DSV RADIO Television

DSV RADIO Television Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from DSV RADIO Television, Radio Station, No. 401 Aminu Kano Way Gordon Dutse, Dala Local Government, Dutse.

23/10/2024

Duba da irin yanayin da ake ciki na yawaitar zazzabin maleria da ke addabar al'uma, Dan takardar shugabancin karamar hukumar Gwale a karkashin inuwar jam'iyyar NNPP Hon. Abubakar Mu'azu (MOJO) babban amin dan takarar Mustapha Iyali Abdullahi (QUANTY) ya bullo da wani shiri mai taken Mojo Care, cikin shirin suna raba wa marasa kafin da ke fadin karamar hukumar magunguna tare da yi musu gwaje-gwaje akan cutukan maleria, da typhoid, da blood pressure, da ciwon hakori, da kuma gudawa, inda bayan tabbatar abin da ke damun mutum za a ba shi magani kyauta, Tsarin na kewaya wa dukkan mazabun da ke karamar hukumar domin cin moriyar sa ga mata, da maza, da yara da kuma manya.
Shirin ya sami karbuwa a duk fadin karamar hukumar ta Gwale, inda al'uma ke yin tururuwa suna karbar magungunan da kuna godiya da sa albarka.
A jawabinsa yayin gudanar da shirin Hon. Mojo ya tabbatar wa yan karamar hukumar Gwale cewa hakan so in tabi ne idan har Allah ya ba su nasara a wannan zabe mai zuwa lallai yanzu aka fara samun ribar dimokaradiiya.
A karshe ya yi kira ga al'umar jihar Kano da su yi zabe cikin kwanciyar hankali tare da bin doka da oda.

10 Oct. 2024 da misali 02:15pm I gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf ya kai zayarar gani da ido makarantun Governor's College ...
10/10/2024

10 Oct. 2024 da misali 02:15pm I gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf ya kai zayarar gani da ido makarantun Governor's College guda biyu da ke Kofar Nassarawa a karamar Birni (Kano Municipal Council) inda ya duba kujeru da tebura da aka jibge don sanya wa dalibai wanda hakan zai taimaka wa malamai da dalibai wajen gudanar da harkar koyo da koyarwa.
Gwamnan ya nuna matukar farin ciki kan irin Yadda aka inganta kayan, da kuma yadda ya ga daliban wadannan makarantun maza da mata suna cikin nishadi bisa wannan tagomashi da gwamnati ta yi musu,onda s**a yi ta tafi da shewa, da kuma ya wa gwamna Kabir addu'o'i da godiya.
A nasa jawabin gwamna Yusuf ya ja hankalin daliban da su yi amfani da kayan kamar yadda ya dace.

Ranar Alhamis 03 ga watan Satumba 2024 rana ce da gwamnatin jihar Kano karkashin jagorancin Alh Abba Kabir Yusuf ta raba...
04/10/2024

Ranar Alhamis 03 ga watan Satumba 2024 rana ce da gwamnatin jihar Kano karkashin jagorancin Alh Abba Kabir Yusuf ta raba kayan koyo da koyarwa karkashin shirinta na tabbatar da dokar tabaci kan harkar ilmi da aka kaddamar a watannin baya.
Gwamna Kabir ya kashi takobin dawo da harkar ilmi cikin hayyacinta kamar yadda ya ce, Kahan ta sa aka samar da littafan karatu da na rubtu, da alli, da dubban kujeru da tenura, da sauran kayan bukata don raba wa a makarantun firamare da sakandare, wanda zai saukaka harkar koyo da koyarwa da samar da inganta cent ilmi a fadin jihar.

A Karo na 2 gwamnatin jihar Kano ta kara rarraba kayan karatu da rubutu da sauran kayayyakin bukata a fagen ilmi, hakan ...
04/10/2024

A Karo na 2 gwamnatin jihar Kano ta kara rarraba kayan karatu da rubutu da sauran kayayyakin bukata a fagen ilmi, hakan na cikin ayyukan da gwamnatin ta sha alwashin gudanar wa kan tsarin dokar ta baci da gwamnatinsa ta sanya kan harkar ilmi a fadin jihar nan.
Gwamna Yusuf ya nuna damuwa kan adadin yaran da basa zuwa makaranta da kuma makarantun kwana da aka rufe wanda ya dura alhakin hakan akan gwamnatin da ta shude, a wannan karon ma Alh Abba Kabir ya jagoranci raba dubban kujeru, da tebura, da latattafan rubutu, da na karatu, da rijistar halartar aji, da littafin tsara hanyar koyarwa, da kwafin sabon take Nigeria, da kuma gina daruruwan sababbin ajujuwa a makarantun firamare da saka dare na jihar nan.
Gwamna Kabir ya tabbatar cewa ilmi shi ne kashin bayan samar da kyakkyawar gobe ga kowacce al'uma, don haka ya ya yi kira ga iyaue da duk masu ruwa da tsaki da su bai wa wannan shiri goyon baya.

