AFRIC MEDIA HAUSA

AFRIC MEDIA HAUSA News and media

13/10/2025

Celebrating my 4th year on Facebook. Thank you for your continuing support. I could never have made it without you. 🙏🤗🎉

Kamfanin Credit Direct ya tallafawa ma'aikata 100 a KatsinaYayin da ake bikin makon hidimtawa abokan hulɗa na shekarar 2...
13/10/2025

Kamfanin Credit Direct ya tallafawa ma'aikata 100 a Katsina

Yayin da ake bikin makon hidimtawa abokan hulɗa na shekarar 2025, kamfanin Credit Direct mai zaman kansa ya raba tallafin wasu kayayyaki na musamman ga ma’aikatan gwamnati 100 a jihar Katsina.

Kamfanin Credit Direct Limited, wanda reshe ne na First City Monument Bank, wato (FCMB), ya raba jikkuna 100 da ke ɗauke da wasu kayayyakin amfanin yau da kullum ga ma’aikatan gwamnati da ke hulɗa da FCMB a jihar Katsina.

Jaridar Hikaya ta ruwaito cewa an gudanar da wannan shiri ne a ranar Alhamis, 9 ga watan Oktoba, 2025, domin nuna jajircewar kamfanin wajen nuna godiya ga abokan hulɗa da kuma ƙarfafa alaƙar zumunci ta hanyar ayyukan ci gaban al’umma masu tasiri.

An gudanar da bikin a Ofishin Credit Direct Limited da ke cikin bankin FCMB a Katsina, inda aka raba kayan abinci da na amfanin yau da kullum ga ma’aikatan gwamnati daga sassa daban-daban na ma’aikatu. An bayyana taron da nufin ƙarfafa zumunci, nuna godiya, da kuma haɓaka jin daɗin abokan hulɗar da s**a kasance masu aminci ga kamfanin tsawon shekaru.

A yayin da yake jawabi, Musa Ayuba, wakilin kamfanin Credit Direct Limited a jihar Katsina, ya bayyana cewa wannan tallafi na cikin shirin alhakin jama’a, wato (Corporate Social Responsibility - CSR) na kamfanin domin nuna godiya ga abokan hulɗa da kuma tallafa wa al’umma. Ya ce kamfanin na ɗaukar ma’aikatan gwamnati a matsayin abokan ci gaba kuma zai ci gaba da tallafa musu ta hanyar samar da lamuni mai sauƙi da shirye-shiryen ƙarfafa tattalin arziki.

Ayuba ya ƙara tunatar da cewa a watan Disamba 2024, kamfanin ya raba kayan abinci ga fiye da mutane 200 waɗanda s**a tsinci kansu cikin matsin rayuwa sakamakon hare-haren ‘yan bindiga da kuma waɗanda s**a rasa matsuguni (IDPs) a fadin jihar Katsina. Ya ƙara da cewa wannan ya nuna irin tausayi da jajircewar kamfanin wajen rage wahala da kawo sauƙi ga al’umma, inda ya ƙara da cewa hangen kamfanin a fannin CSR ba ya tsaya kan harkar kasuwanci kaɗai ba, sai da tasirin zamantakewa da ƙarfafa zumunci a tsakanin al’umma.

Shi ma Alhaji Mannir Lawal, Darakta na Sashen Gudanarwa da Kayan Aiki a Ofishin Babban Sakataren Ma’aikata, ya yaba wa kamfanin bisa irin tallafin da yake bai wa ma’aikata lokaci zuwa lokaci. Ya bayyana Credit Direct Limited a matsayin kamfani mai gaskiya da amana, wanda ke da kyakkyawar niyya ga walwalar abokan hulɗarsa. Ya kuma yi kira ga sauran kamfanoni da su kwaikwayi irin wannan aiki na alheri, yana mai cewa gwamnati kaɗai ba za ta iya ɗaukar nauyin walwalar jama’a ba.

A nasa bangaren, Alhaji Abdurrahman Lawal, Darakta na Sashen Kula da Bashi, ya jinjinawa kamfanin bisa nuna damuwa da bukatun ma’aikatan gwamnati, musamman a wannan lokaci da ake fuskantar ƙalubalen tattalin arziki. Ya bayyana cewa wannan tallafi zai ƙara wa ma’aikata kwarin gwiwa da ƙaunar aiki, tare da ƙarfafa su wajen inganta ayyukan gwamnati.

