19/05/2026
Sadiya Umar Farouq na fama da rashin lafiya a ƙasar Egypt - Lauya
Tsohuwar ministar harkokin jin kai, Sadiya Umar Farouq, ta kasa gurfana a gaban kotu saboda rashin lafiya, k**ar yadda lauyanta Oladipo Okpesheyi ya bayyana.
Jaridar TheCable ta rawaito cewa, lauyan ya shaida wa babbar kotun babban birnin tarayya da ke Apo cewa Farouq tana kasar Egypt domin jinya, kuma likitoci sun tabbatar da cewa ba za ta iya bayyana a kotu ba sai bayan kusan watanni biyu.
Hukumar EFCC tana tuhumar Farouq tare da Bashir Nura Alkali da wani Sani Mohammed kan laifuka 21 da s**a hada da cin amanar aiki da karkatar da kudade. Hukumar ta zarge su da handame kusan dala miliyan 1.3 da kuma naira miliyan 746.6.
A zaman kotun na ranar Litinin, lauyan EFCC, Rotimi Jacobs (SAN), ya bukaci kotu ta ci gaba da aiki da sammacin k**a Farouq saboda rashin bayyana a kotu. Alkalin kotun, Jude Onwuegbuzie, ya nuna rashin jin dadinsa kan jinkirin shari’ar tare da gargadin cewa za a dauki karin mataki idan ba ta gurfana a zama na gaba ba.
Kotun ta dage sauraron karar zuwa ranar 8 ga Yunin 2026 domin fara karanta tuhume-tuhumen.