Online radio zamani fm dutse

Online radio zamani fm dutse Labaran duniya

Dangote Refinery Reduces Petrol Price to N970 Per LitreDangote Petroleum Refinery has reduced the price of Petrol from N...
24/11/2024

Dangote Refinery Reduces Petrol Price to N970 Per Litre

Dangote Petroleum Refinery has reduced the price of Petrol
from N990/litre to N970/litre for the marketers.

A Statement Signed by Anthony Chiejina Group Chief Branding and Communications Officer says the gesture is the Company’s way of appreciating the good people of Nigeria for their unwavering support in making the Refinery a dream come true.

The Statement notes it is also to thank government for their support and complement the measures put in place to encourage domestic enterprise for the Nations collective well-being.

It promised the refinery would not compromise on the quality of its petroleum products and assured Nigerians of the best quality products that are environmentally friendly and sustainable.

07/02/2024

I LOVE YOU DIN BANZA.

Wata rana wani malami yana zaune da jama'a ana ta hira, sai ya tambayesu "anya kuwa suna son matayensu?" gaba daya s**a amsa da "kwarai kuwa". Sai malam ya sake cewa "Yaushe rabon da kowannenku ya furtawa matarsa cewa yana sonta? Misali ya ce "I love U". To, anan ne s**a fara bada amsa, wani ya ce kusan wata daya kenan, wani ya ce fiye da shekara, wani ya ce ba zai iya tunawa ba, da sauransu. Daga nan malam ya ce kowa ya rubuta sakon ta wayar salula ya aikawa matarsa, domin ganin wadanne irin amsoshi zasu bayar. Cikin kankanin lokaci sai ga amsoshi sun fara zuwa daga wajen matayen k**ar haka:

1. Mhmm da kenan banda yanzu.....

2. Maganar auren naka ta rushe kenan?

3. Kana son na baka aron kudi kenan?

4. A mafarki kenan

5. Tab Allah ya k**aka, bari ka dawo ka fadamin wadda kaje aik**a wannan sako

6. Hmmm me kake nufi? Wannan karon ba zan yarda ba.

7. Waye wannan?

8. Wata sabuwa

9. Yau kuma?

10. Hmm munafiki wallahi ban hakura da abin da kamin ba....

11. I love u din banza.....

12. Nafada maka, ka daina shaye shaye......😄😃😃
Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un.... Yaku
jama'a kunsan waye masoyinku na gaskiya
kuwa??? To shine Manzon Allah saw, lokacin da
mala'ikan mutuwa yaxo domin karbar ransa sai
yaji zafi kwarai ya tambayi mala'ikan mutuwa
yace dama haka akejin zafi yayin mutuwa? Sai
yace masa haba ai kai nan an saukaka maka ne
matuka amma sauran mutane ai zafin yawuce
haka nesa ba kusa ba, Allahu akbar jama'a
kunsa me manxon Allah saw yace? To cewa yayi
yana neman alfarma cewar a hada masa
dukkan wani zafi da ukuba da ake yiwa Al
ummarsa yayin mutuwa shi ayi masa baki daya,
ya daukemana.... Allahu akbar jama'a wannan
bawan Allah yana yi mmana sonda ko
mahaifanmu basa yimana, ya Allah ka kara
tsira da Aminci ga shugabanmu Annabi
Muhammadu saw...
Allah ka yafe mana
dukkan laifukansa, ya Allah ka biya masa
dukkan bukatunsa na duniya

Nan bada Jimawa ba Za'a Kawo karshen Wahalhalun da Yan Najeriya ke Fuskanta -Cewar Remi Matar TinubuUwargidan Shugaban ƙ...
06/02/2024

Nan bada Jimawa ba Za'a Kawo karshen Wahalhalun da Yan Najeriya ke Fuskanta

-Cewar Remi Matar Tinubu

Uwargidan Shugaban ƙasa, Sen. Oluremi Tinubu ta bayar da tabbacin cewa nan ba da jimawa ba za a kawo karshen wahalhalun da ‘yan Najeriya ke fuskanta tare da ingantattun manufofin Gwamnatin tarayya.