An kammala taron da mika kayan tallafin ga ma’aikata da kuma ɗaukar hotuna, inda jami’an gwamnati da ma’aikata s**a nuna godiyarsu ga kamfanin Credit Direct Limited bisa gaskiya, jajircewa da kyautata hulɗa da al’umma.

Gwamnatin Katsina ta horas da malaman gona 756 kan dabarun kiwon dabbobiGwamnatin Jihar Katsina ta gudanar da horo na kw...
19/08/2025

Gwamnatin Katsina ta horas da malaman gona 756 kan dabarun kiwon dabbobi

Gwamnatin Jihar Katsina ta gudanar da horo na kwana ɗaya ga Malaman Gona 756 da kuma Jami’an Cigaban Al’umma (CDO’s) a fannoni na dabarun kiwon dabbobi na zamani da kuma buƙatar shawarwari na musamman don samun nasarar kiwo a jihar. Taron ya gudana ne a dakin taro na Sakatariyar Jihar Katsina a ranar Litinin 18 ga watan Agusta, 2025.

A yayin taron, Mai Ba Gwamna Shawara kan Harkokin Kiwon Dabbobi da Gandun Daji, Hon. Yusuf Suleiman Jibia, ya bayyana cewa manufar shirin ita ce wayar da kan mahalarta kan hanyoyin zamani da ake amfani da su a fannin kiwon dabbobi a duniya. Ya ce gwamnatin Dikko Radda ta himmatu wajen inganta kiwon dabbobi, ciki har da rarraba ingantattun awaki ga mata da al’ummomi, aiwatar da rigakafin dabbobi lokaci zuwa lokaci, da kuma gina wuraren kiwo na zamani.

Shugaban Hukumar Bunƙasa Ayyukan Gona ta Jihar Katsina (KTARDA), Alhaji Abubakar Dabo, ya bayyana cewa kasancewar Gwamna Dikko Radda ƙwararre ne a fannin noma ya zama abin alfahari da kuma ci gaba ga jihar. Ya ce kafin zuwan Radda, jihar Katsina ba ta da Malaman Gona fiye da 100, amma yanzu gwamnatin ta ɗauki sama da 700 domin tabbatar da ci gaban noma a kananan hukumomi 34 na jihar.

Shi ma a nasa jawabin, Shugaban Shirin Cigaban Al’umma (CDP), Dr. Kamala Kabir, ya bayyana Malaman Gona a matsayin muhimman abokan tafiya wajen cimma nasarar shirin CDP. Ya buƙace su da su haɗa kai da Jami’an Cigaban Al’umma (CDOs) domin tabbatar da manufar ci gaba da ake son cimmawa.

Rahoton Nigerian Post ya nuna cewa an fara gudanar da irin wannan horo a birnin Katsina, inda mahalarta s**a fito daga kananan hukumomi 11 da ke karkashin yankin Katsina ta tsakiya, sannan za a ci gaba da gudanar da shi a sauran manyan yankuna biyu na jihar.

29/06/2025

Kuna da burin zama ƙwararrun masu aikin jinya ko ungozoma?

To wannan dama ce ta tabbata gare ku! Domin kuwa Kwalejin koyar da ilimin aikin jinya da ungozoma ta CHERISH da ke cikin garin Katsina tana sanar da masu sha’awar wannan fanni zuwa makarantar don samun horo mai inganci da nagarta.

Makarantar na ba da cikakken ilimi da horo na musamman ta hanyar amfani da kayan zamani na gani da ido, domin tabbatar da cewa dalibai sun kware sosai a aikin jinya da na ungozoma.

Don samun gurbin karatu, ana bukatar kiredit biyar daga cikin darussa da s**a haɗa da: Turanci, Lissafi, Biology, Chemistry, da Physics daga jarabawar WAEC ko NECO – kuma ana yarda a haɗa su domin ware kiredit din biyar, amma ba a amince da haɗin WAEC ko NECO da sakamakon NABTEB ko NBAIS ba. Haka kuma, "ba a bada lamunin jiran a kawo sakamakon da bai fito ba."

Daliban da ke son gurbin karatun, yana da kyau su tanadi takardun da s**a hada da: fasfo guda biyu, takardar haihuwa, takardar shaidar zama ɗan asalin ƙaramar hukuma, da sakamakon kammala makarantar sakandare.

Zaɓi Cherish a matsayin zabin farko yayin rajistar JAMB, ko kuma ku koma cibiyar rajistarku domin yin sauyi. Kada ku bari a ba ku labari!

