Labarun Kasar Dukku

Labarun Kasar Dukku Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Labarun Kasar Dukku, Media/News Company, Dukku.

1/11/2025LABARUN KARSHEN MAKO A DUKKU, GOMBEA cikin takaitattun labarun mu na karshen wannan mako, za ku ji cewa:1- Mai ...
01/11/2025

1/11/2025
LABARUN KARSHEN MAKO A DUKKU, GOMBE

A cikin takaitattun labarun mu na karshen wannan mako, za ku ji cewa:

1- Mai girma gwamnan jihar Gombe Alh. Muhammadu Inuwa Yahaya CON (Dan Majen Gombe) ya turo komitin kula da hulda tsakanin Manoma da Makiyaya zuwa fadar mai martaba Sarkin Dukku. Domin tabbatar da zaman lafiya a tsakanin su.

2- Komishinan Gona, da albarkatun kasa na jihar Gombe Dr. Barnabas Malle ya yi kira ga Manoma da Makiyaya dasu zauna da juna lafiya. Tare da sasanta tsakanin su ba tare da zuwa Kotu ba.

3- Mai martaba Sarkin Dukku HRH Alh. Haruna Rashid || CON ya shawarci Manoma da Makiyaya dasu zama masu aiki da dokoki da ka'idojin gwamnati a guraren Kiwo da Noma.

4- Mai martaba Sarkin Dukku HRH Alh. Haruna Rashid || CON ya karrama Zakarun musabakar Al-Qur'ani na bana 2025 a matakin karamar hukumar Dukku a fadar sa Mai albarka.

5- Wakilin Dukku/Nafada a majalisar tarayyar Najeriya Hon. Abdullahi El-Rasheed ya yi gyara, tare da sabunta ajujuwa, da ofishin Malamai a makarantar Duggiri dake gundumar Malala.

6- Shugaban karamar hukumar Dukku Hon. Adamu Mohammed Waziri (Wazirin Dukku) ya gyara rumbun wutar Lantarki (Transformer) dake bakin sakatariyar karamar hukumar Dukku. Bayan ya shafe shekara 8 baya aiki.

7- Shugaban karamar hukumar Dukku Hon. Adamu Mohammed Waziri (Wazirin Dukku) ya kaddamar da biyan kudaden filaye, da gonaken da aka dauka domin gina filin wasanni (Stadium) irin na zamani a Dukku.

8- Hon. Aishatu Jibir Dukku (Gimbiyar Dukku) ta fidda sanarwar neman masu bukatar karatu a makarantar Legal Nafada, domin ta saya musu Form, sannan tayi musu rijista kyauta.

9- Hon. Jamilu Ahmed Shabewa ya dauki nauyin abincin gwarazan musabakar Al-Qur'ani, wadan da zasu wakilci Dukku a Nafada domin shiga musabaka a matakin jihar Gombe.

10- Al'ummar gundumar Lafiya/Tale sun mika bukatar neman karamar hukumar Dukku ta bude musu kasuwa a garin Lafiya, domin bunkasa tattalin kasar su

11- Al'ummar cikin garin Dukku sun fara kururuwar kukan rashin ruwan Sha a cikin garin Dukku.

12- Zirga-zirgar masu diban ruwa a cikin garin Dukku ya kank**a hajaran majaran a tafkunan Kogin Dole, Tafkin Shabewa, da Mbela Bamba.

13- Mal. Kasimu Gimba ya yi kira ga mai girma gwamnan jihar Gombe, da shugaban karamar hukumar Dukku dasu tausaya wa marayu, da masu kananan karfi wajen biyan kudaden filaye, da gonaken da aka dauka domin gina filin wasanni (Stadium) a Dukku.

14- Matasa masu fafutuka a zaurukan sada zumunta (Internet) domin neman a gyara hanyar Gombe, Dukku, zuwa Darazo sun fidda sabon salon sanya hotunansu cikin hatimi. Domin bayyana ma Duniya damuwar su na neman a gyara musu hanya.

15- Rashin babban Likita a Asibitotin gwamnati a karamar hukumar Dukku ya jefa fargabar tabarbarewar kiwon lafiya a zukatan al'ummar kasar Dukku.

16- Anyi gudun famfalaki a tsakin barawon Babur da masu kolala a General Hospital Dukku. Sai dai masu kolala basu yi nasarar k**a Barawon ba!

17- Barawo ya yi awun gaba da Babur din limamin masu salla a rumfar kasuwa, a dai-dai lokacin da suke sallar Isha'i a cikin kasuwar Dukku.

18- Masu kiwon tsuntsaye suna ci gaba da kukan yadda karnuka suke cinye musu Kaji, saffan Agwagi, da 'ya'yan Tolo-tolo a unguwar Tudun Magaji a cikin garin Dukku.