Uwargidan Shugaban ƙasar ta bayar da wannan tabbacin ne a Yau Litinin a gidan Gwamnatin tarayya. Yayin wata ganawa da matan gwamnonin kan aikin Gidauniyar ta, Renewed Hope Initiative (RHI).

Ta bada tabbacin cewa shekarar 2024 na cike da "zaman lafiya, ci gaba, wadata da kuma manyan nasarori" don amfanin 'yan Najeriya baki daya.

Remi Tinubu ta yabawa matan gwamnonin bisa kokarinsu da goyon bayansu a shekarar 2023, inda ta bukace su da kada su yi kasa a gwiwa wajen magance bukatun marasa galihu a jihohinsu.

Lokaci irin wannan yana buƙatar tunani mai zurfi, don haka, dole ne dukkan hannaye su kasance a kan bene. Bugu da ƙari, yanayin wahala na ɗan lokaci ne, ba da daɗewa ba zai shuɗe.

"Ofishina ne ke tafiyar da manufar RHI don cika ajandar sabunta bege na Gwamnatin shugaba Tinubu," in ji ta.

Ta ce shirin tallafa wa aikin gona na mata (WASP), a karkashin RHI, zai baiwa manoma 20 duk wani, daga jihohi biyar na shiyyar Kudu maso Gabas.

“Wadannan manoma za su samu N500,000 kowanne sannan kuma za a ba da jimillar N10m ga ko’odinetocin jihohin RHI biyar

“Hukumar bunkasa filayen noma ta kasa tare da hadin gwiwar RHI za su tallafa wa karin mata manoma 80 daga kowace jiha tare da samar da horo da karfafawa da kuma kayan aikin noma.

"Zamu sayi duk amfanin gonaki bayan girbi wa," inji ta.

12/06/2023

Lalataccen Kiristan Kudu Ya Fi Musulmin Kwarai Dan Arewa Chanchantar Ya Zama Shugabancin Majalisar Dattawan Najeriya, Inji Kashim Shettima Daga Comr Abba Sani Pantami Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima, ya ce ba daidai ba ne musulmin Arewa ya zama shugaban majalisar Dattawa ba. A yayin wani z...

10/06/2023

LABARI: Mamallakin kungiyar Man City Sheikh Mansour yana Istanbul don kallon wasan karshe na gasar zakarun Turai

Rabonsa da halartar kallon wasan Manchester City tun shekarar 2010.

Daga: [Fagen Wasanni]

22/05/2023

Yau Za a Kaddamar Da Matatar Mai Ta Dangote

In an jima kadan ne ake sa ran Shugaba Buhari zai kaddamar da matatar mai ta Dangote, wadda ita ce mafi girma a nahiyar Afirka.

Ana sa ran matatar, mai karfin samar da ganga 650,000 na tataccen mai a kullum za ta biya wa Najeriya bukatunta na man fetur da sauran dangoginsa 100 bisa 100.

Akwai kuma hasashen ‘yan kasar nan za su samu sauki daga abubuwan da matatar za ta rika samarwa irin su kananzir da man dizel da man jirgin sama da man fetur da dai sauransu.

Haka kuma ana hasashen za ta samar da Dala biliyan 21 — kimanin Naira tiriliyan 9.7 — a shekara, a bangaren danyen mai, duk da cewa sai nan gaba a cikin wannan shekara matatar za ta fara aiki.

Rahoton cibiyar S&P Global Commodity Insights mai nazari kan cinikayya ya nuna a cikin watan Yuni mai k**awa Matatar Mai ta Dangote za ta fara samar da tataccen mai.

‘Yan Najeriya na murnar ganin fara ikin matatar wadda kamfanin mai na kasa (NNPCL) ke da kashi 20 cikin 100 na hannun jari.

Masu ruwa da tsaki a bangaren mai na ganin matatar za ta sauya matsayin Najeriya daga mai shigo tataccen mai, zuwa mai fitarwa kasashen waje.

Wannan kuwa na zuwa ne a daidai lokacin da gwamnatin kasar ke shirin soke tsarin biyan tallafin mai wanda kudin da take kashewa a kai y karu daga biliyan N351 a 2005 zuwa tiriliyan N4.39 a 2022, kafin ya karu zuwa tiriliyan N3.6 a watanni shida na farkon 2023.

