GANYE 24 MEDIA

GANYE 24 MEDIA Wannan ce sabuwar page na Jaridar GANYE 24 ku ci gaba da kasancewa da shirye shiryen mu masu fadakarwa da ilmantarwa. GANYE 24 abin alfaharin ku 💯
(1)

Wajibi ne Boko Haram ta dakatar da kashe-kashen da take yi - AmnestyƘungiyar Amnesty International ta kira ga mayaƙan Bo...
15/01/2025

Wajibi ne Boko Haram ta dakatar da kashe-kashen da take yi - Amnesty

Ƙungiyar Amnesty International ta kira ga mayaƙan Boko Haram da su daina far wa mutane suna musu kisan kiyashi.

Ƙungiyar ta bayyana haka a wani martani da ta yi kan kashe sama da mutum 40 da mayaƙan s**a yi a wasu garuruwa da ke jihar Borno da ke arewa maso gabashin ƙasar a ranar 12 ga watan Janairu.

A wata sanarwa da shugaban ƙungiyar na Najeriya, Isa Sanusi ya fitar, ya ce, "Ƙungiyar Amnesty tana alla-wadai da kashe fararen hula da ƴan Boko Haram s**a yi, wanda ya ƙara nuna yadda rashin girmama ƴan'adam da dokokin duniya da ƙungiyar ke yi. Dole Boko Haram ne a hukunta ƴan Boko Haram da s**a yi shekaru suna azabtar da mutane, da yi wa dokokin duniya karan-tsaye.

Sanarwar ta ce bincike Amnesty ya nuna cewa mayaƙan Boko Haram sun yi wa manoman ƙawanya ne, sannan s**a ware mazan, s**a buɗe musu wuta, "sannan s**a bi waɗanda s**a yi yunkurin tserewa suna harbinsu."

"Bayan kashe fararen hula, Boko Haram na cigaba da yin garkuwa da mata da ƴan mata da sace-sace. Yadda suke cigaba da gudanar da wannan ta'asar na nuna akwai buƙatar a ƙara ƙaimi domin kare rayuwa da dukiyar al'umma."

GANYE 24 MEDIA

Rundunar sojin Najeriya ta haramta amfani da jirage marasa matuƙa a yankin arewa maso gabasRundunar haɗin gwiwa ta sojoj...
15/01/2025

Rundunar sojin Najeriya ta haramta amfani da jirage marasa matuƙa a yankin arewa maso gabas

Rundunar haɗin gwiwa ta sojojin Najeriya (operation Hadin Kai) da ke gudanar da ayyukan tsaro a yankin Arewa maso Gabashin ƙasar ta haramta amfani da jirage marasa matuƙa a yankin.

Kwamandan rundunar sojan sama, Air Commodore UU Idris, wanda ya bayar da wannan umarni a wata sanarwa, ya ce amfani da jirage marasa matuƙa ba tare da izini ba yana haifar da barazana a jihohin Borno da Yobe da kuma Adamawa.

Ya bayyana cewa hukumomin gwamnati da wasu masu zaman kansu s**an yi amfani da jiragen ba tare da izinin ɓangaren sojin sama na rundunar ta Operation haɗin kai, k**ar yadda Daily Trust ta ruwaito.

Sanarwar ta ƙara da cewa ƴanbingdiga sun fara ƙwarewa wajen amfani da jiragen sama marasa matuka wurin kai hare-haren kan dakarun soji da kuma muhimman ababen more rayuwa na ƙasa.

''Cikin ƴan kwanakin nan, an samu rahotannin ganin jirage mara matuƙa a wasu wurare da ke kusa da fagen daga. A ranar 7 ga watan Janairun 2025, wani fasinja da ke cikin wani jirgin sama mai zaman kansa daga Maiduguri zuwa Monguno an k**a shi da wani jirgi mara matuki a wani bincike da aka gudanar kan jirgin, inda aka ƙwace jirgin mara matuƙi, kuma a halin yanzu ana cigaba da bincike.'' in ji sanarwar.

