauna muhimman batutuwa da s**a shafe su.

11- Dandalin Dalibai almajiran Shaikh Ibrahim Zakzaky na garin Dukku (Academy Forum of the Islamic Movement in Nigeria, Dukku Chapter) ta karbi bakuncin IVC na shekarar 2026 a matakin jihar Gombe.

Rahoto
Umar Babagoro Dukku
Umar Bappah Dukku

Bibiya da gyara tuntuben alkalami
Comr Huzaifa Ayuba

27/12/2025LABARUN KARSHEN MAKO A DUKKU, GOMBEA cikin takaitattun labarun mu na karshen wannan mako, za ku ji cewa:1- Mai...
27/12/2025

27/12/2025
LABARUN KARSHEN MAKO A DUKKU, GOMBE

A cikin takaitattun labarun mu na karshen wannan mako, za ku ji cewa:

1- Mai martaba Sarkin Dukku HRH Alh. Haruna Rashid || CON ya umurci, Digatai, da Jaurabai dasu daba hadin kai wajen Bincike domin gano masu hannu wajen salwantar kayayyakin makarantin gwamnati bayan aukuwar Iftila'i.

2- Mai martaba Sarkin Dukku HRH Alh. Haruna Rashid || CON ya yi kira ga Daliban Dukku dasu kafa kungiyoyin tsoffin Dalibai, domin sada zumunci, taimaka ma raunanan abokan karatu, da bada gudummawa wajen ganin ci gaban makarantin da s**a yaye Dalibai.

3-Shugaban karamar hukumar Dukku Hon. Adamu Mohammed Waziri (Wazirin Dukku) ya baima mabiya addinin Kirista mazauna Dukku gudummawar naira 1,000,000 domin su gudanar da bikin Kirsimeti cikin walwala a Dukku.

4- Shugaban karamar hukumar Dukku Hon. Adamu Mohammed Waziri (Wazirin Dukku) ya kai ziyarar duba yanayin Lantarki, da matsalar rumbun wutar Lantarki (Transformer) na garin Kunde.

5- Komitin bibiyar barna, tare da Bincike akan wadan da suke da hannu wajen salwantar kayayyakin makarantin gwamnati bayan aukuwar Iftila'i, ta baima Baturen Ilimi na karamar hukumar Dukku wa'adin kwana 7 domin ya tattara bayanan wadan da suke da hannu a cikin barna.

6- Wakilin Dukku/Nafada a majalisar tarayyar Najeriya Hon. Abdullahi El-Rasheed ya fara aikin gina sabbin masallatai a garuruwan Kombi, da Gadum Mai Kasuwa.

7- Hon. Aishatu Jibir Dukku (Gimbiyar Dukku) ta jagoranci bikin yaye Daliban makarantar Darul Ulum.

8- Bata garin matasa sun sari wata baiwar Allah, a lokacin da s**a shiga gidan su cikin dare a Gabas da Sakatariyar karamar hukumar Dukku.

9- Barawo ya yi awun gaba da Babur din wani bawan Allah a lokacin daya ziyarci mahaifiyar shi bayan sallar Isha'i, a unguwar Lafiya a cikin garin Dukku.

10- Wasu masu kiwon Zabbi sun yi kukan zuci bisa yadda bata gari suke harbe musu Zabbi da roban Danko.

11- Adadin yawan masu diban ruwa a Kogin Dole ya fara karuwa, bisa karewar wasu kananan tafkuna a Dukku da kewaye.

12- Adadin mutanen da s**a yanki katin zabe (PVC) a zagaye na farko (First Quarter) a kasar Dukku basu haira 4,000 ba!

Rahoto
Umar Babagoro Dukku

20/12/2025LABARUN KARSHEN MAKO A DUKKU, GOMBEA cikin takaitattun labarun mu na karshen wannan mako, za ku ji cewa:1- Mat...
21/12/2025

20/12/2025
LABARUN KARSHEN MAKO A DUKKU, GOMBE

A cikin takaitattun labarun mu na karshen wannan mako, za ku ji cewa:

1- Mataimakin gomnan jihar Gombe Dr. Mannaseh Daniel Jatau ya tausaya ma al'ummar Dukku bisa munin lalacewar hanyar Dukku zuwa Gombe.

2- Mataimakin gomnan jihar Gombe Dr. Mannaseh Daniel Jatau ya yi jinjina ga mutanen Dukku bisa yadda zaman lafiya yake gudana a tsakanin Fulani, da sauran kabilu a Dukku.

3- Mai martaba Sarkin Dukku HRH Alh. Haruna Rashid || CON ya jagoranci kaddamar da rigakafin Shan Inna a karamar hukumar Dukku.