Duk da cewa babu tabbacin fara aikin matatar zai rage tsadar mai a kasar, zai rage kudin da ake kashewa wajen jigilar man a irin asarar da ake yi.

Wasu masana na ganin za a saumu saukin farashin mai idan har gwamnatin Najeriya za ta ba wa matatar danyan mai a farashi mai sauki; sai dai kuma kamfanin mai bukaci haka ba tukuna.

Wasu masanan kuma na ganin fara aikin matatar zai bude wani sabon babi a kan batun tallafin da gwamnati ke neman cirewa.

Shugaban kungiyar ma’aikatan man fetur da iskar gas (PENGASSAN), Kwamred Festus Osifo, ya ce fara aikin matatar zai rage kudaden da ake kashewa wa

22/05/2023

Ba Zan Daina Rusau Da Korar Ma’aikata Ba, Har Sai Na Bar Mulki —El-Rufai

Gwamnan Kaduna mai barin gado, Nasir El-Rufai, ya ce ba zai daina da korar bara-gurbin ma’aikata da rusa haramtattun gine-gine ba, har sai ya bar mulkin jihar.

El-Rufai ya yi wannan faruci ne washegarin da ya kwace izinin mallaka tare da sanya alamar rusa wasu kadarori tara mallakin tsohon gwamnan jihar, Sanata Ahmed Mohammed Makarfi.

Da yake bayani a taron kaddamar da littafin da wani dan jarida, Emmanuel Ado, ya rubuta a kan ayyukansa, mai suna “Putting The People First”, ya ce, “Har zuwa ranar karshen mulkina, ba zan daina kawar da bara gurbin mutane da sauran miyagun abubuwa ba.”

A cewarsa, “Duk abin da na ga bai dace ba, zan kawar da shi, saboda kada su zama matsala ga sabon gwamnan da zai karbi mulki.”

A lokacin taron, Gwamnan Jihar Ribas, Nyesom Wike, ya bayyana El-Rufai a matsayin mutum mara tsoro, wanda samun mai tsage wa gwamnati gaskiya k**arsa, ke da wuya.

A cewar Wike, “Samun shugaba irin El-Rufai sai an tona, wajen hazaka da jarumta domin tabbatar da adalci ga kowa.

“Shi ba dan amshin shata ba; Ba zan manta wasikarsa ga Shugaba Buhari a watan Maris na 2017 ba, wanda ya tayar da kura, inda ya ja hankalin shugaban kasa kan muhimmancin cika alkawuran da ya yi wa jama’a saboda kada ya bar mummunan tarihi.

“Da wuya a samu gwamnan da zai iya yin haka ga shugaban dan jam’iyyarsa, in ba jarumi wanda ba dan kanzagi ba.”

A wurin taron, Wike ya ba da gudummawar Naira miliyan 20, haka ma shugaban kasa mai jiran gado, Bola Ahmed Tinubu, wanda tsohon Shugaban Asusun Kula da Manyan Makarantu ta Kasa (TETFUND), Kashim Imam, ya wakilta.

16/05/2023

Ƙungiyar Likitocin Najeriya Za Ta Shiga Yajin Aiki


Ƙungiyar Likitoci Masu Neman Ƙwarewa ta Najeriya ta ayyana shiga yajin aikin gargaɗi na kwana biyar kan gaza biya mata buƙatunta da gwamnatin tarayya ta yi.

Ƙungiyar ta bayyana ɗaukar matakin ne bayan ganawar da shugabanin kwamitin gudanarwarta ya yi ranar Litinin.

Likitocin sun ce za su fara yajin aikin gargaɗin ne daga ranar Laraba 17 ga watan Mayu zuwa ranar Litinin 22 ga wata.

Likitocin na buƙatar gwamnati ta gaggauta yin ƙari a tsarin albashin ɓangaren lafiya da kashi 200 kan albashin likitocin na yanzu.

Sannan a ƙara musu kuɗin alawus da s**a nema cikin wata wasiƙa da shugaban ƙungiyar ya rubuta wa ministan lafiya Dakta Osagie Ehanire ranar 7 ga watan Yulin 2022.

