FBC

FBC Welcome to Fact Broadcasting Company's (FBC) page – We are "The Voice of the Voiceless"

Governor Radda Visits Injured CWC Security Officers at FMC KatsinaEarlier this evening, Governor Dikko Umaru Radda paid ...
25/05/2025

Governor Radda Visits Injured CWC Security Officers at FMC Katsina

Earlier this evening, Governor Dikko Umaru Radda paid a visit to the Federal Medical Centre in Katsina, where he checked on members of the Community Watch Corps who were injured during a bandit attack in Marhaba village, Matazu Local Government Area. He also took time to greet other patients, offering comforting words and prayers for their recovery.

Governor Radda reassured the wounded officers of the government’s full support and commended their courage in the line of duty. “Your sacrifice will never be forgotten,” he told them.

Accompanying the governor were Alhaji Kabiru Bature Sarkin Alhazai, Chairman of the Katsina State Pilgrims Welfare Board; Sarkin Kuraye, Alhaji Usman Darda’u; several district heads; and the Special Adviser on Security and Community Watch, Alhaji Yusuf Ibrahim Safana, who led the hospital tour.

This visit underscores Governor Radda commitment to the safety and well-being of both the people of Katsina and the brave individuals who defend them.

A SAKE FASALIN MASARAUTAR KATSINA BISA HUJJAR TARIHI DA CANCANTADaga Wakilan Katsina TimesJaridun Katsina Times sun samu...
11/05/2025

A SAKE FASALIN MASARAUTAR KATSINA BISA HUJJAR TARIHI DA CANCANTA

Daga Wakilan Katsina Times

Jaridun Katsina Times sun samu wata takarda da za a gabatar wa Majalisar dokokin jihar Katsina, wadda take bukatar a canza fasalin masarautar Katsina da samar mata wasu Sarakuna masu daraja ta daya, sai mai daraja ta biyu, sai mai daraja ta uku a bisa hujjar tarihi da kuma cancanta.

Takardar, wadda ta kawo hujjar cewa zamani, kuma lokaci ya yi da za a dauko littafin tarihi a duba wanda zai tabbatar cewa zaman girman Katsina mai Sarki daya tilo da daraja ta daya ya wuce.

Takardar ta kara da cewa, a tarihi gidaje uku s**a amso tuta wajen Mujaddadi Shehu Usman Dan Fodio. Sune Malam Ummarun Dallaje (Allah ya yarda da shi), Malam Muhammudu Na Alhaji (Allah ya yarda da shi) da Malam Ummarun Dunyawa (Allah ya yarda da shi).

Tarihi ya nuna cewa, dukkanin su suna da kasa da s**a rika mulkin ta bayan jihadi, kuma dukkanin su sun rika amsar umurninsu kai tsaye daga Sarkin Musulmi ne, ba Sarkin Katsina ba. Sun rika tafiyar da mulkin Katsina a hadaka, yayin da kowanne yana tafiyar da kasar sa. Zuwan Turawa ya kaskantar da su zuwa masu biyayya ga Sarki daya.

Takardar ta ce, lokaci ya yi da wàdannan gidajen za a mayar masu da martabarsu ta cikakkiyar sarauta, k**ar yadda yake a tarihi. A nan s**a ba da shawarar a ba daya daga cikin su Sarki mai daraja ta daya, sauran biyun a ba su masu daraja ta biyu.

Takardar ta ce, Tarihi ya tabbatar da kasar Kurfi ba ta a cikin daular Katsina. Kasa ce mai zaman kanta, wadda ta rika amsar umurni daga wajen Sarkin musulmi. Har zuwan Turawa ba su taba ’yancinta ba, sai daga baya. Kasar Kurfi a duba matsayinta a tarihi, a ba su Sarki ko mai daraja ta biyu ko daraja ta uku.

