GANYE 24 MEDIA

GANYE 24 MEDIA Talla ku tuntube mu a 09121882331. GANYE 24 Abin alfaharin ku 👊🏼💯
(1)

GANYE 24 MEDIA SERVICES, Jarida ce mai kawo maku rahotanni masu faɗakarwa, Ilmantarwa da Nishaɗantarwa a harshen Hausa, wani lokaci a harshen Turanci, a cikin gida Najeriya dama ƙetare.

MATSALAR TSÃRØ: Muna Nan Kan Bakarmu Na Kare Nijeriya Daga Matsalar Tsaro, Inji Ministan Tsaro, Janar Chiristopher Musa
30/05/2026

MATSALAR TSÃRØ: Muna Nan Kan Bakarmu Na Kare Nijeriya Daga Matsalar Tsaro, Inji Ministan Tsaro, Janar Chiristopher Musa

Dakarun Operation FANSAN YAMMA Sun Ceto Mutane 31 da Aka Yi Garkuwa da Su, Sun Kashe 'Yan Ta'adda Biyar a Zamfara da Kat...
30/05/2026

Dakarun Operation FANSAN YAMMA Sun Ceto Mutane 31 da Aka Yi Garkuwa da Su, Sun Kashe 'Yan Ta'adda Biyar a Zamfara da Katsina

Dakarun Rundunar Operation FANSAN YAMMA ta Sashe na 2 sun samu gagarumar nasara a hare-haren da s**a kai kan maboyar 'yan ta'adda a jihohin Zamfara da Katsina, inda s**a ceto mutane 31 da aka yi garkuwa da su tare da hallaka 'yan ta'adda biyar a wasu jerin samame da s**a gudanar.

A wata sanarwa da Mukaddashin Mataimakin Daraktan Hulda da Jama'a na Rundunar Sojin Najeriya ta 8 Division kuma Sashe na 2 na Operation FANSAN YAMMA, Laftanar Kanal Olaniyi Osoba ya fitar ranar 29 ga Mayu, 2026, ya bayyana cewa an samu nasarorin ne ta hanyar hadin gwiwar hare-haren sama da na kasa.

A jihar Zamfara, dakarun sun ceto mutane 31 da aka yi garkuwa da su a yankin Bagega zuwa Kawaye da ke karamar hukumar Anka. An samu nasarar ceton mutanen ne bayan wani sahihin farmakin sama da rundunar sojin sama ta Operation FANSAN YAMMA ta kai kan sansanonin 'yan ta'adda da ke yammacin dajin Bagega, sannan dakarun kasa s**a bi sahu domin fatattakar miyagun.

Rahoton ya ce wadanda aka ceto sun shafe makonni da dama a hannun masu garkuwa da mutane, kuma sun fito ne daga kananan hukumomin Maga, Gummi, Zuru, Wasugu, Bukuyyum da Anka da ke jihohin Zamfara da Sokoto. An ba su kulawar lafiya kafin a mayar da su ga iyalansu.

Haka kuma, a wani samame daban da aka gudanar a yankunan Maradun da Gidan Dan Jaja a Zamfara, dakarun sun yi artabu da 'yan ta'adda inda s**a kashe mutum biyu daga cikinsu tare da lalata sansanoninsu. An kuma kwato wasu bindigogi da aka kera da hannu da kuma babura guda hudu da ake amfani da su wajen aikata laifuka.

A jihar Katsina kuwa, dakarun sun tare wasu 'yan ta'adda a yankunan Ruwan Godiya da titin Sayaya a karamar hukumar Matazu yayin da suke shirin kai hari. Bayan musayar wuta mai zafi, an kashe 'yan ta'adda uku tare da kwato babura da wasu harsasai.

Sanarwar ta kara da cewa daya daga cikin wadanda aka kashe an gano cewa yana daga cikin mayakan fitaccen shugaban 'yan ta'adda, Muhammadu Fulani. Haka kuma an kwato bindigogi da babura daga wuraren da aka yi artabun.

Rundunar Operation FANSAN YAMMA ta jaddada kudirinta na ci gaba da yaki da ta'addanci da kuma tabbatar da tsaro da zaman lafiya ga al'ummomin yankin Arewa maso Yammacin Najeriya.

Alhazan Adamawa Sun Karɓi Jakunkunan Kaya Masu Nauyin Kilogiram 23 Gabanin Dawowarsu NajeriyaHukumar Jin Daɗin Alhazan M...
30/05/2026

Alhazan Adamawa Sun Karɓi Jakunkunan Kaya Masu Nauyin Kilogiram 23 Gabanin Dawowarsu Najeriya

Hukumar Jin Daɗin Alhazan Musulmi ta Jihar Adamawa ta sanar da karɓar jakunkunan kaya masu nauyin kilogiram 23 da aka tanadar wa alhazan jihar domin sauƙaƙa musu jigilar kayayyakinsu yayin dawowarsu gida bayan kammala aikin Hajjin bana.