19- Matan da Wazirin Dukku ya maida su kan turbar Karatu a karkashin shirin AGILE sun fara kwarewa a fannin koyon Dinki da Sakan kayan sanyi na yara.

20- Magoya bayan jam'iyyar PDP sun yi kukan zuci bisa sabon salon Wazirin Dukku na yin zama da Mata magoya bayan su, tare da yi musu ihsani.

21- Manyan Mata jiga-jiga jam'iyyar PDP sunyi gangamin tabbatar da goyon bayan su ga Hon. Bala Kelly a gidan Haj. Adda Iya a unguwar Tudun Magaji a cikin garin Dukku.

22- An bayyana dacewar daukan matakin ladabtarwa akan Manomin daya dauki Mata 22 a Dukku, ya kaisu aiki a gonarsa dake kasar Zange (Feshare) ya barosu. Wasun su a kafa s**a dawo, yayin da wasu s**a sayar da woyoyin su a hanya domin samun kudin Babur din dawowa.

Rahoto
Umar Babagoro Dukku
Shetiman Nakuja
Auwal Seaman
Umar Mohammed Dukku

Bibiya da gyara tuntuben alkalami
Comr Huzaifa Ayuba

25/10/2025LABARUN KARSHEN MAKO A DUKKU, GOMBEA cikin takaitattun labarun mu na karshen wannan mako, za ku ji cewa:1- Mai...
25/10/2025

25/10/2025
LABARUN KARSHEN MAKO A DUKKU, GOMBE

A cikin takaitattun labarun mu na karshen wannan mako, za ku ji cewa:

1- Mai martaba Sarkin Dukku HRH Alh. Haruna Rashid || CON ya yabi Daliban da s**a nuna kwazo a musabakar karatun Al-Qur'ani, a gasar tantance Daliban da zasu wakilci Dukku a musabakar da za'a gabatar a matakin jihar Gombe.

2- Mai martaba Sarkin Dukku HRH Alh. Haruna Rashid || CON ya yi kira ga iyayen yara dasu kara kokari wajen tura 'ya'yan su makaranta, tare da tura su islamiyya domin karanta addinin musulunci.

3- Mai martaba Sarkin Dukku HRH Alh. Haruna Rashid || CON ya bayyana dacewar jama'ar Dukku suyi ma Allah godiya bisa samun Wazirin Dukku a matsayin Shugaban karamar hukumar Dukku, bisa nasarorin da Dukku take cimmawa a zamanin shugabancin sa.

4- Dan majalisar Dottijan tarayyar Najeriya Sen. Ibrahim Hassan Dankwambo OON (Talban Gombe) ya bada gudummawar naira Dubu Dari Biyar (500,000) domin jinyar Hon. Bello Yauta (Oga Bello)

5- Wakilin Dukku/Nafada a majalisar tarayyar Najeriya Hon. Abdullahi El-Rasheed ya dauki 'yan Dukku 20. Domin taimaka musu wajen fara karatun zangon 2025/2026 a makarantar Legal Islamic Studies Nafada.

6- Shugaban karamar hukumar Dukku Hon. Adamu Mohammed Waziri (Wazirin Dukku) ya bude kofar hadin kan manyan Dukku ba tare da nuna wariya, ko bambamcin siyasa ba.

7- Shugaban karamar hukumar Dukku Hon. Adamu Mohammed Waziri (Wazirin Dukku) ya bayyana salon kyautata ma jama'a, da zaman sa a cikin al'ummar Dukku a matsayin makamin da yayi amfani da shi wajen rage tasirin jam'iyyun adawa a Dukku ba karfin mulki ba.

8- Shugaban karamar hukumar Dukku Hon. Adamu Mohammed Waziri (Wazirin Dukku) ya ziyarci Asibitin Savana Clinic Gombe, domin dubiya ga Hon. Bello Yauta (Oga Bello) da sauran 'yan Dukku da suke jinya a gurin.

9- Shugabar sashin kula da lafiya ta karamar hukumar Dukku Haj. Fatima Abdulkadir Rashid (FHC Coordinator) ta bayyana cewa: "A shekarar data gabata 2024 ba'a samu bullar cutar Shan Inna (Polio) a kasar Dukku ba, bisa hadin kan da iyayen yara, sarakuna, da karamar hukuma s**a bayar wajen karbar alluren rigakafin Polio"

10- Dan takarar kujerar gwamnan jihar Gombe a shekarar 2023 karkashin inuwar jam'yyar PDP Alh. Jibril Barde (Barden Gombe) ya ziyarci Dukku domin ma Hon. Bello Yauta (Oga Bello) gaisuwar sannu da jiki.

