GANYE 24 MEDIA

GANYE 24 MEDIA Talla ku tuntube mu a 09121882331. GANYE 24 Abin alfaharin ku 👊🏼💯
(2)

GANYE 24 MEDIA SERVICES, Jarida ce mai kawo maku rahotanni masu faɗakarwa, Ilmantarwa da Nishaɗantarwa a harshen Hausa, wani lokaci a harshen Turanci, a cikin gida Najeriya dama ƙetare.

DANDALIN WASANNI: PSG sun fara saka idanu a kan ɗan tsakiyar Chelsea Moises Caceido Ɗan wasan tsakiyar na Ecuador yana s...
08/10/2025

DANDALIN WASANNI: PSG sun fara saka idanu a kan ɗan tsakiyar Chelsea Moises Caceido

Ɗan wasan tsakiyar na Ecuador yana samu soyayya daga Real Madrid, inda ake sa ran ƙungiyoyin biyu zasu gwabza domin neman fafutukar ɗaukar sa.

Tsohon Shugaban Ƙasa, Chief Olusegun Obasanjo, ya samu kyautar bujimin saniya daga Gwamnatin Jihar Bauchi a matsayin gir...
08/10/2025

Tsohon Shugaban Ƙasa, Chief Olusegun Obasanjo, ya samu kyautar bujimin saniya daga Gwamnatin Jihar Bauchi a matsayin girmamawa da yabo kan rawar da yake takawa wajen haɗa kai da tallafa wa ci gaban ƙasa.

Taron bayar da kyautar ya gudana ne a cikin garin Bauchi, a yau 8 ga Oktoba, 2025, inda jami’an gwamnatin jihar s**a bayyana cewa wannan tukuici na nuni da irin girmamawa da mutunta tsohon shugaban a idon al’umma.

DA DUMI DUMI: Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya shaidawa Majalisar Dokoki ta Ƙasa cewa gwamnati na neman amincewa da ta...
08/10/2025

DA DUMI DUMI: Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya shaidawa Majalisar Dokoki ta Ƙasa cewa gwamnati na neman amincewa da ta sake ciwo sabon bashin waje mai darajar dala biliyan $2.3, da kuma fitar da Sukuk na dala miliyan $500 domin shiga kasuwar lamunin kuɗin Musulunci ta duniya.

A cewar Kakakin Majalisar Wakilai, Hon. Tajudeen Abbas, wanda ya karanta buƙatar a zauren majalisar, wannan mataki na cikin tanadin dokar kula da bashi ta shekarar 2003.

An bayyana cewa manufar ɗaukar bashin ita ce tallafa wa aiwatar da kasafin kuɗi na 2025, sake biyan tsofaffin lamunin Eurobond, da kuma bunƙasa hanyoyin samun kuɗin shiga ta hanyar tsarin kuɗin Musulunci (Islamic Finance).

DA DUMI DUMI: Jam’iyyar adawa ta ADC ta sanar da sabbin dokoki da tsare-tsaren tantance ‘yan takara da za su tsaya mata ...
08/10/2025

DA DUMI DUMI: Jam’iyyar adawa ta ADC ta sanar da sabbin dokoki da tsare-tsaren tantance ‘yan takara da za su tsaya mata a zaben shekarar 2027.

A cikin sanarwar da jam’iyyar ta fitar, an bayyana cewa sabon tsarin zai tabbatar da gaskiya, adalci, da cancanta, domin tabbatar da cewa kowane dan takara ya cika sharuddan da s**a dace kafin samun tikitin takara.

Haka kuma, jam’iyyar ta jaddada cewa sabon tsarin zai taimaka wajen inganta tsari da mutunci a harkar siyasa, tare da karfafa amincewar jama’a ga jam’iyyar a lokacin zabe mai zuwa.

DANDALIN WASANNI: Dean Huijsen ya samu rauni kuma tuni ya bar sansanin tawagar ƙasar Sifaniya. Likitocin kungiyar kwallo...
08/10/2025

DANDALIN WASANNI: Dean Huijsen ya samu rauni kuma tuni ya bar sansanin tawagar ƙasar Sifaniya.

Likitocin kungiyar kwallon kafa ta Real Madrid sun ce ana sa ran ɗan wasan zai shafe tsawon makonni 2 zuwa 3 yana jinya.

Batun Takardun Bogi: Madugun adawa a Najeriya, Atiku Abubakar, ya bukaci a gudanar da cikakken bincike kan takardun shai...
08/10/2025

Batun Takardun Bogi: Madugun adawa a Najeriya, Atiku Abubakar, ya bukaci a gudanar da cikakken bincike kan takardun shaidar karatu na wasu ministocin gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu.

Atiku ya bayyana cewa wannan mataki zai taimaka wajen tabbatar da gaskiya da amana a cikin gwamnati, tare da kare martabar Najeriya a idon duniya.

Ya kuma yi kira ga hukumomin da abin ya shafa da su yi aiki ba tare da son rai ba, domin tabbatar da cewa duk wanda aka samu da laifi ya fuskanci hukunci bisa ka’ida.

DA DUMI DUMI: Shugaban Hukumar Alhazai ta Ƙasa (NAHCON), Farfesa Abdullahi Saleh Pakistan, ya shafe daren jiya a hannun ...
08/10/2025

DA DUMI DUMI: Shugaban Hukumar Alhazai ta Ƙasa (NAHCON), Farfesa Abdullahi Saleh Pakistan, ya shafe daren jiya a hannun Hukumar Yaki da Cin Hanci da Rashawa ta Ƙasa (EFCC) bayan da aka k**a shi bisa zargin wawure kuɗin aikin Hajji da s**a kai Naira biliyan 50.

