AFRIC MEDIA HAUSA

AFRIC MEDIA HAUSA News and media

Kasance tare da Mu👇https://chat.whatsapp.com/JXyxE50PaHr8fbh8VGZQet  💥 Karatu Kyauta & Takardar Shaida Kyauta 💥  Hikaya ...
17/06/2025

Kasance tare da Mu👇
https://chat.whatsapp.com/JXyxE50PaHr8fbh8VGZQet
💥 Karatu Kyauta & Takardar Shaida Kyauta 💥

Hikaya Academy wata cibiya ce ta koyar da ilimin kafafen yada labarai ta yanar gizo, da nufin bai wa al’umma ilimi da ingantaccen horo a fannin aikin jarida da kafafen yada labarai na zamani.

Manufarmu ita ce samar da ilimi mai nagarta, mai jan hankali da kuma fahimta game da fannoni daban-daban na aikin jarida, ciki har da rubuta labarai, bada rahoto, watsa shirye-shirye da sauran dabaru na ilimin kafafen yada labarai na zamani.

Ku kasance tare da mu a koda yaushe domin samun horo na musamman, bitoci da dabaru masu yawa dake da amfani ga ma'abota ilimin aikin jarida.

https://chat.whatsapp.com/JXyxE50PaHr8fbh8VGZQet

Tura wa jama'a don su amfana.

Sakonnin Babbar Sallah  da aka gabatar jiya Juma’a 10 Ga Watan Zhul-Hajj 1446 wanda yayi daida 06 June, 2025 na Kungiyar...
07/06/2025

Sakonnin Babbar Sallah da aka gabatar jiya Juma’a 10 Ga Watan Zhul-Hajj 1446 wanda yayi daida 06 June, 2025 na Kungiyar Jama’atu Izalatil Bidi’a Wa Ikamati Sunnah ta Jihar Katsina

1. GODIYA GA ALLAH:
Muna godiya ga Allah (S.W.A) da ya kawo mu wannan rana ta idin babbar salla ta shekarar 1446/2025. Muna rokon shi da ya karbi ibadun mu, ya sanya mun dace da dukkanin alkahiran da ke cikin ranar Arfah da ta gabata ranar Alhamis

Alhazan da ke cikin aikin hajji muna rokon Allah ya sanya su yi cikin nasara, su gama lafiya ya kuma maida su gida lafiya

2. MUMMUNAR AKIDA:
Kira ga Malamai akan kara maida hankali wajen karantar da alumma musamman abinda ya shafi Akida domin kaucewa fadawa tarkon zindikai masu amfani da sunan Malunta suna 6atar da alummah

Musamman yanzu da aka samu bayyanar masu akidar batanci ga Hadisan Manzon (S.A.W) da sunan Akidar Kur’ani Zalla a wannan Jiha ta mu ta Katsina

Lallai malamai su kara kokari domin yakar wannan mummunar akida domin kubutar da al’ummar mu daga dukkanin wani sharri da ke cikin ta

3. FATTUN LAYYA:
Kamar yadda aka sani cewa duk shekara Kungiyar Jama’atu Izalatil Bidi’a Wa Ikamati Sunnah ta kan neme gudummuwar sadakar fatun layya daga hannun al’ummar musulmai a fadin Najeriya

A saboda haka ne a wannan shekarar 1446/2025 itama muna kira ga al’ummar musulmai da ke fadin wannan Jiha ta mu mai albarka Jihar Katsina da su bada gudummuwar fatun layyarsu ga wannan Kungiya kaman yadda su ka saba domin cigaba da ayyukan alkhairi da wannan ta ke gudanarwa musamman yanzu da ake aikin ginin Jami’ar As-Salam da ke garin Hadejia Jihar Jigawa mallakar Kungiyar

Za’a iya kai gudummuwar fatun a dukkanin masallatan juma’a/ kamsus salawat na Kungiyar da ke fadin Jihar Katsina

Ga wadan da Allah bai ba su damar yin layya baa kwai rasidi na kudi N100, 200 da N500 da za su iya bada ta su gudummuwar da shi domin a hadu cikin lada

