29/07/2026
Wani jami’in rundunar sojin Najeriya mai mukamin Kanal, Abdusalam Ude, ya rasa ransa a Abuja bayan wasu da ake zargin masu garkuwa da mutane ne s**a yi yunkurin sace shi.
Rahotanni sun bayyana cewa lamarin ya faru ne lokacin da maharan s**a tare Kanal Ude tare da kokarin yin garkuwa da shi. Sai dai jami’in sojan ya yi yunkurin hana su aiwatar da shirin nasu, lamarin da ya kai ga harbe shi har lahira.
Majiyoyi sun ce matar mamacin da direbansa sun samu raunuka sakamakon harbin da maharan s**a yi yayin kai harin, kuma ana ci gaba da kula da su a asibiti.
Wannan lamari ya sake jefa al’umma cikin fargaba tare da tayar da hankula kan tabarbarewar matsalar tsaro a Babban Birnin Tarayya Abuja, wanda a baya ake kallonsa a matsayin ɗaya daga cikin wuraren da s**a fi tsaro a Najeriya.
Me zaku ce?