Tarkardar ta kara da cewa, kasar Maska, Sarkin da ya kafa ta, Sarkin Maska Bako ya yi zamani da Sarkin Katsina Muhammadu Korau. Kasa ce mai tsohon tarihi, kusan daidai da kasar Katsina. Ya k**ata a duba tarihinta da kuma cancantar ta, a ba ta Sarki mai daraja ta daya.

Marubutan s**a kara da cewa, tarihi ya tabbatar da cewa Gwamnan Nijeriya na Turawan mulkin-mallaka Lugard ya taba ba Sarkin Dank**a, Kaura Amah sarautar Sarki mai daraja ta uku, amma Kaura Amah ya ki amsa. Ya ce shi Kaura ne, kuma jarumi, don haka a bar shi karkashin Sarkin Katsina. Marubutan s**a ce ya k**ata a mayarwa da kasar Dank**a wannan darajar da aka taba ba su na Sarki mai daraja ta uku.

Takardar ta kara da cewa, rawar da Malam Dudi na zuri’ar Danejawa ya taka a wajen kafa kasar, wadanda yanzu sune ke sarauta a yankin Malumfashi da Kafur sun cancanta a yi masu sarauta mai daraja ta biyu.

Marubutan s**a ce, duk wadannan abubuwan da s**a bayyana a sama suna nan a littattafan tarihi, ba shaci-fadi bane.

S**a kara da cewa, duk Najeriya ba wata masarauta mai girma k**ar Katsina da take da Sarki daya, mai daraja ta daya, shi daya.

Jihohi suna duba tarihi da maslahar al’ummarsu, su kara masarautu a yankuna daban-daban. Don haka takardar ta kara da cewa, lokaci ya yi da jihar Katsina za ta tafi da zamani.

S**a kara da cewa, duk duniya kasashe masu tarihi suna kariya da girmama gidajen sarautunsu masu tarihi. Don haka s**a ce, lokacin da Katsina za ta maido da martabar wannan tarihin, ya yi. Kuma hakan zai sa hatta tsaro da kudin shiga daga masu bude ido su karu.

Takardar ta ce, ba wani karin kudi da zai karu ga jiha, domin kowace Karamar hukuma ita ke daukar nauyin Hakimanta. Kuma ana cire kaso biyu na kudaden Kananan hukumomi ana bai wa masarauta, kudaden da ba a binciken su ko bin diddigin ya ake kashe su.

S**a ce masarautar Katsina na amsar miliyoyin Naira duk wata, amma har yanzu albashin wasu dogarai a masarautar na karbar kasa da Naira dubu goma.

Takardar ta ce, tun da aka nada Sarkin Katsina da ke sama, akwai yankunan da bai taba kai masu rangadi ba, ya ji wane hali wadannan talakawan nasa suke a ciki. Kuma lamarin na yi ma talakawan yankin ciwo. Don haka duk masarautar da aka yanka za a yi amfani da kudaden da ake cirewa na wannan yankin a bai wa masarautar da ke yankin.

Marubutan s**a ce, yin haka zai sa kowane Sarki ya shiga gaba wajen ci gaban yankinsa da al ummarsa. Takardar ta rika kafa hujja da littattafan tarihi da takardun tarihi.

Jaridun Katsina Times sun tuntubi wani dan Majalisar dokokin jihar Katsina a kan me za su yi in wannan bukatar ta zo gaban su? Ya bayyana cewa, bai son a fadi sunan sa, amma su zababbun al’umma ne, don haka duk wata bukata ta jama’a suna tare da ita.

Idan al’umma na bukatarm karin masarautu, za su duba tsarin mulki da dokokin Majalisa, za su yi masu, don su wakilan al’umma ne.

Katsina City News

Lalacewar Magudanar Ruwa a Ƙerau cikin Birnin Katsina na Barazana ga Dukiya da Lafiyar Jama’a Daga Abdulrazaq Ahamed Jib...
09/05/2025

Lalacewar Magudanar Ruwa a Ƙerau cikin Birnin Katsina na Barazana ga Dukiya da Lafiyar Jama’a

Daga Abdulrazaq Ahamed Jibiya

Mutane mazauna unguwar Ƙerau da ke cikin birnin Katsina na fuskantar barazana ga rayuwarsu sak**akon mummunar lalacewar wata tsohuwar magudanar ruwa da ke yankin, wadda aka gina kimanin shekaru 50 da s**a wuce.