4. TSARO:
Muna yaba ma Gwamnatin Jihar Katsina akan yadda ta dauki maganar matsalar tsaro da muhimmanci wanda mun gani a aikace yadda aka dauki ma’aikatan jami’an tsaron cikin gida (C-Watch) har sau biyu duk domin ganin an magance matsalar rashin tsaron. Kuma muna ganin irin kokarin da jami’an ke yi tun lokacin da su ka fara aiki a yan kunan da ake fama da wannan matsala har zuwa yanzu

Dan haka muna kira ga Gwamnati akan kara daukar matakan da duk su ka kamata domin ganin an magance wannan matsala

Haka kuma muna kara kira ga al’umma lallai su ci gaba da bada ta su gudummuwar ga jami’an tsaro da ita kan ta gwamnati wajen ganin an magance matsalar rashin tsaro

5. YAN SIYASA:
Muna kira ga yan siyasar mu musamman wadan da ke akan madafun iko a halin yanzu da su ji tsoron Allah wajen tabbatar da sun sauke nauyin da Allah ya daura masu na al’ummar da su ka zabe su wajen kawo masu ayyukan alkhairi da samar masu abubuwan more rayuwa da dogaro da kai ba wai zuwa ana ba su abinda bai taka kara ya karya ba wanda ko kishirwa ba zai kashe masu ba da sunan tallafi

6. IYAYE:
Muna kira ga iyaye da su ji tsoron Allah wajen sauke nauyin amanar da Allah ya ba su ta yaransu musamman wajen kula da abinda ya shafi tarbiyarsu

Dole ne a sanya idanu akan su yayin da ake hidimar sallah saboda kada su je su na akaita abinda zai janyo fushin Allah. A kwaidatar da su wajen kai ziyarori wajen yan'uwa da abokan arziki da kuma ja masu kunne na kauce ma wajajen da ake haduwa domin sharholiya

7. DOGARO DA KAI:
Wajibi ne alummarmu su maida hankali kan neman ilimin addini da na boko da koyon sanaoin hannu musamman ga matasan mu. Da yin niyyar yin aiki da abinda aka koya din, wannan zai taimaka wajen dogaro da kai da rage zaman banza musamman ga matasan mu

8. TALLAFAWA MASU RAUNI DOMIN RAGE RADADIN HALIN DA AKE CIKI:
Muna kira akan tallafa ma masu rauni daga cikinmu musamman marayu da zawarawa da nakasassu da gajiyayyu don rage masu radadin talauci da tsadar rayuwa da ake fama da ita a wannan lokaci

Kuma tallafawar kada ta tsaya kadai ga abinci ta hade duk wani abu da dan Adam ke bukata

9. IFTILA’IN AMBALIYAR RUWAN SAMA:
Muna amfani da wannan dama domin jajantama al’ummar garin Mokwa na Jihar Niger akan iftila’in ambaliyar ruwan da ya samesu a satin da ya gabata.

Muna rokon Allah ya jikan wanda da su ka rasu, ya ba iyalansu hakurin rashi, wadan da s**a rasa dukiyarsu ko muhallin su ya maida masu da mafi alkhairi ya kuma kare faruwar hakan a gaba

10. KOMA WA GA ALLAH:
Wajibi ne dukkanmu mu koma ga Allah, mu tuba zuwa gare shi musamman cikin wannan yana yi da muke ciki na fargabar rashin tsaro, tsadar rayuwa. Domin babu wata musiba da ke samun mutane sai dalilin abubuwan da s**a aikata da hannuwansu. Don haka kuma, hanya daya wadda za mu bi Allah ya yaye wandannan musibu shine ta hanyar tuba da koma zuwa gareshi

11. ADDUA:
Kira ga Limaman Juma'a da na Khamsus Salawat da wajen darussa akan cigaba da gabatar da addu'o'in zaman lafiya da kuma yana yin da ake ciki, akan Allah ya kawo mana saukin shi ta hanyar da ba mu tsammani

12. Daga karshe muna kira ga Yan Agaji da Yan Hisbah su yi shiri a wannan lokaci dan kaucewa da kuma magance duk wata fitsara da za'a kawo da sunan bukukuwan sallah a fadin wannan Jiha ta mu ta Katsina baki daya

Muna rokon Allah (S.W.A) ya kara mana zaman lafiya da lumana a wannan Jiha ta mu da ma kasa baki daya. Muna rokon ya aza dukkannin ayyukan mu a mizanin ayyukan alkhairiya saka ma kowa da mafificiyar sakayya ta jannatul Firdausi. Amin