4- Wakilin Dukku/Nafada a majalisar tarayyar Najeriya Hon. Abdullahi El-Rasheed ya baima kungiyar Dalibai na kasa reshen Dukku (N**S) gudummawar #200,000 domin gudanar da taron kulla zumunci, da seta alkiblar Daliban kasar Dukku.

5- Shugaban karamar hukumar Dukku Hon. Adamu Mohammed Waziri (Wazirin Dukku) ya umurci sashin ayyuka da gidaje (Works and Housing) na karamar hukumar Dukku data fidda layuka a sabbin unguwannin cikin garin Dukku

6- Shugaban karamar hukumar Dukku Hon. Adamu Mohammed Waziri (Wazirin Dukku) ya gyara Rijiyar Burtsatse (Borehole) na Wuro Tara domin Tankuna su rinka dibar ruwa ba tare da sunje Kogin Gombe Abba ba.

7- Shugaban karamar hukumar Dukku Hon. Adamu Mohammed Waziri (Wazirin Dukku) ya kuduri aniyar shiga tsakanin Makiyaya da Manoma a gundumar Wuro Tale.

8- Gobara ta cinye gidan Alh. Maikudi Bobo, unguwar Bakari a cikin garin Dukku

9- Dakin Amariya (Matar Auwal Axim) ya Kone kurmus, a unguwar Lafiya a cikin garin Dukku bisa Gobarar da ba'a gano sanadin ta ba.

10- Allah ya takaita Gobarar garin Hashiduyel dake gundumar Wuro Tale a zauren wani dottijo.

11- An bada shawarin dacewar Wakilin Gombe ta Arewa a majalisar tarayyar Najeriya, ko Dan majalisar tarayya Mai wakiltar Dukku /Nafada dayan su ya saya ma Dukku Motar kashe Gobara.

12- An bude cin kasuwar Lafiya/Tale ranar Talata 16/12/2025 data gabata.

13- Mazauna yankin Wuro Tale sunyi kukan fitina, da rikicin da suke zargin wani bakon haure yake haddasawa a tsakanin Manoma da Makiyaya a yankin su. Sai dai wasu na ganin a zauna a sasanta shine maslaha.

14- Jami'an tsaro sun damke Budurwar data sace Keken Dinkin makwabciyar ta a unguwar Lafiya a cikin garin Dukku.

15- 'Yan sintirin yawon gadin unguwanni cikin dare a Dukku sun dawo bakin aiki, bayan wasu sun yi zargin ana kasafi duk karshen wata ba tare da su ba! Lamarin daya jawo s**a yi barci a gidajen su.

16- Mutanen garin Kamba a gundumar Jamari sun taka ma wasu matasa masu Dampara da sunan yankan katin zabe a yanar Gizo (Online) bayan binciken su ya gano matasan basu cika sharuddan da ake bukata wajen yima mutane rijista a yanar Gizo ba!

17- An tsinci Jaririya cikin dare a kofar shiga filin wasanni (Stadium) na garin Dukku.

18- Tafkin Shabewa ya yi ma jama'a bankwana, lamarin daya jawo marasa karfi zasu fara safarar diban ruwan Sha daga Mbela Bamba zuwa Shabewa.

19- Babban limamin masallacin Bawa a gundumar Kunde Mal. Buba Liman ya rasu!

20- Dillalan gidaje, da filaye sun yi kukan karancin gidajen haya a Dukku. Bayan an sauya ranar daurin auren wasu bisa rashin samun gidajen haya a cikin garin Dukku.

21- A wannan mako Kungiyar Dukku Educational Development Initiative (DEDI) zata fara yi ma Daliban Dukku bitar yadda ake rubuta jarrabawar shiga jami'a (Free Tutorial)

22- Mal. Umar Ahmad (Umaru Amu) ya jagoranci tawagar 'yan Dukku membobin zuwa taro shekara-shekara na kungiyar Hausa Fulani, da aka gudanar a Kaduna.

Rahoto:
Umar Babagoro Dukku
Shetiman Nakuja
Jibril Muhammad Madaki

Bibiya da gyara tuntuben alkalami
Comr Huzaifa Ayuba

13/12/2025LABARUN KARSHEN MAKO A DUKKU, GOMBEA cikin takaitattun labarun mu na karshen wannan mako, za ku ji cewa:1- Min...
13/12/2025

13/12/2025
LABARUN KARSHEN MAKO A DUKKU, GOMBE

A cikin takaitattun labarun mu na karshen wannan mako, za ku ji cewa:

1- Ministan Sifirin tarayyar Najeriya Sen. Sa'idu Ahmed Alkali (Sarkin Gabas Dukku) ya sanya ma babban masallacin Juma'a na Izala dake unguwar Gona a cikin garin Dukku babbar Solar.