EFCC ta tabbatar da cewa ta fara bincike a kansa kan zarge-zargen aikata manyan laifukan kuɗi da s**a shafi shirye-shiryen aikin Hajji na shekarar 2025.

Rahotanni sun nuna cewa Mataimakin Shugaban Ƙasa, Sanata Kashim Shettima, a ranar Litinin, ya kammala wani bincike da ya gano cewa shugaban hukumar ya ƙara kuɗin kujerar aikin Hajji na bana ba tare da amincewar gwamnati ba.

Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Geoffrey Nnaji, Ya Bayyana Dalilin Murabus Daga Gwamnatin TinubuTsohon Ministan Kimiy...
08/10/2025

Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Geoffrey Nnaji, Ya Bayyana Dalilin Murabus Daga Gwamnatin Tinubu

Tsohon Ministan Kimiyya, Fasaha da Kirkire-Kirkire, Geoffrey Nnaji, ya ce murabus dinsa daga majalisar ministocin Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya samo asali ne daga niyyarsa na kare mutuncinsa da kuma kauce wa duk wani abin da zai hana aiwatar da manufofin gwamnati cikin lumana.

Nnaji, wanda ya fice daga mukaminsa kwanan nan, ya bayyana cewa ba ya da hannu a wata rashin gaskiya ko wani laifi da ke da nasaba da dalilin murabus dinsa, k**ar yadda ake yayatawa a kafafen yada labarai.

A cewarsa, “Na yanke shawarar murabus ne domin kare martabana da kuma tabbatar da cewa ba ni bane silar wata tangarda ga tafiyar ‘Renewed Hope Agenda’ na Shugaba Tinubu.”

Nnaji ya ce yana alfahari da damar da ya samu na yin aiki a gwamnatin tarayya, sannan ya bukaci a ci gaba da bai wa sabbin shugabanni hadin kai don ciyar da kasa gaba.

Murabus dinsa ya haifar da ce-ce-ku-ce a fagen siyasa, yayin da wasu ke kallon lamarin a matsayin matakin girmamawa da kishin kasa, wasu kuma na bukatar karin bayani daga bangaren gwamnati.

Barka da safiya daga nan Borno fadan jihar Maiduguri.Daga ina kuke bibiyar GANYE 24 MEDIA
08/10/2025

Barka da safiya daga nan Borno fadan jihar Maiduguri.
Daga ina kuke bibiyar GANYE 24 MEDIA

Zargin Badakalar 4.5bn: Binciken Wayar Hannun Emefiele Ya Tsaiko Saboda Rashin Jituwa Tsakanin EFCC da LauyoyinsaAn samu...
08/10/2025

Zargin Badakalar 4.5bn: Binciken Wayar Hannun Emefiele Ya Tsaiko Saboda Rashin Jituwa Tsakanin EFCC da Lauyoyinsa

An samu tsaiko a ci gaba da binciken fasaha (forensic test) na wata wayar salula da ke da matukar muhimmanci a shari’ar zargin badakalar dala biliyan4.5 da ake tuhumar tsohon Gwamnan Babban Bankin Najeriya (CBN), Godwin Emefiele da aikatawa.

Rahotanni sun nuna cewa rashin jituwa tsakanin hukumar EFCC da lauyoyin kare Emefiele ne ya janyo tsaikon gudanar da binciken na musamman da za a yi a kan wayar.

Hukumar EFCC na kallon wayar a matsayin muhimmin abu da zai taimaka wajen gano muhimman bayanai dangane da zargin almundahana da cin hanci. Sai dai lauyoyin Emefiele na kokarin kare hakkin wanda suke karewa, suna cewa dole a bi doka da ka’ida kafin irin wannan bincike ya gudana.

Har yanzu ba a saka sabuwar rana ba domin ci gaba da sauraron shari’ar a gaban kotu, yayin da jama’a ke sa ido kan yadda al’amarin zai kaya a daya daga cikin manyan shari’un da s**a jawo hankalin kasa.

WATA SABUWA: Ana sarai tsohon Shugaban jam'iyyar APC na ƙasa Dr Abdullahi Umar Ganduje na iya  zama Sabon Shugaban Hukum...
07/10/2025

WATA SABUWA: Ana sarai tsohon Shugaban jam'iyyar APC na ƙasa Dr Abdullahi Umar Ganduje na iya zama Sabon Shugaban Hukumar Zaɓe mai zaman kanta ta Najeriya Wato INEC.

Hasashen dai da masa al'amuran yau da kullum s**ayi Sunce tabbas Ganduje shine mutum na Farko da yafi Cancanta da Wannan kujera Duba da tarin Ilminsa da kuma kwarewar sa a Fagen Lissafi.

Shin ya kuke kallon Wannan hasashe idan ya kasance gaskiya?

07/10/2025

Mai Girma Gwamnan Adamawa, yayi sub da baka cewa mutanen Ganye idan baku zabi PDP ba, ba za a gyara muku hanyar LCCN zuwa Mbulo-Jada ba.
~Inji Comrd. Adam Ibrahim Khalil Pola (Shugaban kungiyar Progressive Network for Democracy PND).

Address

Ahmadu Bello Way
Ganye

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when GANYE 24 MEDIA posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to GANYE 24 MEDIA:

Share