Wassalamu Alaikum Wa Rahamatullah Wa Barakatuhu

Yusuf Hassan Buhari
Darakta JIBWIS Social Media
Na Jihar Katsina

Kalli yadda hukumar NAHCON ta samar wa alhazan Najeriya abincin karin kumallo mai inganci wanda kowa ke buƙata👇
01/06/2025

Kalli yadda hukumar NAHCON ta samar wa alhazan Najeriya abincin karin kumallo mai inganci wanda kowa ke buƙata👇

National Hajj Commission of Nigeria

An Bankado Sabon Rikici Tsakanin Manyan Jiga-Jigan Siyasar APC a Katsina!Daga: Hikaya Radio Wani rikici mai É—auke da zaf...
04/05/2025

An Bankado Sabon Rikici Tsakanin Manyan Jiga-Jigan Siyasar APC a Katsina!

Daga: Hikaya Radio

Wani rikici mai ɗauke da zafafan kalamai ya taso tsakanin wani fitaccen ɗan majalisar wakilai daga Musawa/Matazu da Mataimakin Shugaban jam’iyyar APC na jihar Katsina, Bala Abu.

A cikin wani faifan sauti da ɗan majalisar ya ɗauka da kansa, an jiyo shi yana caccakar Bala Abu da zargin cewa akwai matsala a takardun karatunsa. Ya bukaci Bala Abu ya fito fili ya bayyanawa duniya gaskiya, yana mai cewa ba ya buƙatar a ɓoye gaskiya ko a kare wani.

Zazzafar fadar ta kai matakin da É—an majalisar ya furta wasu kalamai masu nauyi da s**a tada kura a tsakanin magoya baya da masu sharhi a kafafen sada zumunta.

Lamarin ya ɗauki hankalin jama’a inda ake ci gaba da sauraron yadda rikicin zai kaya. Muna fatan zaman lafiya da fahimta zai samu a tsakanin su.

Shugaba Tinubu ya halarci É—aurin auren Æ´ar Gwamnan KatsinaShugaban kasar Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya bayar da auren Ai...
03/05/2025

Shugaba Tinubu ya halarci É—aurin auren Æ´ar Gwamnan Katsina

Shugaban kasar Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya bayar da auren Aisha Dikko Umaru Radda, Æ´ar Gwamnan Jihar Katsina Malam Dikko Umaru Radda, ga Ahmed Usman, wani dan asalin masarautar Daura.

Hikaya Newspaper ta ruwaito cewa, taron wanda aka gudanar a Katsina, ya haÉ—a Æ´an siyasa wuri guda, inda ya tattara manyan mutane daga ko'ina a cikin Najeriya.

An gudanar da ɗaurin auren ne bisa tsarin addinin Musulunci, inda Limamin Masallacin Jama'a na Katsina, Malam Mustapha, ya jagoranci addu'a'ar ɗaurin auren tare da Alhaji Amadi Batagarawa, Limamin Masallacin Jumma'a na Modoji kuma tsohon Grand Khadi na Jihar Katsina. An ɗaura auren ne akan sadaki Naira Dubu Ɗari Bakwai ₦700,000, bisa ga abin da Musulunci ya tanadar, tsohon Gwamnan Jihar Bauchi Isa Yuguda ya halarci ɗaurin auren a matsayin Wakili, inda ya karbi auren Amaryar a madadin dangin Angon.

ÆŠaurin auren ya samu halartar manyan shugabannin siyasa, ciki har da Shugaban Majalisar Wakilan Najeriya Hon. Tajudeen Abbas, Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa Senator Barau Jibrin, da Shugaban Jam'iyyar APC Dr. Abdullahi Ganduje. Gwamnonin jihohi da dama, irin su Abdulrahman Abdulrazaq na Kwara da Babagana Zulum na Borno, sun halarci bikin.