A yayin gudanar da bikin murnar sanar samun yancin Nigeria, gwamna Abba Kabir Yusuf na jihar Kano ya kai ziyara zuwa gid...
02/10/2024

A yayin gudanar da bikin murnar sanar samun yancin Nigeria, gwamna Abba Kabir Yusuf na jihar Kano ya kai ziyara zuwa gidan kula da marayu da ke birnin Kano inda ya gabatar da jawabai masu sosa zuciya, ya ce yaran yaya ne kamar kowadanne yara, kuma suna da damar rayuwa kamar kowa, da samun ilmi, da duk wata dama da kowa ya ke da ita, domin basu da hannu wajen kasancewarsu cikin wannan hali, Allah SWT shi ya so ya gan su a hakan, ya kuma ba su tabbacin cewa zai yi duk mai yiwuwa wajen ganin rayuwarsu ta inganta cikin walwala, da kula da ilminsu tun daga farko har zuwa jami'a kyauta, da kula da lafiyarsu, da gurin zamansu da abinci mai inganci, da koyar da su sana'o'i, da daukar dawainiyar aurar da su, da kuma ba su ayyukan yi bayan kammala karatunsu.
Ya kuma ja hankalin, al'uma da su rinka kallon su a matsayin cikakkun yaya kamar wadanda s**a Haifa,
A karshe gwamnan ya kewaya ciki da wajen gidan don ganin irin halin ya ke ciki, da kuma magance matsalolin da suke addabar sa,ya kuma zauna da yaran ya ci abinci tare da su cikin nuna kauna da tausaya wa.

Shin Zaka iya cire tsabar kudi har Naira Miliyan uku domin siyan  waya?
29/09/2024

Shin Zaka iya cire tsabar kudi har Naira Miliyan uku domin siyan waya?

Gwamnan jihar Kano Alh Abba Kabir Yusuf ya kaddamar da gangamin yaki da cetar shan'inna na shekara ta 2024 a karamar huk...
28/09/2024

Gwamnan jihar Kano Alh Abba Kabir Yusuf ya kaddamar da gangamin yaki da cetar shan'inna na shekara ta 2024 a karamar hukumar Dawakin Kudu, hakan wani kokari ne na fatattakar kayar cutar da ma sauran cutukan da ke addabar kananan yara.
Inda kamar yadda aka saba za a ci gada bi gidaje don ba da riga kafin kamuwa da cutar ga kananan yara domin dakile yaduwar cutar, musamman a jihar nan wacce guda daga cikin jihohi 18 na kasar nan da s**a fi fuskantar hadarin yawaitarta.
Gwamna Kabir ya ce za su hada gwiwa da dukkan hukumomin kula da lafiya da ma sauran jama'a don ganin shirin ya yi nasara, don ganin mun bai wa yaranmu kariya daga cutar.
Kuma ya yi kira ga iyaye da su bai wa shirin riga kafin goyon baya da kuma bin dukkan hanyoyin kiwon lafiya kauce wa sauran cutaka.

ILIMI :yadda Shahararren Dan jarida me bankada, Wanda ake Kira Bello Galadanchi (Dan Bello) ya gyara aji tare da zuba ka...
28/09/2024

ILIMI :yadda Shahararren Dan jarida me bankada, Wanda ake Kira Bello Galadanchi (Dan Bello) ya gyara aji tare da zuba kayan aiki irin na zamani akan kudi naira Miliyan 4.1 duk da tsadar rayuwar da ake ciki.

Dan Bello ya gudanar da wannan aiki ne kyauta a Daya daga cikin Makarantun cikin kwayar Birnin Kano domin nunawa Gwamnati yadda yakamata ace anyiwa Makarantun Gwamnati cikin kudade kalilan ,sa6anin yadda ake kashe makudan kudade akan ayyuka kalilan kuma marasa inganci.

Tajuddeen Shuaibu Koki.

A kokarin kara bunkasa harkokin kasuwanci da tattalin arzikin jihar Kano gwamnatin jihar ta kara kulla alaka a bangarori...
27/09/2024

A kokarin kara bunkasa harkokin kasuwanci da tattalin arzikin jihar Kano gwamnatin jihar ta kara kulla alaka a bangarori daban-daban da kasar India.
Hakan na cikin kunshi jawabin da gwamna Abba Kabir Yusuf ya yi a yayin da ya ke karbar babban kwamishinan kasar ta India
Mr. Shri G. Balasubramanian a fadar gwamnati a jiya Juma'a
Ya ce tun tsawon shekaru da s**a shude Kano da kasar India suke da alaka mai karfi a bangarorin ilmi, da noma, da lafiya, da kimiyya da kuma kasuwanci.
Hakan ya sa gwamnati ta tura yan asalin jihar nan da dama zuwa kasar India don karo karatu a fannoni daban-daban a wasu jami'o'in na India.
Ya tabbatar da kara hada gwiwa da kasar wajen kammala tashoshin samar wutar lantarki ta hanyar amfani da ruwa da a ke gina wa a Tiga da Chakawa don farfado da masa'antun da s**a durkushe,
Da yake mai da jawabi Mr. Shri G. ya ce ya kawo ziyarar ne don gabatar da kansa ga gwamna Kabir da tattauna al'amhran da za su amfani dukkan gangarorin biyu, da kuma yin aiki kafada da kafada da juna.
A karshe ya yaba wa gwamna Yusuf bisa irin karbar da ya yi musu, tare fatan cigaba da irin aiyukan da ya ke a fadin jihar nan.

Yadda Hussaina Matar Abbas Haruna Seaman Ta Fashe Da Kuka Farin Ciki Bayan Shafe Shekaru 6 Ana Tsare Da Mijinta.
27/09/2024

Yadda Hussaina Matar Abbas Haruna Seaman Ta Fashe Da Kuka Farin Ciki Bayan Shafe Shekaru 6 Ana Tsare Da Mijinta.

Ba zan sassauta wa masu cin hanci ba - Sabuwar Alkalin Alkalan Nijeriya Kekere-Ekun
27/09/2024

Ba zan sassauta wa masu cin hanci ba - Sabuwar Alkalin Alkalan Nijeriya Kekere-Ekun

26/09/2024

Address

No. 401 Aminu Kano Way Gordon Dutse, Dala Local Government
Dutse

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when DSV RADIO Television posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share