Haka kuma ƙungiyar ta buƙaci a gaggauta biyan su kuɗin horaswa na shekarar 2023, k**ar yadda yake ƙunshe cikin yarjejeniyar da s**a cimma a wata ganawa da masu ruwa da tsaki, da ma'aikatar lafiya ta jagoranta.

Sannan kuma ƙungiyar na buƙatar gwamnatin tarayya da ta fara biyan wasu mambobinta bashin albashin da suke binta a shekarun 2014 da 2015 da kuma 2016.

A ranar 29 ga watan Afrilu ne dai ƙungiyar likitocin ta bai wa gwamnatin tarayya wa'adin mako biyu da ta zartar da yarjejeniyar da s**a cimma ko kuma ta tsunduma yajin aiki.

15/05/2023

BREAKING NEWS
✊✊
MAI MARTABA SARKIN DUTSE ALH. MUHAMMAD HAMIM NUHU SANUSI ya halarci Taron Karramawa da Walimar Yaye Ɗalibai Saba’in da Huɗu (74) da s**a haddace Al_Qur’ani Mai Girma da kuma Ɗalibai Talatin da Bakwai (37) da s**a Sauke Al_Qur’ani Mai Girma cikin Shekara Ɗaya (1) Karkashin Cibiyar SHEIKH JA’AFAR MAHMUD ADAM FOUNDATION dake Rukunin Gidajen Malam Inuwa Dutse dake Ɗanmasara wanda aka gabatar dashi a yau a Malam Aminu Kano Triangle dake Dutse babban Birnin Jihar Jigawa.

Taron ya samu Halartar Uban Taro wato MAI MARTABA SARKIN DUTSE ALH. MUHAMMAD HAMIM NUHU SANUSI, Shugaban Taro Sheikh Dr. ABdullahi Bala Lau Shugaban Kungiyar Izala ta Kasa, Sheikh Dr. Kabiru Haruna Gombe Sakataren Kungiyar Izala ta Kasa, Babban Limamin Masarautar Dutse Dr. ABubakar Sani Birnin Kudu, Mai Masaukin Baki Shugaban Karamar Hukumar Dutse Hon. Bala Usman Chamo da sauran su.

Bayan Kammalawa da Bikin Yaye Daliban ne sai aka dunguma ya zuwa Fadar Mai Martaba Sarki yayin da Shugaban Kungiyar Izalar ta Kasa ya fara da Jawabin Godiya ga Mai Martaba Sarki kana da yi masa kyakkyawan Albishir da bashi Mukamin Grand Patron na kungiyar Agaji ta Izala a kasa baki daya. Yace muna sane da dukkan alkhairan da marigayi Mai Martaba Sarki yake wajen kwaso kananan yara wadanda s**a musulunta domin taimaka musu k**a daga harkar karatunsu da ci da shan su har sai sun girma. Ya kuma jaddada masa da cewa zasu bayar da gudunmawa wajen duba maganar da yayi akan mazauna Yankin Sumaila domin taimakawa wajen ganin an musu Da'awa domin shigowa wannan addinin Allah Madaukakin Sarki.

A nasa jawabin Mai Martaba Sarkin Dutse ya fara da jawabin Maraba sannan ya tunasar musu da yadda gidan nan yake domin daman chan akan harkar hidimtawa Sunnah ta Manzon Allah S.A.W yake bisa shawari da su Malaman Sunnah suke wa Marigayi domin sune fitulun da suke haskaka masa gabansa, ya kuma roki yadda s**a rike Marigayi haka shima su rike shi a wajensu, ya kuma ce In Sha Allahu yadda Marigayi ya rike su h

14/05/2023

Shugaba Buhari Ya Kammala Aikin Wutar Lantarki Ta Zungeru Kamar Yadda Ya Yi Alkawari.

Ministan wutar lantarki Injiniya Abubakar D. Aliyu ya sanar da cewa, an kammala aikin samar da wutar lantarki mai karfin megawatts 700 na Zungeru.

A cewar ministan, tuni kamfanin rarraba wutar lantarkin na Najeriya (TCN) ya shirya ya karbi wutar da aka samar daga cibiyar samar da wutar lantarkin.
Ya kuma ce hakan zai cike gibin da ake samu na bukatun wutar lantarkin kasar.

