Newsroom Radio Jigawa

Newsroom Radio Jigawa Keeping you updated

08-08-2025                    FULATAHadimin wakilin mazabar Kirikasamma da Guri da kuma Birniwa a majalissar wakilai ta ...
08/08/2025

08-08-2025 FULATA
Hadimin wakilin mazabar Kirikasamma da Guri da kuma Birniwa a majalissar wakilai ta kasa a karamar Hukumar Birniwa , Musa Muhammad Isyaku Birniwa ya ce an kammala aikin sanya fitilin kan t**i masu amfani da hasken rana a garuruwa 13 daga cikin 15 da ake aikin a karamar Hukumar Birniwa
Ya sanar da hakan ne a lokacin ganawa da wakilinmu ta wayar hannu
Mallam Musa Muhammad Isyaku ya ce an kammala aikin ne a garuruwan Burseli da Jirgiwa da Matamu da sabbin unguwannin Birniwa da Maiso da cikin garin Diginsa da Jirgiwa da Matamu da Kibu da Laraba da Tsangaya Yamma
Ya ce aiyukan da s**a rage guda biyu sune na garuruwan Matarar Batu da kuma Kubuna
Hadimin na dan majalissar a karamar Hukumar Birniwa yana mai cewar ana gudanar da aiyukan ne domin kawata gari da kuma inganta al’amurran tsaro
Ya ce aiyukan na daga cikin aiyukan mazabu na dan majalissar tarayya Honourable Abubakar Hassan Fulata.
Musa Muhammad Birniwa ya kuma ce ana gudanar da irin wadannan aiyuka a dukkanin kananan hukumomin uku na mazabarsa
Dan majalissar ya kuma gina sabon masalacin kamsisalawati a garin Masewa dake mazabar Karanka da gina ajujuwan karatu shida a garin Fulatanan domin karantar da yara
Haka kuma dan majalissar ya raba kayayyakinh kimiyya da littattafai na kimiyya ga daliban yankin

08/08/2025

08-08-2025 GICC
Shugaban kungiyar hada kan al’ummar Karamar hukumar Gwaram da kawo cigaba a yankin wato GICC, Injiniya Abubakar Galadima Laya ya shawarci al’ummar yankin, musamman wadanda basu da rijistar zabe su fito domin yin rijistar wadda za a fara a ranar sha takwas ga wannan wata na Ogusta.
Injiniya Abubakar Galadima Laya, yace jami’an kungiyar zasu shiga lungu da sako na Karamar hukumar domin wayar da kan jama’a muhimmancin yin rijistar zaben.
Ya tinatar da al’ummar yankin muhimmancin mallakar katin zabe da katin shedar zama Dankasa da sauran muhimman abubuwa da Gwamnati ke son kowa ya mallaka.
Shugaban kungiyar ta GICC ya kara da cewa kungiyar zata cigaba da fafutukar kawowa yankin abubuwan cigaba daga matakin tarayya zuwa Jiha da Karamar hukuma.
Injiniya Abubakar Galadima Laya, daga nan ya godewa al’ummar yankin, musamman masu ruwa da tsaki bisa hadin kai da goyon baya da suke baiwa kungiyar wajen gudanar da ayyukan-ta.

08/08/2025

8-8-25. HASKE/KAILA
Tsohon Kamsilan mazabar Surko, Malam Nura Surko, ya ce ya amsa gayyatar Hasken Birnin Kudu da Buji Engineer Sulaiman Da'u Aliyu zuwa jam'iyar APC ne domin lokaci ya yi da za su jingine jam'iyar PDP domin neman nakoma a siyasance.
Malam Nura Surko ya yi wannan tsokaci ne a wani taron tattaunawa da wakilan Hasken Birnin Kudu da Buji Engineer Sulaiman Da'u Aliyu a garin Birnin Kudu.
Ya bayyana gamsuwa da salon siyasa na Kai ayyukan alkhairi kusa da jama'a da Engineer Sulaiman Da'u Aliyu ya zo da shi, Inda ya jinjina masa bisa bada gudummawar naira milyan daya domin aikin gyaran masallacin Surko yayin da ya sanya fitilu masu amfani da hasken rana guda 30 wadda su ka kawata garin tare da Samar da tsaro da daddare.
A nasa bangaren, Sakataren jam'iyar NNPP na karamar hukumar Birnin Kudu Malam Aliyu Kaila, ya ce matsalolin jam'iyar PDP su ka jawo komawarsu jam'iyar NNPP amma a yanzu ya yanke shawarar tafiya jam'iyar APC domin mara baya ga Hasken Birnin Kudu da Buji Engineer Sulaiman Da'u Aliyu a matsayin matashi mai burin kawo cigaban al'umma.
Ya ce ya kuduri niyyar sauyin sheka zuwa jam'iyar APC ne saboda ya zama wajibi ga jama'a su mara baya ga dan siyasa mai kishin al'umma domin kawo cigaban rayuwa.
A nasu bangaren, Sakataren Kwamatin Harkokin Siyasa na Hasken Birnin Kudu da Buji, wato Malam Sule Adamu da Kuma jami'in tsare tsare Alhaji Sule Bako, sun bayyana taron tattaunawar a matsayin sharar fage na karbar fitartun 'ya'yan jam'iyar PDP daga mazabun karamar hukumar Birnin Kudu a karkashin kulawar Engineer Sulaiman Da'u Aliyu a nan gaba.

