
15/01/2025
Wajibi ne Boko Haram ta dakatar da kashe-kashen da take yi - Amnesty
Ƙungiyar Amnesty International ta kira ga mayaƙan Boko Haram da su daina far wa mutane suna musu kisan kiyashi.
Ƙungiyar ta bayyana haka a wani martani da ta yi kan kashe sama da mutum 40 da mayaƙan s**a yi a wasu garuruwa da ke jihar Borno da ke arewa maso gabashin ƙasar a ranar 12 ga watan Janairu.
A wata sanarwa da shugaban ƙungiyar na Najeriya, Isa Sanusi ya fitar, ya ce, "Ƙungiyar Amnesty tana alla-wadai da kashe fararen hula da ƴan Boko Haram s**a yi, wanda ya ƙara nuna yadda rashin girmama ƴan'adam da dokokin duniya da ƙungiyar ke yi. Dole Boko Haram ne a hukunta ƴan Boko Haram da s**a yi shekaru suna azabtar da mutane, da yi wa dokokin duniya karan-tsaye.
Sanarwar ta ce bincike Amnesty ya nuna cewa mayaƙan Boko Haram sun yi wa manoman ƙawanya ne, sannan s**a ware mazan, s**a buɗe musu wuta, "sannan s**a bi waɗanda s**a yi yunkurin tserewa suna harbinsu."
"Bayan kashe fararen hula, Boko Haram na cigaba da yin garkuwa da mata da ƴan mata da sace-sace. Yadda suke cigaba da gudanar da wannan ta'asar na nuna akwai buƙatar a ƙara ƙaimi domin kare rayuwa da dukiyar al'umma."
GANYE 24 MEDIA