Sanarwar da Jami’in Hulɗa da Jama’a na hukumar, Mikail Danjuma Mubi, ya fitar a ranar 30 ga Mayu, 2026, ta bayyana cewa kwamitin kula da kayan alhazai ya karɓi jakunkunan ne bisa umarnin Shugaban Hukumar, Malam Abubakar Abubakar S. Gurin.

A cewar shugaban hukumar, kowane bako daga jihar Adamawa zai karɓi jakunkuna biyu, kowacce tana ɗaukar kaya masu nauyin kilogiram 23, domin tabbatar da tsari da sauƙin jigilar kayayyaki yayin komawarsu Najeriya.

Ya buƙaci dukkan jami’an kula da alhazai (Schedule Officers), ciki har da na hedikwata da na sashen HSS, da su tabbatar sun karɓi jakunkunan cikin gaggawa tare da raba su ga alhazai cikin gaskiya da adalci, domin tabbatar da cewa kowa ya samu nasa kason.

Haka kuma, shugaban kwamitin kayan alhazai, Malam Salihu Abubakar Sadiq, ya yi kira ga alhazai da su bi ƙa’idojin da aka gindaya game da kaya, tare da tabbatar da cewa abubuwan da s**a saka a cikin jakunkunansu sun dace da dokokin sufuri da na kamfanonin jiragen sama.

Ya jaddada cewa babu wata jaka da za ta wuce nauyin kilogiram 24 k**ar yadda dokokin hukumomin jiragen saman Najeriya s**a tanada.

Malam Salihu ya yi gargadin cewa duk jakar da aka samu ta haura ƙa’idar nauyin da aka amince da ita za a iya buɗe ta tare da sake tsara kayanta domin rage nauyin kafin tashin jirgi, domin kauce wa saɓa wa dokokin sufuri.

A ƙarshe, Shugaban Hukumar Jin Daɗin Alhazan Musulmi ta Jihar Adamawa ya yabawa alhazan jihar bisa haƙuri, juriya, haɗin kai da goyon bayan da s**a bayar tun farkon gudanar da aikin Hajji zuwa yanzu.

Ya kuma yi addu’ar Allah Maɗaukakin Sarki Ya karɓi ibadunsu, Ya ba su lafiya da tsawon rai, tare da ba su damar halartar ƙarin lokutan Hajji cikin zaman lafiya da kwanciyar hankali.

ZABEN 2027: APM Ta Tsayar da Seyi Makinde a Matsayin Dan Takarar Shugaban Kasa na 2027Jam'iyyar Allied Peoples Movement ...
30/05/2026

ZABEN 2027: APM Ta Tsayar da Seyi Makinde a Matsayin Dan Takarar Shugaban Kasa na 2027

Jam'iyyar Allied Peoples Movement (APM) ta tsayar da Gwamnan Jihar Oyo, Seyi Makinde, a matsayin dan takararta na shugaban kasa a babban zaben shekarar 2027.

Makinde ya samu tikitin takarar ne bayan kammala zaben fidda gwani na shugaban kasa da jam'iyyar ta gudanar a birnin Ibadan na Jihar Oyo, inda aka tabbatar da shi a matsayin zabin jam'iyyar ba tare da wata hamayya ba.

Bayan tabbatar da nasararsa, an mika masa takardar shaidar cin zabe tare da tutar jam'iyyar domin jagorantar APM a babban zaben da ke tafe.

DA ƊUMI-ƊUMI: Ƙungiyar kwallon kafa ta PSG ta doke Arsenal a wasan daga kai sai mai tsaron gida wato P.KMe Za Ku Ce?
30/05/2026

DA ƊUMI-ƊUMI: Ƙungiyar kwallon kafa ta PSG ta doke Arsenal a wasan daga kai sai mai tsaron gida wato P.K

Me Za Ku Ce?

DA ƊUMI-ƊUMI: Jam'iyyar NDC ta tabbatar da Peter Obi da Rabi'u Kwankwaso a matsayin ƴan takara Shugaban Ƙasa da Mataimak...
30/05/2026

DA ƊUMI-ƊUMI: Jam'iyyar NDC ta tabbatar da Peter Obi da Rabi'u Kwankwaso a matsayin ƴan takara Shugaban Ƙasa da Mataimaki a zaɓen 2027.

Me Za Ku Ce?

MATSALAR TSÃRØ: Ƴan Bindiga Sun Sace Tsohon Kakakin Sojan Kasan Najeriya, Mejo Janar Rabe Abubakar (Mai Ritaya) Da Matar...
30/05/2026

MATSALAR TSÃRØ: Ƴan Bindiga Sun Sace Tsohon Kakakin Sojan Kasan Najeriya, Mejo Janar Rabe Abubakar (Mai Ritaya) Da Matarsa A Daidai Garin Matazu Akan Hanyarsa Ta Zuwa Katsina, Yau Asabar, k**ar yadda Jaridar Sahara Reporters ta ruwaito.