Don karin bayani, za ku iya tuntubar:
07067707512, 08036600220, 08038355918, ko 08036859423.

Kwalejin koyar da ilimin aikin jinya da ungozoma ta Cherish dake Katsina – Gata ce ta kwararrun masu aikin lafiya!

Kasance tare da Mu👇https://chat.whatsapp.com/JXyxE50PaHr8fbh8VGZQet  💥 Karatu Kyauta & Takardar Shaida Kyauta 💥  Hikaya ...
17/06/2025

Kasance tare da Mu👇
https://chat.whatsapp.com/JXyxE50PaHr8fbh8VGZQet
💥 Karatu Kyauta & Takardar Shaida Kyauta 💥

Hikaya Academy wata cibiya ce ta koyar da ilimin kafafen yada labarai ta yanar gizo, da nufin bai wa al’umma ilimi da ingantaccen horo a fannin aikin jarida da kafafen yada labarai na zamani.

Manufarmu ita ce samar da ilimi mai nagarta, mai jan hankali da kuma fahimta game da fannoni daban-daban na aikin jarida, ciki har da rubuta labarai, bada rahoto, watsa shirye-shirye da sauran dabaru na ilimin kafafen yada labarai na zamani.

Ku kasance tare da mu a koda yaushe domin samun horo na musamman, bitoci da dabaru masu yawa dake da amfani ga ma'abota ilimin aikin jarida.

https://chat.whatsapp.com/JXyxE50PaHr8fbh8VGZQet

Tura wa jama'a don su amfana.

Sakonnin Babbar Sallah  da aka gabatar jiya Juma’a 10 Ga Watan Zhul-Hajj 1446 wanda yayi daida 06 June, 2025 na Kungiyar...
07/06/2025

Sakonnin Babbar Sallah da aka gabatar jiya Juma’a 10 Ga Watan Zhul-Hajj 1446 wanda yayi daida 06 June, 2025 na Kungiyar Jama’atu Izalatil Bidi’a Wa Ikamati Sunnah ta Jihar Katsina

1. GODIYA GA ALLAH:
Muna godiya ga Allah (S.W.A) da ya kawo mu wannan rana ta idin babbar salla ta shekarar 1446/2025. Muna rokon shi da ya karbi ibadun mu, ya sanya mun dace da dukkanin alkahiran da ke cikin ranar Arfah da ta gabata ranar Alhamis

Alhazan da ke cikin aikin hajji muna rokon Allah ya sanya su yi cikin nasara, su gama lafiya ya kuma maida su gida lafiya

2. MUMMUNAR AKIDA:
Kira ga Malamai akan kara maida hankali wajen karantar da alumma musamman abinda ya shafi Akida domin kaucewa fadawa tarkon zindikai masu amfani da sunan Malunta suna 6atar da alummah

Musamman yanzu da aka samu bayyanar masu akidar batanci ga Hadisan Manzon (S.A.W) da sunan Akidar Kur’ani Zalla a wannan Jiha ta mu ta Katsina

Lallai malamai su kara kokari domin yakar wannan mummunar akida domin kubutar da al’ummar mu daga dukkanin wani sharri da ke cikin ta

3. FATTUN LAYYA:
Kamar yadda aka sani cewa duk shekara Kungiyar Jama’atu Izalatil Bidi’a Wa Ikamati Sunnah ta kan neme gudummuwar sadakar fatun layya daga hannun al’ummar musulmai a fadin Najeriya

A saboda haka ne a wannan shekarar 1446/2025 itama muna kira ga al’ummar musulmai da ke fadin wannan Jiha ta mu mai albarka Jihar Katsina da su bada gudummuwar fatun layyarsu ga wannan Kungiya kaman yadda su ka saba domin cigaba da ayyukan alkhairi da wannan ta ke gudanarwa musamman yanzu da ake aikin ginin Jami’ar As-Salam da ke garin Hadejia Jihar Jigawa mallakar Kungiyar

Za’a iya kai gudummuwar fatun a dukkanin masallatan juma’a/ kamsus salawat na Kungiyar da ke fadin Jihar Katsina

Ga wadan da Allah bai ba su damar yin layya baa kwai rasidi na kudi N100, 200 da N500 da za su iya bada ta su gudummuwar da shi domin a hadu cikin lada

