04/12/2025
Labaran Yammacin Alhamis,
13/06/1447AH - 04/12/2025CE.
Ga Takaitattun labaran.
Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya rantsar da Jana ɗin Christopher Musa a matsayin Ministan Tsaro, sa’o’i kaɗan bayan Majalisar Dattawa ta tabbatar da nadinsa.
A Abuja, Tinubu ya amince da naɗin tsohon Kwamishinan Ribas da kuma Dambazau a matsayin jakadu, domin inganta hulɗar diflomasiyyar Najeriya.
Rundunar Sojin Najeriya ta ce ta kai samame a Plateau, inda ta cafke wani mutum da ake zargi da kera da sayar da mak**ai ga ‘yan bindiga.
Kakakin Majalisar Wakilai, Tajudeen Abbas, ya taya sabon Ministan Tsaro, Janar Musa, murnar rantsuwar sa, yana mai kiran a yi aiki tukuru wajen tabbatar da tsaro.
Hukumar NAPTIP reshen Kano ta k**a wani mutum da ya yi yunƙurin safarar mata bakwai zuwa Saudiyya.
Akalla mutum shida sun mutu, wasu 13 sun jikkata, bayan wata bas mai ɗauke da nakasassu ta yi hatsari a hanyar Lokoja–Okene.
Rundunar ‘Yan Sanda ta kubutar da dalibai biyar na Jami’ar Rivers da aka yi garkuwa da su.
A Jihar Imo, an k**a wata mace mai shekaru 38, Juliet Igwe, bisa zargin kona sassan jikin yarinya mai shekaru shida da ke yi mata aikin gida.
INEC ta bayyana cewa daga cikin ’yan Najeriya miliyan 9.89 da s**a fara yin rijistar PVC ta intanet, miliyan 2.57 ne kacal s**a kammala cikakken rijista.
Gwamnan Abia, Alex Otti, ya ce ziyarar sa zuwa fadar Shugaba Tinubu ba ta da nasaba da sauya sheƙa zuwa APC, illa tattaunawa kan batun Nnamdi Kanu.
Gwamnan Zamfara, Dauda Lawal, ya gabatar da kasafin kuɗin N861.337bn na shekarar 2026 ga Majalisar Dokokin jihar.
Kotu ta fara sauraron roƙon Nnamdi Kanu na neman a mayar da shi daga kurkukun Sokoto zuwa wuri dabam.
A Abuja, rundunar ’yan sanda ta tabbatar da rasuwar jami’i ɗaya bayan hatsari a kan hanyar Sani Abacha Expressway.
Yan majalisar Jihar Zamfara biyu daga jam’iyyar APC sun sauya sheƙa zuwa PDP.
Ma’aikatan Shari’a na Jihar Kogi sun fara yajin aiki, saboda biyan ba su bashin albashi da kuɗin hutun shekara.
Bishop Matthew Kukah ya ce koyar da kai kariya ba zai magance matsalar tsaro ba, har sai gwamnati ta gyara tsarin tsaron ƙasa.
Hukumar NDLEA ta k**a mutum 44 tare da kwace kilo 2,059 na miyagun ƙwayoyi a Jihar Edo.
Ma’aikatar Lafiyar Bauchi ta ce mutum 2,246 masu dauke da cutar HIV ne ke ci gaba da karɓar kulawa kyauta a jihar.
Rundunar ’yan sanda ta k**a mutum 20 da ake zargi da kai hari ga yan banga a Jihar Delta.
’Yan bindiga sun yi garkuwa da wani jigon APC, Oriade, a Ibadan.
Google ta fitar da rahoton Year in Search 2025, inda aka nuna cewa Sen. Natasha Akpoti-Uduaghan da Eberechi Eze s**a fi bincike a Najeriya.
Gwamnati ta ce China za ta tallafa wa Najeriya wajen yaki da ta’addanci da farfado da harkokin kasuwanci.
Shugaban Faransa, Emmanuel Macron, ya isa China domin neman tsagaita wuta a yakin Ukraine.
Shugaban Rasha, Vladimir Putin, ya ce Rasha ba za ta janye daga Donbas ba, sai ta tabbatar da karɓe ikon yankin gaba ɗaya.
Kungiyar Amnesty International ta ce yarjejeniyar zaman lafiya a DR Congo ba ta dakatar da cin zarafin bil’adama ba.
A Senegal, daliban Jami’ar Cheikh Anta Diop sun yi arangama da ‘yan sanda saboda tsaikon biyan su tallafin karatu.
Putin ya isa Indiya domin tattaunawa kan faɗaɗa harkokin tsaro da kasuwanci tsakanin kasashen biyu.
Tarayyar Turai ta fara tattauna amfani da kadarorin Rasha domin taimakawa Ukraine.
Wani jirgin saman sojin Amurka nau’in F-16C ya yi hatsari yayin atisaye a kusa da San Bernardino, California.
A Australia, Meta ta fara cire yara daga Facebook, Instagram da TikTok, bisa manufofin tsaro na intanet.
*Daga Harisata dan Wahb (R) Manzon Allah (ﷺ) ya ce: ((Shin ba na ba ku labari game da 'Yan wuta ba? Duk mai halin tashin hankali, mai mummunar dabi'a, mai girman kai))*
📚 Bukhárí da Muslim.