07/06/2025
"Fitilar Gaskiya: Kiran Farkawa Ga Matasa"
“Kowane zamani na da gwagwarmayarsa — tamu ita ce gwagwarmayar ilimi, gaskiya, da sanin yakamata.”
A yau, duniya ta canza. Ba a ƙara yarda da zaman banza ba. Babu lokacin mantuwa da nauyin da ke wuyanka a matsayinka na matashin Arewa. Lokaci ne na tashi daga barcin sakaci da kangin jahilci. Magabatanmu irin su Sir Ahmadu Bello, Malam Aminu Kano, da Sheikh Abubakar Gumi sun kunna fitilar gaskiya, s**a ja mana hanya cikin duhu da tunkude duhun rashin sani.
Ilimi ba kawai karatun lissafi da kimiyya ba ne — ilimi shi ne sanin yakamata, sanin hakkinka da na wasu, sanin me ya kamata ka yi domin gina kanka da al’umma. Akwai nauyi a kan kowane matashi da ya san ya karanta da ya fahimta. Akwai alhaki a kan kowacce budurwa da ta san darajar kanta da addininta.
Matasa su ne ginshikin gobe. Su ne jirgin da za a hau zuwa gaban ci gaba ko halaka. Idan ka zauna, an zauna da Arewa. Idan ka tashi, Arewa ta tashi. Idan ka koyi gaskiya da rikon amana, gobe za ta kasance tamkar rana mai dumi ba baƙin hadari.
Kar ka bari ka zama makaho cikin zamanin wayewa. Kar ka zama abin kallo a lokacin da ake rubuta tarihi. Ka zama mai zana tarihi! Ka zama fitila mai haskaka da ke farfado da zukatan ‘yan uwanka!
’Yan Gaskiya su ne waɗanda s**a san hanya, s**a karanta tarihi, s**a fahimci mafita, s**a ɗauki alhakin farfado da al’umma ba tare da jiran roƙo ba.
Arewa ba za ta sake tashi ba sai matasa sun gane muhimmancinsu, s**a rungumi gaskiya, ilimi, da aiki tukuru.
Mu zama ’Yan Gaskiya. Mu rayu da hikima. Mu haskaka Arewa.
Dan BelloDokin Karfe TVAbba Sani PantamiEveryoneArewa Media