Rahotanni sun bayyana cewa magudanar ruwan na ci gaba da tabarbarewa, lamarin da ke barazana ga gidajen da ke kusa da ita, musamman a lokacin damina. Mazauna yankin sun bayyana damuwarsu kan yadda zaizayar ƙasa ke ci gaba da lalata muhallin su, inda s**a ce matsalar ta wuce ƙarfin su na magancewa.

Wasu daga cikin mazauna yankin, ciki har da Alhaji Yusuf Dankano da Alhaji Musa Jikamshi, sun ce sun shafe shekaru suna kai ƙorafi ga hukumomi, amma ba a ɗauki matakin da ya dace ba. A cewarsu, lalacewar magudanar ruwan na barazana ga lafiyar jama’a sak**akon yaduwar sauro da wasu ƙwari da ke haifar da cututtuka.

Umar Abubakar da Habibu Ahmed Dara sun bayyana cewa yankin ya zama matattarar sauro da sauran ƙwari masu haddasa cututtuka, musamman ga yara da tsofaffi. Haka zalika, wata mata mai suna Rabi’atu Ahmed Danbaba ta bayyana damuwarta kan yadda matsalar ke shafar lafiyar yara, inda ta gargadi cewa idan ba a dauki matakin gyara ba kafin damina mai zuwa, matsalar za ta ƙara muni.

Mazauna yankin sun yi kira ga hukumomin gwamnati da su gaggauta ɗaukar matakin gina sabuwar magudanar ruwa domin ceto rayukan al’umma. Sun bukaci hadin gwiwar wakilan da ke wakiltar yankin domin kawo mafita ga matsalar da ta dade tana addabar Ƙerau.

Masu sharhi sun bayyana cewa irin wannan matsala na buƙatar matakin gaggawa daga gwamnati domin dakile haɗurra da kare lafiyar jama’a, musamman a yanayi na sauyin yanayi da ake fuskanta a yanzu. Sun kuma bukaci samar da tallafi ga waɗanda wannan matsala ta shafa kai tsaye.

GOVERNMENT HOUSE, KATSINAPRESS RELEASE Governor Radda Applauds FG $158 Million Agricultural Value Chain Programme for No...
07/05/2025

GOVERNMENT HOUSE, KATSINA

PRESS RELEASE

Governor Radda Applauds FG $158 Million Agricultural Value Chain Programme for Northern Nigeria


Katsina State Governor and Chairman of the Northwest Governors' Forum, Malam Dikko Umaru Radda, has applauded the Federal Government's signing of a $158.15 million financing agreement for the Value Chain Programme in Northern Nigeria (VCN).

The Governor, who attended the signing ceremony at the Presidential Villa, Abuja, described the development as a vital intervention that will significantly improve agricultural productivity across the northern region.

"This initiative represents a transformative opportunity for our farmers and agribusinesses in Katsina State and across the entire northern region," Governor Radda stated.

The Governor also added that the VCN programme aligns perfectly with the state's agricultural development agenda and will complement ongoing efforts to modernize farming practices, enhance value addition, and create sustainable livelihoods for the people.

The Governor pledged Katsina State's full commitment to the successful implementation of the programme, noting that his administration has already put in place necessary structures to maximize the benefits for local farmers, especially women, youth, and vulnerable groups.

The eight-year VCN initiative, which will be implemented immediately in nine northern states including Katsina, aims to sustainably reduce poverty, enhance nutrition, and improve resilience of rural and vulnerable populations. The programme is co-funded by the International Fund for Agricultural Development (IFAD), the French Development Agency (AFD), and the Government of Nigeria.