11- Jama'a na ganin sanyan taimakon 500k ga Oga Bello a media, da wallafa labarin biya ma Haj. Larai Sambo bashi a social media bai dace ba! Bisa la'akari da girma, tare da gudummawar da s**a baima jam'yyar PDP a Dukku.

12- A musabakar karatun Al-Qur'ani da aka gabatar a matakin karamar hukumar Dukku, Alar. Muhammad Karamba Ibrahim daga Darul Ulum ya zo na farko a Izu 60 tare da Tafsiri. Yayin da Alar. Maryam Umar Faruk daga JIBWIS fiy Tahfizil Qur'an ta zama ta farko a Izu 60 na tilawar Al-Qur'ani mai girma.

13- Komitin musabakar karatun Al-Qur'ani mai girma ta yabi kokarin Mai martaba Sarkin Dukku bisa tsayuwarsa wajen ganin musabakar ta gudana. Sannan ta yi godiya ga Wazirin Dukku bisa daukar nauyin musabaka.

14- Hon. Jamilu Ahmed Shabewa (Wazirin Shabewa) ya yi kira ga Malamai, da Daliban da s**a yi nasarar lashe musabakar Al-Qur'ani a matakin karamar hukumar Dukku dasu kara himma da kwazo domin samun damar lashe musabaka a matakin jihar Gombe.

15- An yabi kokarin Hon. Abdullahi El-Rasheed bisa ziyarar biko daya kaima Alh. Zubairu Goje Shabewa. Sannan an bayyana dacewar ya yi hakuri ya dawo da albashin babban Ko'odineton sa Alh. Sani Barwa.

16- Anyi addu'ar sakayyar alkairi ga Alh. Maikudi Bobo bisa saya ma wani matashi sabuwar waya albarkacin mai gidan sa Hon. Bala Kelly.

17- An yabi al'ummar Dukku bisa nuna tarbiyya, ladabi, da bin tsari wajen karbar Lemi Solar na tsawon makonni 2 a kofar Mai martaba Sarkin Dukku, da garin Shabewa.

18- Jami'an tsaro sun yi nasarar chabke matasa uku (3) bisa zargin fashin da makami. Bayan sun tare wani attajiri Dan jihar Adamawa sun kwace guzurin sa, tare da raunata shi a hanyar sa ta zuwa garin Jonde.

19- Masu kwacen waya sun raunata wani Basullube bayan sallar Isha'i a farfajiyar Makarantar Markaz a cikin garin Dukku, tare da kwace masa waya.

20- Sunayen 'Yan Dukku 3 sun bayyana a cikin sunayen 642, wadan da s**a samu gurbin karatu (admission) a makarantar Federal Polytechnic Kaltungo a matakin farko sabbin Daliban (First Batch) data dauka a zangon 2025/2026.

21- Kungiyar Dalibai na kasa reshen Dukku (N**S) ta ziyarci Baturen Ilimi na karamar hukumar Dukku Alh. Umar Mohammed Hashidu, domin tattauna muhimman batutuwa da s**a shafi kokarin dawo da yara kan turbar Karatu.

Rahoto
Umar Babagoro Dukku
Shetiman Nakuja
Umar Mohammed Dukku
Umar Bappah Dukku

20/10/2025

DUKKU TV

Shirin labarun karshen mako a Dukku TV

18/10/2025LABARUN KARSHEN MAKO A DUKKU, GOMBEA cikin takaitattun labarun mu na karshen wannan mako, za ku ji cewa:1- Ma'...
18/10/2025

18/10/2025
LABARUN KARSHEN MAKO A DUKKU, GOMBE

A cikin takaitattun labarun mu na karshen wannan mako, za ku ji cewa:

1- Ma'aikatar samar da Ruwa da tsabtace muhalli na tarayyar Najeriya (Federal Ministry of Water Resources and Sanitation) ta zabi Dukku a cikin kananan hukumomi 4 a tarayyar Najeriya. Wanda gwamnatin tarayya zata gudanar da aiki na musamman akan tsabtar muhalli.

2- Mai martaba Sarkin Dukku HRH Alh. Haruna Rashid || CON ya yi kukan yawan mutanen Dukku sun fi karfin ruwan Buster! Sannan bai k**ata a wannan karnin ace 'yan Dukku suna Shan ruwan tafki tare da dabbobi ba!

3- Mai martaba Sarkin Dukku HRH Alh. Haruna Rashid || CON ya yabi kokarin Hon. Bala Kelly bisa ci gaban daya kawo na babbar makaranta, da filin wasanni. Sannan ya bukaci al'ummar Dukku su tsaya da addu'a wajen ganin sun tabbata.