📸 Hikaya Newspaper

Da Dumi-Dumi: Kalli wata zazzafar waka da Rarara ya sake yi wa Gwamna Radda na jihar Katsina.👇
13/04/2025

Da Dumi-Dumi: Kalli wata zazzafar waka da Rarara ya sake yi wa Gwamna Radda na jihar Katsina.👇

Ku yi subscribe na HIKAYA TV 08102933059

"Mun gamsu da hukuncin SDP na kin amincewa da ruguza shugabancinta domin gina sabo. Yin hakan zai iya kawo cikas ga yunk...
12/04/2025

"Mun gamsu da hukuncin SDP na kin amincewa da ruguza shugabancinta domin gina sabo. Yin hakan zai iya kawo cikas ga yunkurinta na samar da shugabanci nagari a Najeriya" - Aliyu Maiwada Masanawa.👇

Alhaji Aliyu Maiwada Masanawa, mataimakin shugaban jam'iyyar SDP na shiyyar Katsina ta tsakiya a jihar Katsina, Najeriya.

MAN OF THE PEOPLE.( KWACHAM) Abdurrahman Buba Kwacham is a prominent Nigerian businessman, politician, and philanthropis...
02/03/2025

MAN OF THE PEOPLE.

( KWACHAM)

Abdurrahman Buba Kwacham is a prominent Nigerian businessman, politician, and philanthropist from Adamawa State.

Business Ventures

Kwacham has established himself as a successful businessman, engaging in various commercial activities that have contributed to the economic development of Adamawa State. His business acumen has earned him recognition and respect within the community.

Philanthropy

Demonstrating a strong commitment to philanthropy, Kwacham has been involved in numerous charitable endeavors. Notably, he donated vehicles to 19 different organizations, showcasing his dedication to supporting local communities and initiatives.

In recognition of his exceptional humanitarian efforts, Wisdom University African Campus recently honored Kwacham with a doctorate degree. This accolade highlights his significant contributions to society and his unwavering commitment to improving the lives of others.

Political Career

Kwacham has been actively involved in Nigerian politics, particularly within Adamawa State:

PDP Membership and Departure: He was a member of the People's Democratic Party (PDP) but left the party due to perceived injustices. He publicly cited a lack of fairness as his reason for departing.

2023 Senatorial Ambitions: Following his departure from the PDP, Kwacham announced his intention to run for the Senate seat representing Adamawa North in the 2023 elections. His campaign emphasized his readiness and capacity to serve the people of Adamawa North.

Community Engagement

Kwacham has held leadership positions in various organizations, reflecting his dedication to community development. He served as the Chairman of the Movement for Northeast Youth Organizations Forum, where he worked to empower youth and address regional challenges.

Through his diverse roles as a businessman, philanthropist, and politician, Abdurrahman Buba Kwacham has made significant contributions to the socio-economic and political landscape of Adamawa State.

Kalli bidiyon yadda aka yi harbe-harbe a yayin da EFCC s**a kewaye gidan Gwamnan Kogi suna neman Yahaya Bello a Abuja👇
19/09/2024

Kalli bidiyon yadda aka yi harbe-harbe a yayin da EFCC s**a kewaye gidan Gwamnan Kogi suna neman Yahaya Bello a Abuja👇

Ku yi SUBSCRIBE na HIKAYA TV 08102933059

PDP ONE FAMILY ta yi zazzafan martani ga Cif Olabode dake ƙalubalantar Atiku Abubakar a kakar siyasa ta 2027 mai zuwa  W...
06/09/2024

PDP ONE FAMILY ta yi zazzafan martani ga Cif Olabode dake ƙalubalantar Atiku Abubakar a kakar siyasa ta 2027 mai zuwa

Wani mai fafutukar siyasa daga ƙaramar hukumar Dala ta jihar Kano, kuma shugaban ƙungiyar 'PDP ONE FAMILY' na ƙasa, Hon. Abdulrahman Mainasara, ya mayar da zazzafan martani kan wata s**ar da wani jigo a jam’iyyar PDP, Cif Olabode George ya yi, inda Mainasara ya kare mutuncin Atiku Abubakar da halayensa na shugabanci. Mainasara ya bayyana yadda Atiku zai iya ceto Najeriya daga ƙalubalen da take fuskanta na mulkin jam’iyyar APC.

Mainasara ya kuma soki kiraye-kirayen da Cif Bode George ya yi na neman ɗan takarar shugaban ƙasa a kudancin ƙasar, inda ya ba da misali kan yadda ƴan kudu s**a shugabanci jam’iyyar PDP a baya, mutanen da ya ayyana sun haɗa da Obasanjo da Jonathan. Ya kuma jaddada ƙwarewar Atiku a shugabanci a matsayin muhimmin abinda zai ciyar da Najeriya gaba.