Daga shafin BBC HAUSA

GANYE 24 MEDIA

Wutar dajin Los Angeles ta haddasa asarar dala biliyan 150 a CaliforniaWasu alƙaluman ƙwararru da ke sanya idanu kan wut...
15/01/2025

Wutar dajin Los Angeles ta haddasa asarar dala biliyan 150 a California

Wasu alƙaluman ƙwararru da ke sanya idanu kan wutar dajin Los Angeles can a jihar California ta Amurka sun nuna yadda adadin ɓarnar da wutar ta haifar kawo yanzu ya iya zarta dala biliyan 150, ninki 3 na asarar da a farko aka yi hasashen wutar za ta haddasa.

Wutar dajin ta fiye da mako guda wadda a baya masana su ka ƙiyasin za ta haddasa asarar dala biliyan 50, tuni s**a sauya matsaya inda ƙwararrun ke cewa tun a yanzu wutar dajin ta haddasa asarar da ka iya zarta dala biliyan 150 a wani yanayi da har yanzun ba a iya shawo kanta ba, lura da yadda ƙaƙƙarfar iskar Santa Ana da ke rarraba wutar zuwa sassa daban-daban ke barazana ga ƙoƙarin da ake na kashe wutar.

Masu aikin kashe gobarar sun bayyana cewa zai iya kai aƙalla kwanaki 3 a nan gaba gabanin iya shawo kan wutar lura da yadda iskar ke mayar da aikinsu baya.

Zuwa yanzu wutar dajin ta hallaka mutane 24 baya ga ƙone kadada dubu 40 a iya yankunan birnin na Los Angeles yayinda ta ƙone kadada dubu 23 a Palisades a wani yanayi da kuma wutar ke barazana ga Brentwood da Encino da kuma Westwood.

A gefe guda mahukuntan na Los Angeles sun ce zuwa yanzu wutar ta ƙone gine-ginen da s**a kai dubu 12 da 300, a wani yanayi da aka kwashe mutanen da yawansu ya kai dubu 92 ake kuma kan hanyar kwashe wasu ƙarin dubu 89.

Ƙwararru a ɓangaren kiwon lafiya na ci gaba da kiraye-kiraye wajen ganin al’ummomin da ke kusa da yankunan da wannan wuta ke ci gaba da ci kan su kaucewa shaƙar hayaƙinta saboda illar hakan ga lafiya.

Tuni da aka samar da asusun tallafawa waɗanda wannan ibtila’i ya shafa, galibinsu waɗanda s**a rasa muhallansu da dukkanin abin da s**a mallaka.
Rfi

GANYE 24 MEDIA

HOTUNA: Yadda Gwamna Bala Abdulkadir Mohammed (Kauran Bauchi) ya kaddamar da fara aluran riga kafin dabbobi na shekarar ...
15/01/2025

HOTUNA: Yadda Gwamna Bala Abdulkadir Mohammed (Kauran Bauchi) ya kaddamar da fara aluran riga kafin dabbobi na shekarar a garin Itas Gadau.

GANYE 24 MEDIA

SANARWA TA MUSAMMAN Rundunar yan sandan jahar Adamawa, na sanar da al'umma cewa zasu yi atisayin harbin bindiga a babban...
15/01/2025

SANARWA TA MUSAMMAN

Rundunar yan sandan jahar Adamawa, na sanar da al'umma cewa zasu yi atisayin harbin bindiga a babban offishin yan sanda na (CTU) dake kan hanyar Mubi, a karamar hukumar Girei a nan jahar Adamawa.

A tisayin ana saran gudanar dashi ne na yini guda a yau Laraba 15 ga watan Junairu shekarar 2025.

Sabida hakan rundunar take sanar da mazauna yankin, yan kasuwa, masu ababen hawa, manoma da makiyaya da cewa su nesanci wajen.

Sannan ana sanar da al'umma an dauki dukkan matakan kariya kan hakan.

Sanarwa: SP Suleiman Yahaya Nguroje, ANIPR, kakakin rundunar yan sandan jahar Adamawa a madadin Commissioner yan Sanda.

Daga shafin Mubarak Aliyu

GANYE 24 MEDIA

Barka da safiya daga nan Jihar Bayelsa .Jihar Bayelsa jiha ce dake kudu maso kudancin Najeriya, tana nan a tsakiyar yank...
15/01/2025

Barka da safiya daga nan Jihar Bayelsa .