Injiniya ya fadi haka ne a ranar Asabar, 13 ga watan Mayu a jihar Neja a lokacin da yake bayani bayan ziyarar duba aikin da aka kammala.

A lokacin ziyarar, yana tare da gwamnan jihar Abubakar Sani da kuma wasu manyan jiga-jigan majalisar da ke kula da ayyukan mak**ashi.

Da yake karin haske, ya ce an kammala dukkan gwaje-gwaje na aiki da na’urorin da ake amfani dasu, kuma za a kaddamar da aikin nan ba da jimawa ba a hukumance.

A cewarsa, tun shekarun 1960 rabon da Najeriya ta yi irin wannan aikin, amma sai gashi ya samu a karkashin jagorancin Shugaba Buhari.

Hakazalika, ya ce, gwamnatin Najeriya ta zuba dimbin hannun jari a wannan aikin na Zungeru don ta inganta samun wutar lantarki.

A gefe guda, ya ce irin wadannan ayyuka na daga buri da kudurin Buhari na ciyar da Najeriya gaba a karkashin ikonsa.

Baya ga samar da karin wutar lantarki ga ‘yan Najeriya, aikin a halin yanzu ya samar da ayyukan yi ga ‘yan Najeriya da dama kuma zai samar da hanyoyin magance ambaliyar ruwa, ban ruwa a noman rani, da kuma samar da ruwa wadatacce.

A nasa bangaren, gwamnan jihar Neja, Abubakar Sani Bello, ya yabawa shugaba Buhari kan kammala aikin samar da wutar lantarkin mai karfin megawatt 700 na Zungeru ta jihar Neja.

A tun farko, gwamnatin Najeriya ta bayyana yadda aikin wutar lantarkin ke cin kudi da kuma yadda 'yan Najeriya ke shakku.

13/05/2023

Ayyukan Raya Ƙasa: Najeriya na buƙatar kashe dala biliyan 100 duk shekara – Daraktan Kasafin Kuɗaɗe.

Babban Daraktan Ofishin Tsare-tsaren Kasafin Kuɗaɗe, Ben Akabueze, ya ce aƙalla Najeriya na buƙatar ta riƙa kashe dala biliyan 100 duk shekara, idan ana so a cimma samar da dukkan ayyukan raya ƙasa da ake tsananin buƙata.

Akabueze ya ce tilas an fa an raba ƙafa wajen kashe kuɗaɗen, wato gwamnati da kuma masu kamfanoni da masana’antu na kan su riƙa zuba kuɗaɗe wajen gudanar da ayyukan ci gaban da ƙasar nan.

Ya bayyana haka a ranar Laraba, a wurin taron nuna wa zaɓaɓɓun ‘yan majalisar tarayya sanin mak**ar aikin majalisa.

Ya ce k**a daga Gwamnatin Tarayya da gwamnatin jihohi sun kasa iya kashe dala biliyan 100 wajen bunƙasa ayyukan raya ƙasa a duk shekara.

“Na farko dai kafin a iya saisaita tattalin arzikin Najeriya, mu na buƙatar a riƙa kashe dala biliyan 100, aƙalla duk shekara.

Ya ce kasafin da ake samu daga gwamnatin tarayya a duk shekara bai wuce dala biliyan 30 ba. Jihohi da Babban Birnin Tarayya, FCT ba su ƙara wa kasafin Najeriya wani karsashi ko ƙarfi. Wato idan ma sun kashe dukkan kuɗaɗen da tarayya ke ba su, har yanzu dai ana barin giɓi sosai,” haka Akabueze ya bayyana.

Babban Daraktan na kasafin kuɗaɗe, ya nuna matuƙar damuwa ganin babu wata ƙwaƙƙwarar doka kan kasafin kuɗaɗe.

Sai dai ya ce akwai ƙudiri ajiye a Majalisar Tarayya. Daga nan ya yi kira ga majalisa mai barin gado su ƙoƙarta su saka hannu kan ƙudirin domin ya zama doka.

Address

New Market Street
Dutse
6-6

Telephone

+2349128097919

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Online radio zamani fm dutse posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Online radio zamani fm dutse:

Share

Category