Vice President Kashim Shettima, who presided over the signing ceremony, described the initiative as "a declaration of faith in the North—not as a region of deficits, but as a place of abundance," adding that it fulfills President Bola Ahmed Tinubu's promise to reduce poverty, nourish Nigerians, and restore dignity to farming families across the beneficiary states.

The Vice President emphasized that the programme will serve as a steady pipeline of raw materials for the Special Agro-Industrial Processing Zones (SAPZs) currently under construction across Nigeria, shifting the country "from exporting raw produce to exporting value-added goods—creating jobs, wealth, and industrial stability."

Equally speaking, the Minister of Agriculture and Food Security, Sen. Abubakar Kyari said the signing of the financing agreement represents a significant milestone in the efforts to transform the agricultural landscape in Nigeria under the Renewed Hope Agenda of the Tinubu administration.

Mrs. Dede Ekoue, Country Director of IFAD, noted that the programme will target about 3.1 million household members across the nine states, focusing on climate-smart agriculture, improving post-harvest handling, increasing access to business development services for youth and women agri-preneurs, and scaling up access to digital solutions for productivity.

The IFAD Country Director also added that the expected results include the creation of over 30,000 jobs and entrepreneurial opportunities for youths, women, and vulnerable groups, as well as the construction of over 229km of roads across the region to enhance access to markets.

Other governors present at the ceremony, including Prof. Babagana Zulum of Borno and Alhaji Umar Namadi of Jigawa, joined Governor Radda in commending President Tinubu and Vice President Shettima for their leadership in implementing this transformative programme for northern Nigeria.

Also present at the meeting were some members of the National Assembly; Minister of State for Regional Development, Hon. Uba Maigari Ahmadu; the Regional Director of IFAD, Mr Bernard Mwinyel Hien; the Deputy Governors if Zamfara, Kebbi, Sokoto, Kano, Yobe and Bauchi States; heads of government agencies and representatives of development partners, among others.

Ibrahim Kaula Mohammed
Chief Press Secretary to the Governor of Katsina State

8th April, 2025

BAYANI KAN BILLBOARD DIN "KATSINA BA KORAFI"Daga, Abdullahi GoraDG Katsina ba Korafi Movement Ina son amfani da wannan d...
07/05/2025

BAYANI KAN BILLBOARD DIN "KATSINA BA KORAFI"

Daga, Abdullahi Gora
DG Katsina ba Korafi Movement

Ina son amfani da wannan dama wajen yin bayani tare da neman hakuri daga jama'ar Jihar Katsina kan wasu Billboard da aka sanya a cikin garin Katsina yayin ziyarar Shugaban Kasa Satin daya gabata, da suke dauke da taken, “Katsina Ba Korafi”.

Wannan taken ya janyo cece-kuce da fassara iri-iri daga jama’a, ciki har da manyan masu sharhi. Wannan ya nuna cewa akwai bukatar karin bayani daga gare ni.

1. Fahimtar Jama'a ta Sauya Daga Manufar Asali:
An fahimci sakon da ke cikin billboard din ba daidai ba. Jama’a da dama sun dauka cewa taken na nufin cewa al’ummar Katsina ba su da korafi ko wata matsala, lamarin da ba gaskiya ba ne. Hakikanin gaskiya shi ne, k**ar yadda kowace jiha ke fama da matsaloli, Katsina ma tana da nata kalubale na yau da kullum k**ar tsaro, karancin albarkatu, da dai sauransu.

2. Manufar Asali Ta Movement Din “Katsina Ba Korafi”:
Wannan tafiya ce ta siyasa da muka kirkiro watannin baya da nufin gina zaman lafiya da hadin kai tsakanin ‘yan jam’iyyar APC a jihar Katsina, musamman tsakanin Gwamna Dikko Umar Radda da Maigidanmu, Ministan Gidaje, Arc. Ahmed Musa Dangiwa.
Mun kafa wannan tafiya ne domin nuna cewa ba tare da wata baraka ko rikici ba, mu matasa a APC muna tare da gwamnati, hadin kai, da kuma nuna gamsuwa da salon shugabancin Malam Dikko Radda.

