Mujallar Arewa

Mujallar Arewa Mujallar Arewa jarida ce da take kawo muku sahihan labarai da Harshen Hausa akan Abubuwan da suke faruwa a Arewacin Najeriya da ma Duniya baki daya
(2)

MINISTAN MATASA....Daga Rabiu Biyora Ganin irin yadda Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya tsaya tsayin daka wajen jana'izar mar...
22/07/2025

MINISTAN MATASA....

Daga Rabiu Biyora

Ganin irin yadda Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya tsaya tsayin daka wajen jana'izar marigayi tsohon Shugaban Nigeria Muhammadu Buhari da kuma kyakkyawar alakar dake tsakanin Buhari da Tinubu sai nake ganin abu ne mai kyau a siyasa Shugaba Tinubu ya bawa Yusuf Buhari mukamin Minista musamman Ministan Matasa...

Yin hakan zai kara dankon zumunci sosai...

A yanzu Yusuf Buhari yana da shekara 33 a duniya shekarun da zasu bashi damar tsayawa kowacce irin takara a Nigeria...

A bangaren siyasar Arewa kasancewar Yusuf Buhari minista a gwamnatin Tinubu hakan zai iya zama dalilin da Tinubu zai samu karin magoya baya daga yankin Arewa Maso Yamma.....

Tsohon Mataimakin Shugaban Majalisar Dattijai Sanata Omo Ovie Agege da tsohon Mataimakin Kakakin Majalisar Wakilai Hon. ...
22/07/2025

Tsohon Mataimakin Shugaban Majalisar Dattijai Sanata Omo Ovie Agege da tsohon Mataimakin Kakakin Majalisar Wakilai Hon. Ahmad Idris Wase da sauran ƴan tawagarsu sun ziyarci gidan marigayi tsohon Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari da ke Daura domin yi wa iyalinsa ta'aziyyar rasuwarsa.

Shin Kuna goyon bayan Hawa'u Halliru gwangwazo ta cigaba da fitowa a shirye shiryen gidan talabijin na RFI - Hausa ?
20/07/2025

Shin Kuna goyon bayan Hawa'u Halliru gwangwazo ta cigaba da fitowa a shirye shiryen gidan talabijin na RFI - Hausa ?

TIRƘASHI: Shugabaɲ Ƙaramar Hukumar Rijau Dake Jihar Neja, Honarabul Ɗanladi K. Uganda Ya Shiga Dãji Domin Yakar Ƴãɲ Bìɲd...
20/07/2025

TIRƘASHI: Shugabaɲ Ƙaramar Hukumar Rijau Dake Jihar Neja, Honarabul Ɗanladi K. Uganda Ya Shiga Dãji Domin Yakar Ƴãɲ Bìɲdiģa Da S**a Addabe Ƙaramar Hukumar

Wace fata za ku yi masa?

A Yau ne Alhaji Abdul Samad Rabiu ya isa Daura Domin ta'aziyya ga iyalai da makusantan Marigayi Tsohon Shugaban kasa Muh...
20/07/2025

A Yau ne Alhaji Abdul Samad Rabiu ya isa Daura Domin ta'aziyya ga iyalai da makusantan Marigayi Tsohon Shugaban kasa Muhammadu Buhari.

Daga Karshe Shiekh Sani Yahaya Jingir Ya Janye Kalaman Sa Tare Da  Bada Haƙuri Kan Kalaman Da Ya Yi Wa Mataimakin Sa Shi...
18/07/2025

Daga Karshe Shiekh Sani Yahaya Jingir Ya Janye Kalaman Sa Tare Da Bada Haƙuri Kan Kalaman Da Ya Yi Wa Mataimakin Sa Shiekh Yusuf Sambo

Daga Muhammad Kwairi Waziri

DA DUMI-DUMI: Mataimakin Shugaban kasa Kashim Shettima ya k**a hanyar komawa Abuja daga Katsina bayan kammala addu’ar Uk...
17/07/2025

DA DUMI-DUMI: Mataimakin Shugaban kasa Kashim Shettima ya k**a hanyar komawa Abuja daga Katsina bayan kammala addu’ar Ukun margayi Buhari

Tun bayan mutuwar tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari Kashim ke zirga-zirga daga London zuwa Katsina har sai yau zai koma Abuja

Mun kasa sauƙa a filin jirgin saman Katsina saboda rashin wurin sauƙa-Akpabio Kimanin jirage Goma Sha Biyar ne aka bayya...
17/07/2025

Mun kasa sauƙa a filin jirgin saman Katsina saboda rashin wurin sauƙa-Akpabio

Kimanin jirage Goma Sha Biyar ne aka bayyana sun kasa sauƙa a filin jirgin sama na Malam Ummaru Musa Ƴar'adua da ke Katsina a ranar Talatar da ta gabata saboda rashin wurin da jiragen za su sauƙa.