4- Mai martaba Sarkin Dukku HRH Alh. Haruna Rashid || CON ya mika bukatar hukumar samar da ruwan sha na tarayyar Najeriya (Ministry of Water Resources and Sanitation) ta samar da ruwan Sha a Dukku.

5- Mai martaba Sarkin Dukku HRH Alh. Haruna Rashid || CON ya yi kira ga Wakilin Dukku/Nafada a majalisar tarayyar Najeriya Hon. Abdullahi El-Rasheed daya dauki kukan al'ummar Dukku na neman a gyara hanyar Dukku/Gombe/Darazo zuwa gwamnatin tarayya, da sauran guraren da s**a dace a kai kuka.

6- Wakilin Dukku/Nafada a majalisar tarayyar Najeriya Hon. Abdullahi El-Rasheed ya bayyana rashin zuwan (Supervisors) masu duba yanayin muhallin wucin gadi (Temporary side) daga Federal Ministry of Education a matsayin abunda ya hana bude makarantar FCE (S) Dukku.

7- Wakilin Dukku/Nafada a majalisar tarayyar Najeriya Hon. Abdullahi El-Rasheed ya bayyana cewa lalacewar Rijiyar Burtsatse mai aiki da hasken Rana (Solar Borehole) dake cikin garejin Dukku karamar matsala ce, kuma zai gyara kayan sa nan bada jimawa ba.

8- Shugaban karamar hukumar Dukku Hon. Adamu Mohammed Waziri (Wazirin Dukku) ya fara gyaran makarantar sakandaren jeka ka dawo (GDJSS) dake Jarkum.

9- Shugaban karamar hukumar Dukku Hon. Adamu Mohammed Waziri (Wazirin Dukku) ya bada gudummawar #200,000 domin fara jinyar Matar Mal. Abdu Direba Shabewa.

10- 'Yan uwa da abokan Saminu Muhammad (Mejo) sunyi kukan zuci bisa yadda Mejo ya kasa samun kulawa a raunin daya samu a tawagar Hon. Abdullahi El-Rasheed. Sannan sunyi godiya ga Comr Lamido Mohammed Kombi (Mai Nasaran Dukku) bisa daukar nauyin jinyar Mejo bayan raunin ya fara tsami bisa rashin samu kulawar.

11- Kungiyar 'yan kasuwa na jihar Gombe, Gombe Traders Association ta amince da nada mai martaba Sarkin Dukku HRH Alh. Haruna Rashid || CON a matsayin uban kungiya. Bisa kwarewarsa a fannin sanin tattalin arziki.

12- Alh. Damana Abubakar (Hakimin Jamari) ya amince da nada Mal. Bashar Al-Hassan Musa a matsayin sabon sarkin garin Dugo, bayan rasuwar mahaifin su.

13- Mai unguwar Dugge Mal. Muhammadu Gambo Magaji (Yeriman Magajin garin Dukku) ya amince da nada Alh. Ibrahim Usman (Galadiman Dugge) a matsayin Wakilin Dugge, bayan rasuwar Mal. Ahmed Abdullahi (Guru Nagas)

14- Hatsarin Mota ya ritsa da mutum 'yan Dukku 3 a hanyar su ta zuwa Kano, biyu (2) sun rasu! Daya (1) ya samu Karaya a Cinya da wasu kananan raunuka.

15- An bayyana dacewar samar da komitin kula da sololin da aka kafa a manyan titunan cikin garin Dukku, domin gaggauta gyara duk wanda ya lalace ba tare da samun jinkiri ba.

16- Rayuwar wasu 'yan sintirin tabbatar da zaman lafiya a unguwannin cikin garin Dukku ta shiga hatsari. Bisa ganin Kotu ta saki matashin da s**a k**a, bayan dawowar sa daga gudun hijira na sama da sheka uku, bisa mummunan laifin da ake zargin shi ya jagoranci aikatawa.

17- An yabi kokarin Dr. Umar Hassan (Jajin Dukku) wajen samawa Mal. Adamu Umar (Info) aiki a babban Kotun daukaka kara na kasa dake Abuja (Federal High Court of Apple, Abuja) tare sama masa masauki kusa da gurin aikin sa, domin saukake masa Sifiri a birnin tarayya Abuja.

18- Alh. Sani Abdullahi Sambo (Majen Dukku) ya sama wa Rt. Lieut. Aliko El-Rasheed (Dan Amanan Dukku) aiki a National Forest Security Services a matsayin Head of Counter Terrorism and Tacnical Operations Unit.