2- Mai martaba Sarkin Dukku HRH Alh. Haruna Rashid || CON ya gargadin masu bin sawu wajen karban belin masu aikata miyagun laifuka, musamman bin sawun masu aikata Fyade.

3- Mai martaba Sarkin Dukku HRH Alh. Haruna Rashid || CON ya yi kira ga hakimai, Dagatai, da Jaurabai dasu bada gudummawa wajen wayar da kan mutanen karkara muhimmancin tsabtace muhalli, da tonon Shadda a cikin gidajen, domin barin Kashi a ko'ina.

4- Komishiniyar Mata ta jihar Gombe Hon. Asma'u Mohammed Iganus ta yi kira ga masarautar Dukku data fassara kundin dokoki, da hukunce-hukuncen cin zarafin Mata zuwa harshen Fullanci, da Hausa. Domin saukake ma jama'a fahimtar sakon dake ciki.

5- Shugaban karamar hukumar Dukku Hon. Adamu Mohammed Waziri (Wazirin Dukku) ya fara aikin gyara Tankunan karamar hukumar Dukku, domin ci gaba da samar da ruwan Sha ga al'umma.

6- Shugaban karamar hukumar Dukku Hon. Adamu Mohammed Waziri (Wazirin Dukku) ya dauki dawainiyar mutane 42 zuwa Asibin Makka Specialist Eye Hospital Bauchi, tare da yi masu jinyar ciwon Ido.

7- An zabi Mataimakin shugaban karamar hukumar Dukku Hon. Umar Manu Malala (Mallawan Dukku) a matsayin shugaban kungiyar mataimaka shugabannin kananan hukumomin tarayyar Najeriya (Association of Local Government Vice Chairmen of Nigeria) na tarayyar Najeriya.

8- 'Yan Darikar Tijjaniyya na Dukku sun gudanar da ziyarar shekara-shekara ga Khalifan Tijjaniyya na Dukku Shaikh Muhammadu Zabairu.

9- Shugabar ma'aikar koyawa Mata sana'o'in dogaro da kai (Women Center) na Dukku Mal. Bibatu Wakili ta yi kira ga mazaje dasu baima Matan aure damar zuwa Women Center domin koyon sana'a.

10- Likitoci sunyi nasarar ceto ran matar da makobciyarta tayi mata dukan bankwana da Duniya a unguwar Bauchi a cikin garin Dukku.

11- Anyi kira ga al'ummar kasar Dukku dasu kara kaimi akan yankan katin zabe.

12- Kungiyar Zakka da sadakoki (Charity Association and Margarity) ta yi bikin cika shekara 2 da bude gidan kula da marayu a cikin garin Dukku.

13- Masarautar Gombe Abba, Jamari, Dokoro, Bozomshulwa, da Kunde sun karbi bakoncin masu wayar da kan al'umma dangane da muhimmancin tsabtace muhalli, da barin Kashi a ko'ina.

14- Faduwar farashin amfanin Gona ya sabbaba wasu Manoma sun fara sayar da gonaken su. Domin warware wassu manyan matsalolin su.

15- Magoya bayan Alh. Sani Abdullahi Sambo (Majen Dukku) sunyi liyafar godiya ga Allah bisa samun jagora na gari, wanda ya rungumi al'umma ba tare da nuna bambamcin haifayya, ko kabilanci ba.

16- Hukumar bunkasa kiwon lafiya a matakin farko na tarayyar Najeriya (National Primary Health Care Development Agency) ta karrama shugaban karamar hukumar Dukku Hon. Adamu Mohammed Waziri (Wazirin Dukku) da lambar yabo bisa kwazon sa wajen kula da bangaren kiwon lafiya.

Rahoto
Umar Babagoro Dukku
Muhammad Haruna Gombe Abba
Shetiman Nakuja
Saleh Dahiru Kunde

Bibiya da gyara tuntuben alkalami
Comr Huzaifa Ayuba

6/12/2025LABARUN KARSHEN MAKO A DUKKU, GOMBEA cikin takaitattun labarun mu na karshen wannan mako, za ku ji cewa:1- Mai ...
06/12/2025

6/12/2025
LABARUN KARSHEN MAKO A DUKKU, GOMBE

A cikin takaitattun labarun mu na karshen wannan mako, za ku ji cewa:

1- Mai martaba Sarkin Dukku HRH Alh. Haruna Rashid || CON ya bayyana bukatar karamar hukumar Dukku ta maida Dukku Community Library Solar System. Domin maida dakin Nazari da bincike na Dukku dai-dai da zamani.

