30/05/2026
Alhazan Adamawa Sun Karɓi Jakunkunan Kaya Masu Nauyin Kilogiram 23 Gabanin Dawowarsu Najeriya
Hukumar Jin Daɗin Alhazan Musulmi ta Jihar Adamawa ta sanar da karɓar jakunkunan kaya masu nauyin kilogiram 23 da aka tanadar wa alhazan jihar domin sauƙaƙa musu jigilar kayayyakinsu yayin dawowarsu gida bayan kammala aikin Hajjin bana.
Sanarwar da Jami’in Hulɗa da Jama’a na hukumar, Mikail Danjuma Mubi, ya fitar a ranar 30 ga Mayu, 2026, ta bayyana cewa kwamitin kula da kayan alhazai ya karɓi jakunkunan ne bisa umarnin Shugaban Hukumar, Malam Abubakar Abubakar S. Gurin.
A cewar shugaban hukumar, kowane bako daga jihar Adamawa zai karɓi jakunkuna biyu, kowacce tana ɗaukar kaya masu nauyin kilogiram 23, domin tabbatar da tsari da sauƙin jigilar kayayyaki yayin komawarsu Najeriya.
Ya buƙaci dukkan jami’an kula da alhazai (Schedule Officers), ciki har da na hedikwata da na sashen HSS, da su tabbatar sun karɓi jakunkunan cikin gaggawa tare da raba su ga alhazai cikin gaskiya da adalci, domin tabbatar da cewa kowa ya samu nasa kason.
Haka kuma, shugaban kwamitin kayan alhazai, Malam Salihu Abubakar Sadiq, ya yi kira ga alhazai da su bi ƙa’idojin da aka gindaya game da kaya, tare da tabbatar da cewa abubuwan da s**a saka a cikin jakunkunansu sun dace da dokokin sufuri da na kamfanonin jiragen sama.
Ya jaddada cewa babu wata jaka da za ta wuce nauyin kilogiram 24 k**ar yadda dokokin hukumomin jiragen saman Najeriya s**a tanada.
Malam Salihu ya yi gargadin cewa duk jakar da aka samu ta haura ƙa’idar nauyin da aka amince da ita za a iya buɗe ta tare da sake tsara kayanta domin rage nauyin kafin tashin jirgi, domin kauce wa saɓa wa dokokin sufuri.
A ƙarshe, Shugaban Hukumar Jin Daɗin Alhazan Musulmi ta Jihar Adamawa ya yabawa alhazan jihar bisa haƙuri, juriya, haɗin kai da goyon bayan da s**a bayar tun farkon gudanar da aikin Hajji zuwa yanzu.
Ya kuma yi addu’ar Allah Maɗaukakin Sarki Ya karɓi ibadunsu, Ya ba su lafiya da tsawon rai, tare da ba su damar halartar ƙarin lokutan Hajji cikin zaman lafiya da kwanciyar hankali.