19- 'Yan uwa da abokan arziki sun yi godiya ga Alh. Sani Abdullahi Sambo (Majen Dukku) bisa samawa Mal. Ashiru Sa'idu Liman aiki a Nigeria Hydrological Services Agency

20- Alh. Sani Abdullahi Sambo (Majen Dukku) ya shawarci Mal. Ashiru Liman daya maida hankali wajen korewa akan koyan aiki, tare da daukar matasan Dukku aiki idan ya samu damar dauka, ba tare da sanya bam-bamci ko wariya ba.

21- Jam'yyar APC ta gudanar da taron kara ma juna sani ga shugabannin jam'iyya na gundumomin kasar Dukku, domin fara aikin yanka ma al'umma katin jam'iyya.

22- Shugaban Dottijan jam'yyar PDP na karamar hukumar Dukku Alh. Bawa Mohammed (Sarkin Bai Dukku) ya jagoranci zama na musamman da Dottijan jam'yyar. Domin tattauna muhimman batutuwan da s**a shafi ci gaban PDP a Dukku.

23- Budeddiyar wasikar Comr Sulaiman Sa'idu Liman ga Hon. Bala Kelly ya dauki hankulan al'umma a kafafen sada zumunta, tare ta tafka muhawara akan yanayin siyasar Hon. Kelly.

24- Jama'a na ci gaba da bayyana takaici bisa rufe Bankin Micro Finance a Dukku! Bisa dalilin karancin masu hada-hada a Bankin. Lamarin daya jawo 'yan Dukku masu Asusun ajiya a Bankin zasu daura niyyar fara zirga-zirga zuwa Bajoga idan bukatar shiga cikin Bank ya taso.

25- Hukumar tsara jarrabawar kammala sakandare na bangaren NABTEC ta daura niyyar rufe Cibiyar ta (center) dake Dukku. Bisa samu gibin Dalibai 10 da zasu biya kudin rijista domin rubuta jarrabawa a November/December 2025.

26- Cibiyar Sabuwar fasahar ci gaban kirkira (Technology for social change and development initiatives) dake Lagos ta karrama shugaban kungiyar Dukku Facebook Connect Mal. Adamu Mohammed Yerima da lambar yabo. Bisa gudumawa daya bayar wajen horar da al'umma akan Basic Digital Literacy Training.

Rahoto
Umar Babagoro Dukku
Shetiman Nakuja
Abubakar M Kawu
Ibrahim Jijo Jamari
Jibril Mohammed Madaki

Bibiya da gyara tuntuben alkalami
Comr Huzaifa Ayuba

13/10/2025

DUKKU TV

Shirin mu na farko a bangaren Labaru. Insha Allahu sauran shirye-shirye daban-daban zasu fara zuwa muku a wannan gidan TV nan bada dadewa ba.

11/10/2025LABARUN KARSHEN MAKO A DUKKU, GOMBEA cikin takaitattun labarun mu na karshen wannan mako, za ku ji cewa:1- Mai...
11/10/2025

11/10/2025
LABARUN KARSHEN MAKO A DUKKU, GOMBE

A cikin takaitattun labarun mu na karshen wannan mako, za ku ji cewa:

1- Mai martaba Sarkin Dukku HRH Alh. Haruna Rashid || CON ya bayyana takaicinsa bisa munin komabayan Ilimi a gundumomin Jamari, da Wuro Tale.

2- Mai martaba Sarkin Dukku HRH Alh. Haruna Rashid || CON ya yi kira ga duk wani Digaci, ko Jauron da bazai iya farfado da makarantar garin sa ba ya gaggauta ajiye rawanin sa.

3- Wakilin Dukku/Nafada a majalisar tarayyar Najeriya Hon. Abdullahi El-Rasheed ya kara kafa sololi a wasu muhimman hanyoyi, da gurare a cikin garin Dukku. Domin kawata gari, da inganta harkokin tsaro.

4- Shugaban karamar hukumar Dukku Hon. Adamu Moh'd Waziri (Wazirin Dukku) ya bada cikakken gudummawa domin gyara rumbun wutar Lantarki (Transformer) dake Durmiyel a cikin garin Dukku.

5- Shugaban karamar hukumar Dukku Hon. Adamu Mohammed Waziri (Wazirin Dukku) ya bayyana Dukku a matsayin karamar hukumar data fi yawan masu Digiri a fadin jihar Gombe. Sannan ya koka akan yadda aka samu koma baya a karatun yara a kasar Dukku.

6- Shugaban hukumar kashe Gobara na jihar Gombe DCF Sulaiman Mohammed Sulaiman ya amince da ofishin da Wazirin Dukku ya basu domin Bude ofishi a Dukku. Sai dai DCF Sulaiman ya bukaci wasu kananan gyare-gyare kafin ya bude shi.

7- Jama'a sun yi yabo da godiya ga Sen. Ibrahim Hassan Dankwambo OON (Talban) bisa gudummawar #500,000 daya bayar domin daukar Haj. Larai Sambo zuwa Gombe domin nema mata lafiya.