08/08/2025

08-08-2025 STKK
Majalissar zartarwa ta karamar hukumar Sule Tankarkar ta amince da gudanar da muhimman aiyuka a bangarorin kiwon lafiya da sauran aikace aikacen ciganan alumma
Taron majalissar bisa jagorancin shugaban KH Tasi’u Adamu, ya amince da gina makarantun Tsangaya guda uku na zamani da za a sanyawa sunayen wasu fitattun yan siyasa na yankin da s**a rasu
Za a gina makarantun tsangayar ne a garuruwan Danzomo da Shabaru da kuma Rukutu wadanda za a sanyawa sunan marigayi Sanata Dalha Ahmad Dan Zomo da Honourable Musa Waziri Kamus da kuma Honourable Ali Ado.
Haka kuma majalissar ta amince da gyaran masallatan Juma’a na Hannun Giwa da Dan Ladin Gumel da masallacin Tsangaya na Sule Tankarkar
Haka kuma za a gina sabbin masallatan kamsisalawati guda biyar a garuruwan Chiromawa da Kofar Yamma da kuma Babban Sara.
Majalissar ta kuma amince da gina asibitoci matsakaita guda uku a Dan Makama da Mabia da kuma Sarkin Gandu
Haka kuma za a gina magudanan ruwa da kuma samarda ruwan sha mai amfani da hasken rana a garin Lula
Majalisar zartarwar ta kuma amince da sayo kayayyakin gyaran tuka tuka na naira miliyan 11 da kuma amincewa da kudi naira miliyan biyar da dubu dari biyar domin sayen magunguna da feshin maganin sauro
Haka kuma an amince da gyaran ofishin shugaban majalissar kamsiloli da kuma ofisoshin masu bada shawara guda bakwai don inganta ayyukan gwamnati a yankin
Shugaban KH ya ce aiyukan na daga cikin kudirorinsa guda biyar da ya yi koyi da ga cikin kudirorin gwamna 12 domin kyautata rayuwar jamaarsa

08/08/2025

08-08-2025 SCHOLARSHIP
Gwamnatin Jihar Jigawa ta amince ta sakin kuɗi fiye da naira miliyan 156 domin sayen tikitin jirgi na mayar da daliban Jigawa masu karatun likita 184 da s**a kammala hutunsu a gida zuwa makaranta a kasar Cyprus
Sakataren zartarwa na Hukumar bada tallafin Karatu ta Jiha Malam Saidu Magaji, ya sanar da hakan ga wakilinmu
Malam Saidu Magaji ya ce tuni rukunin farko na daliban mata 31 s**a tashi ta filin jirgin saman Lagos zuwa Istanbul inda za a dauke su zuwa Ercan na Cyprus don fara sabon zangon karatu.
Sakataren dake tare da daliban kafin tashin su , ya yaba da kulawar Gwamna Mallam Umar Namadi kan tallafawa daliban jihar nan domin ci gaba da karatunsu
Haka kuma ya nuna jin dadi da irin kulawar kwamishinan Ilmi mai zurfi ga daliban Jigawa dake karatu a ciki da kuma wajen kasar nan
Idan za a iya tunawa daliban Jigawa 184 masu karatun aikin likita a kasar Cyprus sun zo hutu bayan kammala zango na biyu na karatunsu kamar yadda gwamnati ta yi alkawarin kawo su hutu idan sun kammala zango na biyu na karatunsu