Jihar Bayelsa jiha ce dake kudu maso kudancin Najeriya, tana nan a tsakiyar yankin Niger Delta.
An kirkiri Jihar Bayelsa ne a shekarar alif dubu daya dari Tara da casa'in da shida (1996), kuma an cire ta ne daga Jihar Rivers.
Hakan yasa ta zamo daya daga cikin sabbin jihohin kasar. Ta hada iyaka da Jihar Rivers daga gabas, da kuma Jihar Delta daga yamma, inda Tekun Atalanta ta mamaye yankin kudancin jihar.

Jihar Bayelsa nada fadin fili na kimanin kilomita 10,773kmaq, wanda yasa ta zamo jiha mafi karancin fili a Najeriya.
Kuma tana da yawan jama’a kimanin mutum 2,394,725, (kiyasin shekara ta 2016), wanda ya sanya ta jiha mai mafi karancin mutane. Babban birnin jihar, itace Yenagoa.

Douye Diri ne gwamnan jihar a shekara ta 2022, mataimakin shi kuma shine Lawrence Ewhrudjakpo.
Dattijan jihar sun hada da: Goodluck Jonathan, David Clark, Ben Murray Bruce, Emmanuel Paulker Izibefien da Evan Foster Ogola.

A sanadiyyar kasancewarta a yankin Niger Delta, Jihar Bayelsa mamaye take da kogi da koramu, kuma kusan duka garin cikin ruwa yake, hakan ya jawo rashin cigabanta ta hanyar gina hanyoyi.

Ana amfani da harshen Ijaw a ko ina a jihar, tare da sauran harsuna k**ar Isoko da Urhobo a tsaffin kyaukan jihar.

Daga ina kuke bibiyar GANYE 24 MEDIA

------SASHIN TALLACE-TALLACE------

INA 'YAN KASUWA DA MA'ABOTA BIBIYAR GANYE 24 NESA TAZO KUSA..

Zaku iya aiko mana da tallace-tallacen na kasuwancin ku, Biki ko Aure da sauran su, duk a farashi mai rahusa.

Ko ku aike mana da sakon WhatsApp ta wannan lambar 09121882331

Mun gode, sai mun ji ku💯

Rundunar ‘yan sanda ta Bauchi ta k**a mutum biyu bisa zargin yin luw@di da kananan yara a wurare daban-daban. A Tilden F...
14/01/2025

Rundunar ‘yan sanda ta Bauchi ta k**a mutum biyu bisa zargin yin luw@di da kananan yara a wurare daban-daban.

A Tilden Fulani, an k**a Aminu Musa, mai shekaru 41, bisa zargin yin luw@di da yaro mai shekaru 11, inda ya yaudarashi da kudi da abinci.

Haka zalika, a cikin garin Bauchi, an k**a wani Adamu Abdullahi, mai shekaru 38, da zargin tilasta wa yaro mai shekaru 10 shiga gini ba a kammala ba, tare da aikata wannan mummunan abu. Dukkan wadanda ake zargin sun amsa laifinsu.

Haka kuma, rundunar ta cafke wasu mutum biyu, Abubakar Yakubu da Almustapha Hassan, bisa zargin mallakar bindigu na gida da kuma shiga aikin fashi da makami.

An samu bindigu biyu, mashina biyu, adda, da wasu kayayyaki daga hannunsu.

Sun amsa laifinsu tare da bayyana yadda suke fasa mashina da kayayyaki su sayar.

Rundunar ta yi kira ga al’umma su ci gaba da bayar da hadin kai da rahoton duk wani motsi da basu amince da shi na ga ofishin ‘yan sanda mafi kusa.

DA DUMI DUMI: Tsohon Gwamnan Jihar Sokoto Alh. Attahiru Dalhatu Bafarawa Ya fice Daga Jam'iyyar PDP.
14/01/2025

DA DUMI DUMI: Tsohon Gwamnan Jihar Sokoto Alh. Attahiru Dalhatu Bafarawa Ya fice Daga Jam'iyyar PDP.

TIRKASHI: Wata Bazawara Ta Roki Kotu Da Ta Daura Mata Aure Da Tsohon MasoyintaWata Bazawara mai suna Aisha Zubairu ta ga...
14/01/2025

TIRKASHI: Wata Bazawara Ta Roki Kotu Da Ta Daura Mata Aure Da Tsohon Masoyinta

Wata Bazawara mai suna Aisha Zubairu ta garzaya kotun shari’a da ke Magajin Gari a jihar Kaduna, inda ta nemi kotu ta sa baki ta auri tsohon masoyinta, Aminu Saminu.