Shugaban majalisar Dattawa ya tabbatar da wannan labarin inda yace rashin samun wurin yasa dole s**a koma Abuja sai daga baya s**a dawo s**a sauka domin yin ta'aziyya ga iyalan marigayi tsohon shugaban ƙasa Buhari

Mujallar Arewa

Majalisar Dokokin Kano na shirin bincikar shugabar Karamar Hukumar Tudun Wada ALGON. Sa'adatu Yusha'u.Majalisar dokokin ...
17/07/2025

Majalisar Dokokin Kano na shirin bincikar shugabar Karamar Hukumar Tudun Wada ALGON. Sa'adatu Yusha'u.

Majalisar dokokin jihar Kano, ta sha al’washin gudanar da bincike kan ƙorafin da wasu manoma ke yi na zargin shugabancin ƙaramar hukumar Tudun Wada karkashin jagorancin Hajiya Sa’adatu Yusha'u, kan kwace musu gonakinsu da ke Dajin Gurfa a karamar hukumar ta Tudun Wada a Kano.

‎Shugaban masu rinjaye na Majalisar Alhaji Lawan Hussain Cediyar ƴan Gurasa ne ya tabbatar da hakan jim kaɗan bayan amsa gayyatar da Majalisar ta yi wa kungiyar da ke rajin kare hakkin Ɗan-adam da tabbatar da daidaito a cikin al'umma wadda ta aike wa Majalisar korafin Manoman.

‎Da ya ke jawabi bayan amsa gayyatar da Majalisar ta yi musu, shugaban kungiyar Sa'id Bin Usman, ya ce akwai tarin korafe-korafe kan dambarwar hakkin mallaka na gonaki tsakanin shugabancin karamar hukumar Tudun Tada da kuma manoman yankin.

‎Manoma da dama ne a Dajin na Gurfa da ke yankin karamar hukumar Tudun Wada s**a shigar da korafin su kan zargin shugabar ƙaramar hukumar da ƙwace musu Gonakin su, in da kuma suke fatan majalisar dokokin jihar kano da ta duba kokensu domin samar musu da adalci.

TIRKASHI:-'Buhari Yayi Min Wasiyyar Cewa ‘Don Allah In Kula Da Talakawan Najeriya’ –Inji- Peter ObiTsohon ɗan takarar sh...
17/07/2025

TIRKASHI:-'Buhari Yayi Min Wasiyyar Cewa ‘Don Allah In Kula Da Talakawan Najeriya’ –Inji- Peter Obi

Tsohon ɗan takarar shugaban ƙasar Najeriya na jam’iyyar Labour Party Peter Obi ya bayyana cewa marigayi Shugaba Muhammadu Buhari ya yi masa wasiyya a lokacin kamfen na 2023 da cewa: “Don Allah ku kula da talakawan Najeriya.” Obi ya bayyana hakan ne a ziyarar da ya kai Daura domin yin ta’aziya ga iyalan marigayi Buhari.

Ya ce bai halarci jana’izar ba ne saboda tsaiko a filin jirgin sama na Katsina, amma ya ziyarci iyalan domin nuna girmamawa da ƙauna. Obi ya ce Buhari ya yi iya ƙoƙarinsa wajen shugabanci, kuma ya bukaci 'yan siyasa da kada su mayar da makoki siyasa.

Me Zakuce?

" Har Ga Allah Bànyí Niyyàr Yàfiyà Ga Buhari Ba Amma Sabóda Tàusayin Dansa Yusuf Ne Yasa Wallahi  Naji Na Yafewa Mahaifi...
17/07/2025

" Har Ga Allah Bànyí Niyyàr Yàfiyà Ga Buhari Ba Amma Sabóda Tàusayin Dansa Yusuf Ne Yasa Wallahi Naji Na Yafewa Mahaifinsa Dukkan Hakkínà Dake Kàñsa Tareda Rokon Allah Ya Masa Rahama Ya Gafarta Masa"

Cewar, Rukayya Abdullahi Sokoto

17/07/2025

I got over 400 reactions on one of my posts last week! Thanks everyone for your support! 🎉

Address

Fct Abuja

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Mujallar Arewa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Mujallar Arewa:

Share