08/08/2025

08/08/2025 GOVERNOR WIFE
Mai dakin Gwamnan Jihar Jigawa, Hajiya Amina Umar Namadi ta yi kira ga Matan jihar nan su tabbatar suna shayar da jariran su nono zallar daga lokacin haifuwa zuwa watanni shida.
Ta yi wannan kiran ne a lokacin gangamin bikin tunawa da ranar shayar da jajirai nonon uwa zalla ta duniya wanda aka gudanar a garin Kirikasamma.
Hajiya Hadiza Umar Namadi, ta ce shayar da yara nonon uwa zalla tare da kula tsaftar su, nauyine da ya rataya akan iyaye, a saboda haka akwai bukatar maida hankali wajen shayar da yara nono zalla na tsawon watanni shida, inda daga bisani za a iya ciyar dasu nau’in abinci daban daban da zai kare su daga kamuwa da cututtuka.
Mai dakin Gwamnan ta lura cewa Mata a Jihar Jigawa suna da kokari wajen shayar da jariransu nonon zalla, amma akwai bukatar karfafa musu gwiwa domin shayar da yaran a matsayin su na manyan gobe.
Tun farko a jawabinsa na maraba, manajan hukumar lafiya matakin farko na karamar hukumar ta Kirikasamma, Malam Kabiru Musa ya godewa Maidakin gwamnan bisa ziyarar, inda yace hakan zai taimaka wajen kara wayar da kan iyaye Mata muhimmancin bawa jarirai nonon uwa zalla.
Wata kwararriya a fannin abinci mai gina jiki dake Asibitin koyarwa na Jami’ar tarayya dake Dutse, Madam Helen ta yi karin haske kan sinadaren da nonon uwa yake dauke da shi wajen inganta lafiyar jarirai.
Daga bisani Maidakin gwamnan ta raba kayan abinci mai gina jiki da inganta lafiyar yara.

08-08-2025                   FULATAMember representing Birniwa/Kirikasama/Guri Federal Constituency, Honourable Abubakar...
08/08/2025

08-08-2025 FULATA
Member representing Birniwa/Kirikasama/Guri Federal Constituency, Honourable Abubakar Hassan Fulata, has completed the Installation of solar powered street light in 13 out of 15 towns in Birniwa Local Government Area.
His Personal Aide in charge of Birniwa, Musa Muhammad Isyaku Birniwa, disclosed this during a phone interview with our correspondent.
He stated that the work was completed in the towns of Burseli, the new settlements of Birniwa, and within the towns of Diginsa, Jirgiwa, Matamu, Kibu, Laraba, as well as Tsangayar Yamma.
He added that the remaining two wards to benefit with the solar street light project are Matarar Batu and Kubuna, where works are still ongoing.
Musa Birniwa said the projects are aimed at beautifying the towns and improving security of lives and properties.
He noted that the projects are part of the federal legislator’s Constituency projects brought about by Dr. Abubakar Hassan Fulata to improve the wellbeing of the people.
Musa Muhammad Birniwa also stated that similar projects are being carried out in Kirikasamma and Guri local government areas.
He noted that the legislator also built a new masjid in Masewa town in Karanka ward and constructed two block of three classrooms in Fulatanan town to educate children.
Musa Birniwa added that Dr Fulatan has distributed science laboratory materials and science textbooks to students for improved teaching in learning process.
COV/MAG/IMBK

08/08/2025

8-8-25. AUYO
The Chairman of Auyo Local Government Council, Malam Binyaminu Ahmad Adamu Kafur, has charged newly appointed Senior Special Assistant, Personal Assistants and Special Assistant to the local government chairman to be fair and just in the discharge of their responsibilities.
He made the plea during the Inaugural ceremony of the 69 senior special assistant, personal assistants and special assistant at the Senator Ibrahim Hassan Hadejia Community Centre in Auyo.
Malam Binyaminu Kaffur reaffirmed the council's commitment to work hand in hand with stakeholders toward the provision of social amenities and infrastructure to ensure that dividend of democracy reach the nooks and crannies of the area.
He called on the people not to relent in offering prayers to enable those on the mantle of leadership succeed in the implementation of policies and programs that will uplift their living condition.
Earlier, the Chairman of the local branch of the APC Malam Saleh Muhammad Ganuwa expressed satisfaction with the council chairman's commitment to engaged party members to contribute their quarter toward the development of the area
Also speaking, a party Stalwart, Alhaji Umar Jura, commended the council Chairman for choosing the right persons to serve during his tenure and the appointees to cooperate and work deligently to justify the confidence reposed in them.
Speaking on behalf of the appointees, Malam Yakubu Muhammad Auyo and former sole administrator Mika'ila Auyo, thanked the council chairman for finding worthy to serve in that capacity and pledged their cooperation towards achieving the desired objectives.
PR/MUH/IMBK