8- Jama'a na ci gaba da tausayawa ga shugabar Mata na jam'yyar PDP na karamar hukumar Dukku marigayiya Haj. Larai Sambo bisa yadda ake zargin 'yan siyasa sun yi watsi da jinyar ta har jikin ta ya jikkata kafin a dauke ta zuwa neman magani.

9- Al'ummar Gombe Abba sun gano babu Dan gundumar Gombe Abba a cikin sakatariyar karamar hukumar Dukku a duk cikar ma'aikatan karamar hukuma.

10- Ma'aikatan kashe Gobara sun gaggauta zuwa gidan Alh. Bakoji, a lokacin da wuta ta tashi a gidan sa a cikin garin Dukku. Sai dai rashin motar kashe Gobara ya jawo konewar gidan kurmus!

11- Uwar gidan shugaban karamar hukumar Gombe Haj. Aishatu Sani Ahmed ta jagoranci rabiyar gudummawar audugar Mata ga Daliban sakandare na Dukku a madadin uwar gidan mai girma gwamnan jihar Gombe Haj. Asma'u Inuwa Yahaya.

12- Alh. Umar Abdullahi (Kuliyo) ya jagoranci rabiyar gudummawar Dr. Salim Iliyasu Goje (CEO Dan Mama Smart Homes LMD) ga Daliban makarantar Manga Primary School Dukku, wanda ya hada da: kayan makaranta (uniform) littatafai, da alkaluma.

13- An bayyana dacewar gyara Rijiyar Burtsatse mai aiki da hasken Rana (Solar Borehole) dake cikin Asibitin Comprehensive Health Center Dukku, kafin dawowar lokacin wahalar ruwa.

14- Al'ummar Dukku suna ci gaba da kiraye-kirayen neman a gyara hanyar Dukku zuwa Gombe.

15- Komishinan kudi da tattalin arziki na jihar Gombe Mal. Muhammadu Gambo Magaji, da Comr Lamido Mohammed Kombi sun tura wakilci domin gabatar da ta'aziyyar rasuwar Shehu Madaki Malala.

16- A gasar da Hon. Abba Dan Joy ya shirya ma makarantin sakandare a Dukku, domin murna bisa zagayowar ranar samun ‘yancin Najeriya. Fudiyya ta zama ta farko a Essay Writing, Dukku Community ta lashe Debate, yayin da Dukku Central ta samu nasarar zama ta daya a Quiz Competition.

17- Al'ummar Yole sun yi kukan yadda suke fidda kayan noman su a Kwale-kwale su tsallaka ta Sabon garin Yautere a jihar Bauchi, bisa matsalar rashin hanya daga Yole zuwa Wuro Tara.

18- 'Yan sintirin tabbatar da zaman lafiya a cikin garin Dukku sunyi nasarar damke wani gawurtaccen matashi mai tada hankalin al'umma. Bayan ya shafe sama da shekara uku yana gudun hijira bisa ta'addacin da ake zargin ya aikata.

19- Hon. Rilwanu Shehu ya yi zama da masu wallafa Labarun karshen mako a Dukku (Dukku Media Reporters) a madadin shugaban karamar hukumar Dukku. Domin tattauna muhimman batutuwan da s**a shafi harkokin media a kasar Dukku.

Rahoto
Umar Babagoro Dukku

Bibiya da gyara tuntuben alkalami
Comr Huzaifa Ayuba

WAZIRIN DUKKU YA BADA SAKO A GAYA MA 'YAN SOCIAL MEDIA A yau Alhamis 9/10/2025 masu wallafa Labarun karshen mako a Dukku...
09/10/2025

WAZIRIN DUKKU YA BADA SAKO A GAYA MA 'YAN SOCIAL MEDIA

A yau Alhamis 9/10/2025 masu wallafa Labarun karshen mako a Dukku (Dukku Media Reporters) s**a ziyarci shugaban karamar hukumar Dukku. Domin sada zumunci, da neman shawarwari akan labarun karshen mako da suke wallafawa.

A ta bakin Hon. Rilwanu Shehu Wazirin Dukku ya bayyana farin cikin sa bisa ziyarar da aka kawo masa, sannan ya yabi tsarin Dukku Media Reporters wajen dauko membobi daga sassa daban-daban na fadin kasar Dukku ba tare da sanya bangaranci, ko nuna bambamcin siyasa ba.
Wazirin Dukku ya shawarci Reporters dasu zama masu tan-tance labaru kafin wallafawa, sannan su kauce wallafa labarin da zai haifar da rikici, ko husuma a kafafen sada zumunta.