HATSARIN M9TĀ: Wasu Ƴan Yankin Darazo Dake Jihar Bauchi, Masu Zuwa Kasuwar Soro Sun Yi Hadarìn Mota A Safiyar Nan, A Gab...
30/05/2026

HATSARIN M9TĀ: Wasu Ƴan Yankin Darazo Dake Jihar Bauchi, Masu Zuwa Kasuwar Soro Sun Yi Hadarìn Mota A Safiyar Nan, A Gaba Da Nahuta, Mashigar Yalwan Darazo, Inda Mutane Da Dama S**a Jikkata

Daga Shuaibu Mai Swansea

CIKIN HOTUNA: Yadda Jagoran Kwankwasiyya, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, ya jagoranci taron tabbatar da yan takara a Jam'i...
30/05/2026

CIKIN HOTUNA: Yadda Jagoran Kwankwasiyya, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, ya jagoranci taron tabbatar da yan takara a Jam'iyyar NDC domin shiga zaben shekarar 2027 mai zuwa.

Taron wanda ya gudana ranar Juma'a a Kano, an tabbatar da Peter Obi da Kwankwaso a matsayin dan takarar shugaban Ƙasa da mataimaki, sai kuma Comrade Aminu Abdussalam Gwarzo a matsayin dan takarar Gwamnan Kano.

Alhaji Kassim Batayya an tabbatar dashi a matsayin dan takarar Sanatan Kano ta Kudu, yayin da Dr Nasiru Yusuf Gawuna ya zama dan takarar Sanatan Kano ta tsakiya, sai kuma yan takarar majalisar wakilai da majalisar dokokin Jihar Kano.

📸 Hon Saifullahi Hassan

DA ƊUMI-ƊUMI: Idan Gwamnati bata ceto dalibai 46 da aka sace ba nan da kwana Hudu zan jagoranci hada kudi domin amso fan...
30/05/2026

DA ƊUMI-ƊUMI: Idan Gwamnati bata ceto dalibai 46 da aka sace ba nan da kwana Hudu zan jagoranci hada kudi domin amso fansarsu -in ji Very Dark Man (VDM)

Me zaku ce?

BABBAR MAGANA: "Na Auri Wani Babban Mutum A Gwamnatin Tinubu Ya K**a Mun Gida Na Zuba Kayan Alatu Amma Sama Da Shekara B...
30/05/2026

BABBAR MAGANA: "Na Auri Wani Babban Mutum A Gwamnatin Tinubu Ya K**a Mun Gida Na Zuba Kayan Alatu Amma Sama Da Shekara Bai Taɓa Zuwa Inda Nake Ba A Ƙarshe Ma Cewa YaYi Be Sanni Ba", In Ji Fati Karishima

Jarumar Kannywood, Fati Karishima, ta bayyana cewa kamfen ɗin shugaban ƙasa Tinubu na 2023 shi ne abu mafi muni a rayuwata. Domin kuwa a shi ne ta haɗu da wani mutum wanda yanzu jami'i ne a gwamnatin ya aure ta ya kuma watsar da ita, k**ar yadda Dokin Ƙarfe TV ta ruwaito.

A cewarta, tun bayan auren nasu, mijin bai taɓa zuwa inda take ba, haka kuma bai amince ta je inda yake ba, sai dai su yi bidiyo call. Amma kuma ya k**a mata gidan haya tare da tura mata kuɗin cefane lokaci bayan lokaci.

Karishima ta ce bayan wasu watanni da fara zaman auren, ta fara fama da wata matsalar rashin lafiya da ba a san kanta ba, inda ta ke zubar da jini daga jikinta tsawon watanni biyar. Ta bayyana cewa duk da gwaje-gwajen da aka yi mata a asibiti, likitoci ba su gano musabbabin matsalar ba. Baya da haka har dogon suma take.

Jarumar ta ƙara da cewa a daidai lokacin da take fama da wannan yanayi, mijin nata ya daina tuntuɓarta tare da katse duk wata kulawa da yake ba ta. Ta ce ya daina ɗaukar kiran wayarta tare da dakatar da tura mata kuɗaɗen cefane.

A cewarta, lamarin ya kai ga duk abin da take da shi sai da ya ƙare kuma kowa ya guje ta. Sannan kuma a lokacin da ta nemi ya sake ta, mutumin ya ce shi bai aure ta ba, kuma bai ma san ta ba.

"Daga ƙarshe, komai da nake da shi ya ƙare. Lokacin da na nemi ya sake ni, sai ya ce wai bai taɓa aure na ba ta ya zai saki abin da bai aura ba, kuma bai ma san ni ba kwata-kwata". In ji Fati.

Daga Dokin Karfe TV ✍️

Address

Ahmadu Bello Way
Ganye

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when GANYE 24 MEDIA posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to GANYE 24 MEDIA:

Share