2- Mai martaba Sarkin Dukku HRH Alh. Haruna Rashid || CON ya yi kira ga kungiyar Dukku Consultative Forum (DCF) data nazarci hanyar da za'a bi wajen samar da bangaren Nazari, da Bincike a yanar Gizo a cikin Dukku Community Library.

3- Shugaban karamar hukumar Dukku Hon. Adamu Mohammed Waziri (Wazirin Dukku) ya fara aikin gyara, tare da sauya fasalin wasu bangarori na fadar mai martaba Sarkin Dukku.

4- Shugaban karamar hukumar Dukku Hon. Adamu Mohammed Waziri (Wazirin Dukku) ya bada gudummawar 250,000 ga kungiyar Dalibai na karamar hukumar Dukku (N**S) domin gudanar da taron shekara-shekara ga Daliban kasar Dukku.

5- Wakilin Dukku/Nafada a majalisar tarayyar Najeriya Hon. Abdullahi El-Rasheed ya fara aikin gyara Rijiyar Burtsatse (Borehole) din da yake cikin Garejin karamar hukumar Dukku.

6- Al'ummar Dukku sun bayyana farin ciki, tare da murna bisa mukamin da shugaban kasa Bola Ahmad Tinubu ya baima Hon. Aishatu Jirib Dukku (Gimbiyar Dukku) na shugabar Tinubu Renewed Hope Initiative na jihar Gombe.

7- Mai girma Hakimin Jamari Alh. Damana Abubakar ya amince da nada Mal. Ya'u Otega a matsayin Sarkin Gwarin Jamari.

8- Jami'ar jihar Gombe (GSU) ta baima Dukku Community Library littatafai Nazari guda 301, Manyan Tebura (Reading Carrells) guda 12, Kujerun karatu 72, da Kantar aje littafai (Shelves)

9- 'Yan sintirin tabbatar da zaman lafiya a kasar Dukku sunyi nasarar k**a gawurtaccen mai safarar haramtattun kayan maye a garin Kuni, tare da damkashi hannun hukumar yaki da Shan miyagun kwaya (NDLE) domin fiskantar hukunci.

10- Matashin da yayi yunkurin cin mutuncin kawun sa a social media ya yi amai ya lashe. Bayan jami'an tsaro sun bukaci ya kawo hujjoji akan kalaman daya wallafa a shafin sa na Facebook. Lamarin daya jawo masa wallafa sakonnin bada hakuri kala-kala domin gudun fiskantar hukunci.

11- Hon. Abubakar Chiroma (Kansilan Kunde) ya raba Bargunan lullubin maganin sanyi ga al'ummar Kunde.

12- Kungiyar 'yan Achaba na karamar hukumar Dukku ta amince da nada Mal. Ahmed Mohammed (Milo) a matsayin sabon shugaban ta.

13- Kungiyar masu Sayarwa, Gyara, da Chagin Woyoyi na Dukku (GSM Association) ta yi kira ga jama'a dasu kauce bayar da Chajin Waya ba tare da karbar kati ba! Sannan su kauce sayan Wayar da bata da Kwali, ko takardar shaidar ciniki, domin gudun sayan kayan sata.

14- Zuriyar Sarki Shehu Malala sun ziyarci makarantar Sarki Shehu Malala Primary School, tare da karrama Daliban makarantar da littafai albarkacin mariga Sarki Shehu.

15- Matan Darikar Tijjaniyya dana Shi'a sun kulla sabuwar kawance, tare hadin kai, domin kafa tubalin bukukuwan Maulidin 'yar Manzon Allah Nana Fatima (AS)

16- Jami'an duba gari na karamar hukumar Dukku sun gudanar da ziyarorin duba yanayin tsabtar abinci, da abin Sha a cikin kasuwar Dukku.

17- Shugaban karamar hukumar Dukku Hon. Adamu Mohammed Waziri (Wazirin Dukku) ya gudanar da aikin jinya kyauta (Free Medical Outreach) ga masu larurar ciwon Ido a Karamin Asibitin Dukku (PHC Dukku)

Rahoto:
Umar Babagoro Dukku
Ibrahim Jijo Jamari

Bibiya da gyara tuntuben alkalami
Comr Huzaifa Ayuba

Address

Dukku
760401

Telephone

+2348133865636

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Labarun Kasar Dukku posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Shortcuts

Share