08/08/2025

08-08-2025 STKK
Sule Tankarkar Executive Council has approved major funding for community development in healthcare and infrastructures.
The Executive Council meeting chaired by the council Chairman Tasi'u Adamu, approved the construction of three modern Tsangaya schools.
The schools would be constructed at Danzomo, Shabaru and Rukutu which when completed will be named after the late Senator Dalha Ahmad DanZomo, Musa Waziri Kamus and Honorable Ali Ado.
The council approved the construction and renovation of several mosques in Hannun Giwa, DanLadin Gumel and Tsangaya mosque in Sule Tankarkar town.
In addition five new daily prayer mosques will be constructed at Chiromawa village in Amanga ward, Kofar Yamma in Sule Tankarkar ward and one at Babban Sara.
Also the council approved the construction of three primary health centers at Dan Makama, Mai Mazari and Sarkin Gandu villages.
Other projects approved include a new drainage in Bango village and a solar-powered water scheme in Lula village.
The council also approved the sum of 11 million Naira for the purchase of hand pump materials to improve water supply while 5.5 million Naira was allocated for malaria prevention, including the purchase of medicine and mosquito sprayer.
The council also approved the renovation of the Local Legislative Speaker's office and seven Supervisory councillors offices to provide conducive atmosphere for administrative functions.
In his remark, the council Chairman Tasi'u Adamu stated that these initiatives are a core part of his Five-Point Agenda adapted from the Eleven-Point Agenda of Governor Malam Umar Namadi
PR/UG/MAG/IMBK

08/08/2025

08-08-2025 SCHOLARSHIP
Jigawa state government has approved and released over 156 million Naira for the return tickets of the 184 Jigawa students studying Medical and applied Medical courses in the Near East University in Cyprus.
The Executive Secretary of the state Scholarship Board, Malam Sa'idu Magaji, made this known in an interview with our reporter.
Malam Sa'idu Magaji explained that the first batch of 31 female students who were in Nigeria for a holiday after spending two academic session as part of the government policy were airlifted from Nnamdi Azikiwe International Airport Lagos to Istanbul for the commencement of the new academic session
The Executive Secretary who escorted the first batch of the students commended the passion and concern of Governor Mallam Umar Namadi towards supporting the indigenes of the state to further their education for the benefit of the state
He also commended the tireless efforts of the state Commissioner for Higher Education, Science and Technology Professor Isa Yusuf Chamo for ensuring the successful sponsorship of over 184 Jigawa state indigenes to further their studies abroad by the state government.
It will be recalled that 184 Medical and applied Medical courses Jigawa state students who are currently undergoing courses in the Near East University Cyprus arrived Jigawa for a holiday after spending two academic session in the university as part of the present administration's pledge to bring them back for a holiday after every two academic sessions.

PR/WUR/MAG/IMBK

08/08/2025

08/08/2025 GOVERNOR WIFE
Wife of the State Governor Hajiya Amina Umar Namadi has called on lactating Mothers to breast feed their children for the period of six Month after birth.
She made the called at the 2025 Breast feeding day campaign awareness in KiriKasamma Local Government area.
According to her, the World Health Organization recommended the exclusive breast feeding for the first six month of the new born baby adding that the breast feeding is not just a mother’s duty, but a share responsibility to ensure the provision of exclusive breast feeding.
Amina Umar Namadi added that the State was blessed with culture and values that motherhood is childcare, hence the need to be encourage.
Earlier in his welcome address, the PHC Manager Kirikasamma Local Government Malam Kabiru Musa applauded the effort of the Governor’s wife for launching the campaign in Kirikasamma, Birniwa and Guri local government areas.
Madam Helen, a nutritionist from Rasheed Shekoni Federal University Dutse Teaching Hospital highlighted the importance of six month breast feeding to children health.
About ninety lactating mothers of the three local government benefited from the nutritious baby food items, distributed by the wife of the Governor, Hajiya Amina Umar Namadi.
COV/AI/MAG.

07/08/2025

07-08-2025 projects
Jigawa State Government has completed 26 road projects inherited from the previous administrations in the state.
A statement issued by the chief Press Secretary to the governor, Hamisu Mohammed Gumel, said the state government also initiated 48 new roads at the length of 976 kilometres.
He said only the Maigatari – Babura road is yet to be completed due to additional length.
The spokesperson noted that Governor Umar Namadi initiated 48 road projects in which 30 of them have reached advanced stage of completion.
According to him, the ongoing Sara – Gantsa Road, which awarded at the cost of 11 billion naira and 15 feeder roads are at various stages of completion
Also, the ongoing Bulangu and Gandun Sarki township road projects as well as Dutse capital road networks are at 60 – 70 per cent completion.
MAG

Address

Kiyawa Road Dutse
Dutse

Telephone

+2348169154019

Website

https://x.com/@RadioJigawaNews

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Newsroom Radio Jigawa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Newsroom Radio Jigawa:

Share