Hon. Rilwanu ya kara da cewa: "Wazirin Dukku ya bada Sako a gaya muku ('yan social media) Dan Allah ku rinka mutunta juna! Ku daina rikici da juna akan 'yan siyasa. Sannan kofar sa a bude take ga 'yan media a duk lokacin da s**a bukaci shawarin sa, ko gudummawa domin ganin aikin su ya inganta.

Umar Yahya Jatau (Babagoro)
Hadimin shugaban karamar hukumar Dukku a bangaren sadarwa

GIBI MAI WUYAR CIKEWA!1- Tare da shi muka tsara ID Card na DUKKU MEDIA REPORTERS2- Ya kammala kokarin yadda zamu yi link...
08/10/2025

GIBI MAI WUYAR CIKEWA!

1- Tare da shi muka tsara ID Card na DUKKU MEDIA REPORTERS
2- Ya kammala kokarin yadda zamu yi linking da wasu manyan ma'aikan GMC TV
3- Ya fara (Assignment) na yin nazarin yadda zamu fara samu labaru a gundumar Zaune! Sai Rai yayi halin sa!
Gashi zamu raba ID Cards ba tare da shi ba!

CIGIYA: Ana Neman Aishatu MufidaAn nemi wata yarinya mai suna Aishatu Mufida, ’yar shekara 13, ’yar Malam Yahaya Jibrin....
06/10/2025

CIGIYA: Ana Neman Aishatu Mufida

An nemi wata yarinya mai suna Aishatu Mufida, ’yar shekara 13, ’yar Malam Yahaya Jibrin. Gidansu yana unguwar Chiroma (kusa da ƙaramin asibiti) a cikin garin Dukku, Jihar Gombe.

Aishatu Mufida ta ɓar gida tun ranar Talata, 30/9/2025, bayan sallar Azahar. Har zuwa yanzu ba a san inda take ba. An bincika wajen makwabta da sauran wuraren da ake zaton za a same ta, amma ba a same ta ba.

Idan Allah Ya nufa wani ya ganta, ana roƙon shi da ya taimaka ya dawo da ita gida, ko ya kai ta gidan Mai unguwa ko Hakimi, ko kuma ya kira mahaifinta a waɗannan lambobin:

📞 0802 110 2983
📞 0806 469 4283

Allah Ya sa a same ta lafiya.

4/8/2025LABARUN KARSHEN MAKO A DUKKU, GOMBEMuna cikin jimamin rasuwar daya daga cikin Wakilan mu na gundumar Malala, Mal...
04/10/2025

4/8/2025
LABARUN KARSHEN MAKO A DUKKU, GOMBE

Muna cikin jimamin rasuwar daya daga cikin Wakilan mu na gundumar Malala, Mal. Shehu madaki Malala. Dan haka wannan mako bazamu samu damar kawo muku labarun karshen mako ba!
Da fatan Allah ya jikan Mal. Shehu ya gafarta masa.

*Sa hannu*
Umar Yahya Jatau
A madadin Dukku Media Reporters

DUKKU MEDIA REPORTERS TA YI BABBAN RASHIMuna yi ma juna jaje, da ta'aziyyar rasuwar abokin aikin mu (Wakilin mu na Malal...
02/10/2025

DUKKU MEDIA REPORTERS TA YI BABBAN RASHI

Muna yi ma juna jaje, da ta'aziyyar rasuwar abokin aikin mu (Wakilin mu na Malala) Mal. Shehu madaki Malala
Da fatan Allah ya jikan shi ya gafarta masa

27/9/2025LABARUN KARSHEN MAKO A DUKKU, GOMBEA cikin takaitattun labarun mu na karshen wannan mako, za ku ji cewa:1- Shug...
28/09/2025

27/9/2025
LABARUN KARSHEN MAKO A DUKKU, GOMBE

A cikin takaitattun labarun mu na karshen wannan mako, za ku ji cewa:

1- Shugaban kasar Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya amince da daukaka darajar Dr. Bello Maigari CON (Tafidan Dukku) daga mukamin Tinibu Connect Northern Coordinator, zuwa DG National Coordinator Nationwide Tinubu Connect Association.

2- Mai girma gwamnan jihar Gombe Alh. Muhammadu Inuwa Yahaya CON (Dan Majen Gombe) ya kafa komitin zagayen duba ingancin gyaran Asibitocin daya gyara a kasar Dukku, tare da duba bukatun su.

3- Ministan Sifirin tarayyar Najeriya Sen. Sa'idu Ahmed Alkali ya ziyarci Ministan Ayyukan tarayyar Najeriya Engr. David Umahi domin mika kukan munin lalacewar hanyar Dukku zuwa Gombe. Tare da neman alfarmar a gyara ta akan lokaci.