4. TSARO:
Muna yaba ma Gwamnatin Jihar Katsina akan yadda ta dauki maganar matsalar tsaro da muhimmanci wanda mun gani a aikace yadda aka dauki ma’aikatan jami’an tsaron cikin gida (C-Watch) har sau biyu duk domin ganin an magance matsalar rashin tsaron. Kuma muna ganin irin kokarin da jami’an ke yi tun lokacin da su ka fara aiki a yan kunan da ake fama da wannan matsala har zuwa yanzu

Dan haka muna kira ga Gwamnati akan kara daukar matakan da duk su ka kamata domin ganin an magance wannan matsala

Haka kuma muna kara kira ga al’umma lallai su ci gaba da bada ta su gudummuwar ga jami’an tsaro da ita kan ta gwamnati wajen ganin an magance matsalar rashin tsaro

5. YAN SIYASA:
Muna kira ga yan siyasar mu musamman wadan da ke akan madafun iko a halin yanzu da su ji tsoron Allah wajen tabbatar da sun sauke nauyin da Allah ya daura masu na al’ummar da su ka zabe su wajen kawo masu ayyukan alkhairi da samar masu abubuwan more rayuwa da dogaro da kai ba wai zuwa ana ba su abinda bai taka kara ya karya ba wanda ko kishirwa ba zai kashe masu ba da sunan tallafi

6. IYAYE:
Muna kira ga iyaye da su ji tsoron Allah wajen sauke nauyin amanar da Allah ya ba su ta yaransu musamman wajen kula da abinda ya shafi tarbiyarsu

Dole ne a sanya idanu akan su yayin da ake hidimar sallah saboda kada su je su na akaita abinda zai janyo fushin Allah. A kwaidatar da su wajen kai ziyarori wajen yan'uwa da abokan arziki da kuma ja masu kunne na kauce ma wajajen da ake haduwa domin sharholiya

7. DOGARO DA KAI:
Wajibi ne alummarmu su maida hankali kan neman ilimin addini da na boko da koyon sanaoin hannu musamman ga matasan mu. Da yin niyyar yin aiki da abinda aka koya din, wannan zai taimaka wajen dogaro da kai da rage zaman banza musamman ga matasan mu

8. TALLAFAWA MASU RAUNI DOMIN RAGE RADADIN HALIN DA AKE CIKI:
Muna kira akan tallafa ma masu rauni daga cikinmu musamman marayu da zawarawa da nakasassu da gajiyayyu don rage masu radadin talauci da tsadar rayuwa da ake fama da ita a wannan lokaci

Kuma tallafawar kada ta tsaya kadai ga abinci ta hade duk wani abu da dan Adam ke bukata

9. IFTILA’IN AMBALIYAR RUWAN SAMA:
Muna amfani da wannan dama domin jajantama al’ummar garin Mokwa na Jihar Niger akan iftila’in ambaliyar ruwan da ya samesu a satin da ya gabata.

Muna rokon Allah ya jikan wanda da su ka rasu, ya ba iyalansu hakurin rashi, wadan da s**a rasa dukiyarsu ko muhallin su ya maida masu da mafi alkhairi ya kuma kare faruwar hakan a gaba

10. KOMA WA GA ALLAH:
Wajibi ne dukkanmu mu koma ga Allah, mu tuba zuwa gare shi musamman cikin wannan yana yi da muke ciki na fargabar rashin tsaro, tsadar rayuwa. Domin babu wata musiba da ke samun mutane sai dalilin abubuwan da s**a aikata da hannuwansu. Don haka kuma, hanya daya wadda za mu bi Allah ya yaye wandannan musibu shine ta hanyar tuba da koma zuwa gareshi

11. ADDUA:
Kira ga Limaman Juma'a da na Khamsus Salawat da wajen darussa akan cigaba da gabatar da addu'o'in zaman lafiya da kuma yana yin da ake ciki, akan Allah ya kawo mana saukin shi ta hanyar da ba mu tsammani

12. Daga karshe muna kira ga Yan Agaji da Yan Hisbah su yi shiri a wannan lokaci dan kaucewa da kuma magance duk wata fitsara da za'a kawo da sunan bukukuwan sallah a fadin wannan Jiha ta mu ta Katsina baki daya

Muna rokon Allah (S.W.A) ya kara mana zaman lafiya da lumana a wannan Jiha ta mu da ma kasa baki daya. Muna rokon ya aza dukkannin ayyukan mu a mizanin ayyukan alkhairiya saka ma kowa da mafificiyar sakayya ta jannatul Firdausi. Amin

