Aliyu Said Gamawa

Aliyu Said Gamawa Aliyu said Gamawa

07/04/2026

HIMMA BA TA GA RAGO:
Godiya ta tabbata ga Allah da ya halatta mana neman abin Kai, Kuma aka Sanya sana'a ta zamo ibada Mai taron falla da albarka.

Ana fatan kowanni mumini ya tashi ya tsaya wajen neman halal, Kuma mu gujewa cin haramun a rayuwar mu

Abin kyama ne a addini, haka baya cikin koyarwar Annabi (saw) Mutum ya zama cima zaune, Dan maula, ko rago mai zaman jiran tsammani

Gaskiyata masu magana s**a ce:
1. Na zaune baya nasa (kullum Yana zan yi har komi ya wuce shi)
2. Na zaune baiga gari ba (Yana zaman Shan inuwa Maza suna duniya wajen nema)
3. Na zaune gwanin kokawa (kullum Yana tsara nema da Samu a baki har dama ta wuce shi)

Yan uwa mu kula da sana'oin mu na gado kada mu raina su, Mu koyi halatattun dabarun zamani na neman kudi. Ka da mu ajiye Noma, Kiwo da kanin kofi/ fawa

Mu Sani falalar Allah tana da yawa, duk Wanda ya dage ya tashi ya nemi taimakon Allah zai Samu daga albarkar kasuwanci.

Mata da Matasa a tashi a nemi halal ta hanyar halal. Allah ya bamu dacewa duniya da lahira, amin

07/04/2026

MATASHIYA:
1. A rayuwa ana son bawa yayi haƙuri. Mu Sani duk abin da bawa ke ciki Allah yana ganin mu.

2. Mu Sani wahala ba ta dauwama, amma ladan haƙuri yana dauwama, hakuri shine maganin zaman duniya

3. Bawa ya kula da ibada musamman sallah da addu’a, domin Allah ba Ya mantuwa. Allah Yana albarka ga rayuwar masu kula da addini

4. Kada zuciya ta Kai Mutum ga aikata haramun, duk halin da Mutum ke ciki wata rana zai wuce, hakika tare da wahala akwai sauƙi.

5. Idan Allah Ya jiɓanci lamuranka, zai sauƙaƙa maka duk wani abu mai wahala. Hakika ba mai iya bayarwa ko hanawa sai Allah, don haka mu dogara ga Allah shi kadai

6. Muna rokon Allah Ya tafiyar da rayuwar mu a tsari, kuma Ya cika mana abin da muka ɗauka ba zai yiwu ba.
Ya Allah, Ka jiɓanci lamarinmu, amin

Aliyu Said Gamawa

27/03/2026
27/03/2026

*Bayan Ramadan 🌙*
Azumi bai kare ba da karewar ramadan

Kuma ba a tafiyar da Qur'ani ba da wucewar ramadan

Ba za a rufe masallatai don an kammala ramadan ba

Kuma ba za a dena amsar addu'o'i ba

Kuma ba a dena bada lada ga kyawawan ayyuka ba

Don haka; "...Ku bauta wa Ubangijinku har mutuwa ta zo muku." [15:99]

Mu kasance masu tsoron Allah, kada mu kasance bayin Allah na kwarai kadai a iya watan ramadan.

Mu kasance Rabbaniyyan [masanin addini mai aiki da abinda ya sani,kuma yana isar dashi]

Amma kada mu zama Ramadaniyan kawai (masu yin ibadu da ayyuka na kwarai acikin ramadhan kadai)

03/02/2026

FALALAR TAIMAKON MUTANE A KAN BUKATUNSU
Manzon Allah (ﷺ) ya ce : "Lallai in yi tafiya tare da ɗan’uwana domin biya masa wata buƙata shi yafi soyuwa a gare ni, fiye da na yi i‘itikafi a wannan masallaci, na tsawon wata guda" (yana nufin Masallacin Annabi (ﷺ).
Imam Addabarani.

26/12/2025

MATASHIYA:
Kada ka yi tarayya da mutane 4:

1. Wadanda idan suna tsararka, sai su rika yin gasa da kai, da kushe ka

2. Idan ka fi su, sai su rika yi maka hassada da cin kafa da aibata ka

3. Idan sun fi ka, sai su rika raina ka, suna yi maka wulakaci da nuna maka matsayin ka

4. Wadanda basa taimako sai in suna bukatarka, in sun gama da kai suyi gori

Irin wadannan mutane kada ka saki jiki da su, babu alheri a mu'amala da su

10/09/2025

Ɗan'uwa kasani mutuwa bazata jira har sai kazama mutumin kirki ba.

Ka zama mutumin kirki, kayi ta addu'a sai ka jira mutuwa.

23/05/2025

Madina

08/05/2025

🍃

"...... ku sabar ma ƴaƴanku aikata alkhairi domin shi aikin alkhairi yana dawowa".

-Ibn Abbas

Address

Garko Street
Gamawa

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Aliyu Said Gamawa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share