Aisha ta kai karar mahaifinta, Zubairu Surajo, inda ta zarge shi da hana ta auren mutumin da ta ke so saboda bacin rai.

Aisha ta shaidawa kotun cewa "Ni wanda a yanzu aka sake ni, kuma ina son kotu ta tabbatar min da hakkina na zaben wanda zan aura." Ta bayyana cewa mahaifinta ya tilasta mata auren da ta yi a baya, wanda yanzu sun rabu da mijin, kuma a yanzu ya ki yarda ta auri tsohon saurayin ta Saminu.

Mahaifinta, wanda lauyansa Nasiru Abdullahi ya wakilta, ya kare matsayinsa, inda ya bayyana rashin mutunta dangin Saminu a baya. Ya bayyana cewa tun farko iyayen Saminu sun ki karrama dangin su.

Sai dai Zubairu bai ce komai ba idan kotu ta yanke hukuncin daurin auren. "Ba mu da wata hujja idan kotu ta dage, amma ba za mu mara mata baya ba sai dai fatan alheri," in ji shi.

Alkalin kotun, Malam Kabir Muhammad, ya dage ci gaba da sauraren karar zuwa ranar 29 ga watan Janairu, sannan ya bukaci a ci gaba da sauraron karar Zubairu Surajo a ci gaba da sauraren karar.

Yammacin yau daliban Sashen Geography na Jami'ar Tarayya ta Kashere sun kai ziyarar ban girma ga HRH Lamido Adamawa Alh....
14/01/2025

Yammacin yau daliban Sashen Geography na Jami'ar Tarayya ta Kashere sun kai ziyarar ban girma ga HRH Lamido Adamawa Alh. Dr. Muhammadu Barkindo (PhD, CFR, shugaban majalisar sarakunan Adamawa.

Daliban sun samu tarba a fadar daga Farfesa Abubakar Abba Tahir (Kakaki Adamawa) da Abubakar Muh'd Bello (Chief Protocol to Lamido), inda s**a zagaya ta dakunan karatu na fadar Lamido domin zurfafa binciken ababen tarihi dake fadar.

Gwamna Ahmadu Umaru Fintiri tare da Kwamishinan ’Yan sandan Jihar Adamawa, CP Moris Dankwanbo, sun yi wa ASP Bello Moham...
14/01/2025

Gwamna Ahmadu Umaru Fintiri tare da Kwamishinan ’Yan sandan Jihar Adamawa, CP Moris Dankwanbo, sun yi wa ASP Bello Mohammed da ke rike da mukamin kwamandan rakiya na Gwamna da ASP Yusuf Abana sabbin muk**ai na mataimakin sufetan Yansanda (DSP).

An gudanar da bikin kawata ne a gidan gwamnati dake Yola.

DA ƊUMI-ƊUMI: Shugabancin Ƙungiyar Kiristoci (CAN) reshen karamar hukumar Michika a jihar Adamawa ta rage kudin da ake k...
14/01/2025

DA ƊUMI-ƊUMI: Shugabancin Ƙungiyar Kiristoci (CAN) reshen karamar hukumar Michika a jihar Adamawa ta rage kudin da ake kaiwa domin neman Aure.

Shugaban Ƙungiyar Rev. Daniel T. Tumba yace sunyi haka ne domin baiwa matasa damar yin Aure a fadin karamar hukumar.

Me Za ku Ce ?

Gwamna Umaru Mohammed Bago ya tallafawa Cibiyar koyar da karatun adabi na BM Dzukogi dake Minna da  Naira Miliyan Hamsin...
14/01/2025

Gwamna Umaru Mohammed Bago ya tallafawa Cibiyar koyar da karatun adabi na BM Dzukogi dake Minna da Naira Miliyan Hamsin.

A wani bikin cikar sa shekaru sittin da ƙaddamar da wasu litattafai daya wallafa, Gwmnan ya yaba masa kan Gundumar sa na habbaƙa ilimi a Neja tare da bada Gudunmawar Naira Miliyan Hamsin.

Wani ÆŠan Kasuwa mai suna Bala Kwatu shima ya bada Gudunmawar Naira Miliyan Goma da dubu Hamsin.