Wassalamu Alaikum Wa Rahamatullah Wa Barakatuhu

Yusuf Hassan Buhari
Darakta JIBWIS Social Media
Na Jihar Katsina

Kalli yadda hukumar NAHCON ta samar wa alhazan Najeriya abincin karin kumallo mai inganci wanda kowa ke buƙata👇
01/06/2025

Kalli yadda hukumar NAHCON ta samar wa alhazan Najeriya abincin karin kumallo mai inganci wanda kowa ke buƙata👇

National Hajj Commission of Nigeria

An Bankado Sabon Rikici Tsakanin Manyan Jiga-Jigan Siyasar APC a Katsina!Daga: Hikaya Radio Wani rikici mai ɗauke da zaf...
04/05/2025

An Bankado Sabon Rikici Tsakanin Manyan Jiga-Jigan Siyasar APC a Katsina!

Daga: Hikaya Radio

Wani rikici mai ɗauke da zafafan kalamai ya taso tsakanin wani fitaccen ɗan majalisar wakilai daga Musawa/Matazu da Mataimakin Shugaban jam’iyyar APC na jihar Katsina, Bala Abu.

A cikin wani faifan sauti da ɗan majalisar ya ɗauka da kansa, an jiyo shi yana caccakar Bala Abu da zargin cewa akwai matsala a takardun karatunsa. Ya bukaci Bala Abu ya fito fili ya bayyanawa duniya gaskiya, yana mai cewa ba ya buƙatar a ɓoye gaskiya ko a kare wani.

Zazzafar fadar ta kai matakin da ɗan majalisar ya furta wasu kalamai masu nauyi da s**a tada kura a tsakanin magoya baya da masu sharhi a kafafen sada zumunta.

Lamarin ya ɗauki hankalin jama’a inda ake ci gaba da sauraron yadda rikicin zai kaya. Muna fatan zaman lafiya da fahimta zai samu a tsakanin su.

Shugaba Tinubu ya halarci ɗaurin auren ƴar Gwamnan KatsinaShugaban kasar Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya bayar da auren Ai...
03/05/2025

Shugaba Tinubu ya halarci ɗaurin auren ƴar Gwamnan Katsina

Shugaban kasar Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya bayar da auren Aisha Dikko Umaru Radda, ƴar Gwamnan Jihar Katsina Malam Dikko Umaru Radda, ga Ahmed Usman, wani dan asalin masarautar Daura.

Hikaya Newspaper ta ruwaito cewa, taron wanda aka gudanar a Katsina, ya haɗa ƴan siyasa wuri guda, inda ya tattara manyan mutane daga ko'ina a cikin Najeriya.

An gudanar da ɗaurin auren ne bisa tsarin addinin Musulunci, inda Limamin Masallacin Jama'a na Katsina, Malam Mustapha, ya jagoranci addu'a'ar ɗaurin auren tare da Alhaji Amadi Batagarawa, Limamin Masallacin Jumma'a na Modoji kuma tsohon Grand Khadi na Jihar Katsina. An ɗaura auren ne akan sadaki Naira Dubu Ɗari Bakwai ₦700,000, bisa ga abin da Musulunci ya tanadar, tsohon Gwamnan Jihar Bauchi Isa Yuguda ya halarci ɗaurin auren a matsayin Wakili, inda ya karbi auren Amaryar a madadin dangin Angon.

Ɗaurin auren ya samu halartar manyan shugabannin siyasa, ciki har da Shugaban Majalisar Wakilan Najeriya Hon. Tajudeen Abbas, Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa Senator Barau Jibrin, da Shugaban Jam'iyyar APC Dr. Abdullahi Ganduje. Gwamnonin jihohi da dama, irin su Abdulrahman Abdulrazaq na Kwara da Babagana Zulum na Borno, sun halarci bikin.

📸 Hikaya Newspaper

Da Dumi-Dumi: Kalli wata zazzafar waka da Rarara ya sake yi wa Gwamna Radda na jihar Katsina.👇
13/04/2025

Da Dumi-Dumi: Kalli wata zazzafar waka da Rarara ya sake yi wa Gwamna Radda na jihar Katsina.👇

Ku yi subscribe na HIKAYA TV 08102933059

Address

Garki

Telephone

+2348069578288

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when AFRIC MEDIA HAUSA posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to AFRIC MEDIA HAUSA:

Share