Shugaban ƙungiyar ta ‘PDP ONE FAMILY’ na ƙasa, Abdulrahman Mainasara, ya jaddada buƙatar samun shugaban da zai samar da haɗin kan ƙasa a zaɓen 2027 mai zuwa, inda ya nuna gazawar gwamnatin APC mai ci a yanzu. Ya kuma nuna ƙwarin gwiwa kan yadda Atiku zai iya kawo kyakkyawan sauyi ga tattalin arzikin Najeriya, inganta tsaro, da inganta ababen more rayuwa.

Hon. Mainasara ya kuma buƙaci Cif Bode George da sauran su da su goyi bayan takarar Atiku Abubakar, inda ya bayyana cewa Atiku yana da dabarun da zai jagoranci Najeriya zuwa ga tudun mun tsira da kuma tunkarar ƙalubalen zamantakewa da tattalin arziki da siyasar ƙasar.

Ana dai kallon Atiku Abubakar a matsayin ɗan takara mai kimar da zai iya kifar da Gwamnatin shugaban ƙasa Bola Tinubu na jam’iyyar APC a zaben 2027, inda Mainasara ya bayyana yadda Atiku zai iya kawo sauyi mai kyau da ci gaban tattalin arziki a Najeriya.

Kiran a baiwa Atiku Abubakar haɗin kai ya zo ne a daidai lokacin da ake ci gaba da nuna damuwa kan halin da al’ummar ƙasar ke ciki da kuma buƙatar samar da ingantaccen shugabanci don magance matsalolin da ke addabar Najeriya.

Ayyanawar da Hon. Mainasara ya yi wa Atiku Abubakar a matsayin zaɓin Jama’a ya nuna salon da jam’iyyar 'PDP ONE FAMILY' ta ɗauka na ƙarawa Atiku ƙaimi a matsayin babban jigo mai iya kai Nijeriya ga ci gaba mai ɗorewa.

Sanarwar da Hon. Mainasara ya fitar ta ƙara jaddada mahimmancin cikakken hangen nesa kan makomar Najeriya, inda ake sa ran Atiku Abubakar zai sake fitowa takara a zaɓen 2027, duk da kasancewarsa a matsayin wani jigo a babbar jam'iyar adawa ta PDP.

"A yayin da al’amuran siyasa ke ƙara tabarbarewa, mayar da hankali kan takarar Atiku Abubakar na nuni da cewa an samu sauyi ga tsarin haɗin kai da dabaru a cikin PDP ONE FAMILY, da zummar ganin an samu ƙwaƙƙwaran matsayi a takarar shugaban ƙasa mai zuwa," in ji Hon. Mainasara.

19/08/2024

KATSINAWA NA GODIYA! Fitaccen alaramman nan ɗan asalin jihar Kebbi a Najeriya, Alaramma Mustafa Shu'aibu Argungu, ya GwanGwaje al'ummar jihar Katsina da addu'o'i a sakamakon matsalar tsaro dake addabar wasu daga cikin ƙananan hukumomin ta.

AYI SAURARO LAFIYA👇

KHUƊBAR SALLAR JUMA'A         🕋🕋🕋🕋🕋🕋Tare da: Sheikh. Lawal Musa JibiaMAUDU'I: Kame Zuciya da Yiwa Shugabanni Addu'a👇http...
16/08/2024

KHUÆŠBAR SALLAR JUMA'A
🕋🕋🕋🕋🕋🕋

Tare da: Sheikh. Lawal Musa Jibia

MAUDU'I: Kame Zuciya da Yiwa Shugabanni Addu'a👇
https://darulfikr.com/s/190115

AYI SAURARO LAFIYA
🎧🎧🎧🎧🎧

Kasance da darulfikr.com domin samu karatuttukan maluman sunnah a sauƙaƙe.

Abdulrazak Ahmad Jibia
JIBWIS Social Media
+2348102933059

Darulfikr.com is an Islamic website that provides a comprehensive resource for Muslims to deepen their understanding of Islam. It focuses on promoting the values of Islam and spreading the message of peace, love, and unity.

Address

Garki

Telephone

+2348069578288

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when AFRIC MEDIA HAUSA posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to AFRIC MEDIA HAUSA:

Share