Al'umma da sun halacci taron kuma sun masa fatan alkairi.

Gwamna Ahmadu Umaru Fintiri na jihar Adamawa ya jaddada aniyarsa na samar da zaman lafiya da cigaba a wata ganawa da al'...
14/01/2025

Gwamna Ahmadu Umaru Fintiri na jihar Adamawa ya jaddada aniyarsa na samar da zaman lafiya da cigaba a wata ganawa da al'ummar Lunguda karkashin jagorancin Kwandi Nungurya Kurhaye Dishon Dansanda a fadar gwamnati dake Yola.

Ya bayyana wajabcin zaman lafiya domin samun ci gaba mai ma’ana tare da karfafa gwiwar al’umma da su ci gaba da inganta wadannan dabi’u. Dansanda ya yabawa Gwamna bisa samar da masarautu da masarautu da ke inganta hadin kai da ci gaba, yayin da ya kuma bukaci al’ummar Lunguda su samu wakilci nagari a aikin gwamnati.

Sauran shugabannin al’umma da s**a hada da Cif Ibrahim Wiliye da jami’an yankin sun yaba da ayyukan ci gaban da Gwamnan ya yi a masarautar Lunguda. Taron ya kuma kunshi nunin raye-rayen al'adu.

Nayi Alkawarin yin fito na fito da duk wanda zai ja da Bago ~ Cewar KantikiTsohon Dantakarar Gwamnan Jihar Neja kuma Jig...
14/01/2025

Nayi Alkawarin yin fito na fito da duk wanda zai ja da Bago ~ Cewar Kantiki

Tsohon Dantakarar Gwamnan Jihar Neja kuma Jigo a Jam'iyar PDP Alhaji Isah Liman Kantigi yace ba zai yi takarar kujerar Gwamna ba a zaben 2027.

Kantigi ya bayyana haka ne a lokacin da ya gana da manema labarai a yammacin ranar Litinin da ta gabata, inda yace sun gamsu da salon mulkin Umaru Mohammed Bago sannan ba zai taba lamuntar wani ya fito takara dashi ba.

CIKIN HOTUNA: Yadda Sarki Kano Na 15 Aminu Ado Bayero ya gudanar da zaman fada a ranar Litinin data gabata, bayan zaman ...
14/01/2025

CIKIN HOTUNA: Yadda Sarki Kano Na 15 Aminu Ado Bayero ya gudanar da zaman fada a ranar Litinin data gabata, bayan zaman kotun daukaka kara.

📷 Hoton Kamal Photography

YANZU-YANZU: Za a kara kudin man feturMan Fetur  na iya tsada fiye da yadda ake sayarwa yanzu, kasancewar masu tashoshin...
14/01/2025

YANZU-YANZU: Za a kara kudin man fetur

Man Fetur na iya tsada fiye da yadda ake sayarwa yanzu, kasancewar masu tashoshin mai sun kara farashi da kimanin kaso 4.74 cikin 100.

Wannan karin farashin ya biyo bayan tashin farashin danyen mai a kasuwannin duniya, ciki har da Bonny Light na Najeriya, wanda ya tashi zuwa $80 kowanne ganga a wannan makon daga $73 a makon da ya gabata.

Vanguard ta rawaito cewa tuni wasu tashoshin mai, k**ar Swift Depot, su ka kara farashin lodin man fetur zuwa N950 kan kowacce lita daga N907 kowanne lita. Tashar Wosbab ma ta kara farashinta zuwa N950 daga N909 kowanne lita.

Haka zalika, tashar Sahara ta kara farashin ta zuwa N950 kowanne lita daga N910, yayin da Shellplux ta kara zuwa N960 kowanne lita daga N908 kowanne lita, k**ar yadda Daily Nigeria Hausa ta ruwaito.

KIWON LAFIYA: Najeriya za ta karbi bakuncin taron samar da rigakafin cutar Lassa Fever na kasashen yammacin Afrika.
13/01/2025

KIWON LAFIYA: Najeriya za ta karbi bakuncin taron samar da rigakafin cutar Lassa Fever na kasashen yammacin Afrika.

Address

Ahmadu Bello Way
Ganye

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when GANYE 24 MEDIA posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to GANYE 24 MEDIA:

Videos

Share