4- Mai martaba Sarkin Dukku HRH Alh. Haruna Rashid || CON ya yi kukan zuci bisa samun labarin Nafada, da Funakaye sun kusan cimma Dukku a yawan adadin wadan da s**a mallaki katin zabe.

5- Mai martaba Sarkin Dukku HRH Alh. Haruna Rashid || CON ya yi zagayen rangadi a kasar Dukku, domin wayar da kan al'ummar karka bisa muhimmancin sanya yara a makaranta, da yankan katin zabe.

6- Mai martaba Sarkin Dukku HRH Alh. Haruna Rashid || CON ya umurci Hakimai su kawo masa bayanin adadin yaran da s**a shiga Primary 1 a wannan shekara a gundumomin su.

7- Mai martaba Sarkin Dukku HRH Alh. Haruna Rashid || CON ya yi kira ga Hakimai dasu kafa komitocin sintirin kula da zaman lafiya a kowace gunduma. Sannan jama'a su tsaya addu'o'in rokon zaman lafiya, da tsaro a gurin Allah madaukakin Sarki.

8- Shugaban karamar hukumar Dukku Hon. Adamu Moh'd Waziri (Wazirin Dukku) ya tausaya ma al'ummar unguwannin Balu, Gona, Bakari, da sauran masu amfani da Transformer na Durmiyel bisa shafe tsawon lokaci basu da Lantarki. Sannan ya turo kwararru su duba matsalar.

9- Shugaban karamar hukumar Dukku Hon. Adamu Moh'd Waziri (Wazirin Dukku) ya yi kukan matsalar hana karin jini a kananan Asibitoci. Sannan ya mika bukatar hukumar lafiya ta jihar Gombe ta daukaka darajar wasu Asibitoci a kasar Dukku, domin su fara karin jini.

10- Hukumar zabe (INEC) na karamar hukumar Dukku ta yabi kokarin Wazirin Dukku bisa saya ma 'yan social media sabbin Woyoyi domin gudanar da aikin rijistan katin zabe.

11- Hakimin Bozomshulwa Alh. Kamalu Hayatu Gurama ya bukaci izinin Mai martaba sarkin Dukku. Domin ya fara kai karar iyayen da s**a ki saka 'ya'yan su a makaranta a Kotu a kasar Bozomshulwa.

12- Gundumar Hashidu ta ciri Tuta a cikin gundumomin kasar Dukku (Banda cikin garin Dukku) a bangaren samar da ingantattun makarantun Firamare, sakandare, da yawan yara masu zuwa makaranta.

13- Gundumar Zaune ta zama abun koyi a tsakanin gundumomin kasar Dukku wajen yin Tururuwa zuwa ofishin hukumar zabe (INEC) na Dukku, domin yankar katin zabe.

14- Komitin sintirin gadin unguwanni ta mika bukatar jami'an tsaro su rinka ajiye baraye amfanin Gona har zuwa karshen kammala dawo da amfanin Gona gida.

15- Anyi kira ga al'umma dasu kaushe zubda shara a cikin lambatu, domin gudun toshewar su, da jawo ambaliyar ruwan sama.

16- Zirga-zirgar matafiya ya samu tsaiko a hanyar Jarkum zuwa garin Wawa, a dai-dai lokacin da aka samu labarin bayyanar Barayi masu Pashi da makami a tsakanin Galumji, da Wawa.

17- Kungiyar ci gaban gundumomi (WDC) ta bayyana dacewa, tare da bukatar karamar hukumar Dukku ta gyara Rijiyar Burtsatse Mai aiki da hasken Rana (Solar Borehole) dake unguwar Madaki a cikin garin Malala.

18- Hon. Aishatu Jibir Dukku (Gimbiyar Dukku) ta yi zaman sirri da wasu fitattun 'yan kasuwa na Dukku, wadan da s**a hada da: Alh. Zubairu Goje Shabewa, da Mal. Sunusi Lamuwa (Kawun Didi)

18- Masu hasashe sun fara hango kujerar Dukku/Nafada zata fi karfin 'yan Dukku, bisa yadda 'yan Nafada suke tururuwar yankan katin zabe, kuma karfin kuri'un su alkibla ce guda daya.

19- Masu zuwa cin kasuwar garin Kamaba a kasar Jamari sun koka rashin rumfunan kasuwa a Kamba, wanda hakan yake jawo manyan matsaloli, musamman lokacin da ake zabga ruwan sama.

Rahoto
Umar Babagoro Dukku
Shehu madaki Malala
Jamilu Jamsy Bozomshulwa
Jibril Muhammad Madaki

Address

Dukku
760401

Telephone

+2348133865636

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Labarun Kasar Dukku posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share