3. Lokacin Damuka Sanya Billboard:
Mun ga cewa ziyarar Shugaban Kasa dama ce da za mu yi amfani da ita wajen bayyana cewa akwai jituwa da fahimta tsakanin manyanmu, kuma mu matasa muna tare da su da kuma tafiyar jam’iyya. Ba domin wuce gona da iri ba, ba kuma domin rage kima ko jin radadin halin da jama'a ke ciki ba.

Wadannan kalmomi an tsara su ne don karfafa dankon zumunci da jituwa a tsakanin shugabanninmu, ba wai don watsi da korafin jama’a ba. A gaskiya, muna da cikakken fahimta cewa akwai korafi a Katsina, k**ar yadda kowace jiha ke da nata.

Ina rokon gafara da fahimta daga jama’ar Katsina kan yadda aka fahimci billboard din. Ba domin raina matsalolin jama'a aka sanya su ba, illa kawai muna nuna hadin kai da goyon bayan gwamnatin Gwamna Malam Dikko Umar Radda da jam’iyyar APC a jahar katsina.

Allah ya kara mana fahimta da zaman lafiya a jihar Katsina da Nigeria baki daya.
Na gode.

Rahoto/ Katsina Post

Magana ta kare :  Jigo a tafiyar Jam'iyyar CPC ta Buhari, Barista Abubakar Malami SAN, kuma tsohon babban lauya na taray...
05/05/2025

Magana ta kare : Jigo a tafiyar Jam'iyyar CPC ta Buhari, Barista Abubakar Malami SAN, kuma tsohon babban lauya na tarayya, yayi ganawar sirri da Malam Nasiru El-Rufai.

Ziyarar ta bar tambayoyi masu tarin yawa a zukatan Yan Najeriya, wasu na ganin akwai yiyuwar Malami ya sauya sheka daga jam'iyyar APC mai mulki zuwa jam'iyyar adawa ta SDP.

A kwanakin baya raɗe-raɗi da dama sun yawaita, akan shirin sauya sheka da ake tsammata, ciki har da Malami da Amechi da wasu daga cikin manya yan Siyasa a Najeriya.

ATP Hausa

An Bankado Sabon Rikici Tsakanin Manyan Jiga-Jigan Siyasar APC a Katsina!Daga:  Hikaya Radio Wani rikici mai ɗauke da za...
04/05/2025

An Bankado Sabon Rikici Tsakanin Manyan Jiga-Jigan Siyasar APC a Katsina!

Daga: Hikaya Radio

Wani rikici mai ɗauke da zafafan kalamai ya taso tsakanin wani fitaccen ɗan majalisar wakilai daga Musawa/Matazu da Mataimakin Shugaban jam’iyyar APC na jihar Katsina, Bala Abu.

A cikin wani faifan sauti da ɗan majalisar ya ɗauka da kansa, an jiyo shi yana caccakar Bala Abu da zargin cewa akwai matsala a takardun karatunsa. Ya bukaci Bala Abu ya fito fili ya bayyanawa duniya gaskiya, yana mai cewa ba ya buƙatar a ɓoye gaskiya ko a kare wani.

Zazzafar fadar ta kai matakin da ɗan majalisar ya furta wasu kalamai masu nauyi da s**a tada kura a tsakanin magoya baya da masu sharhi a kafafen sada zumunta.

Lamarin ya ɗauki hankalin jama’a inda ake ci gaba da sauraron yadda rikicin zai kaya. Muna fatan zaman lafiya da fahimta zai samu a tsakanin su.

Gwamnatin Nijeriya Ta Goyi Bayan Amfani Da Ƙirƙirarrar Basira Cikin Ɗa'a A Aikin Jarida - IdrisGwamnatin Nijeriya ta bay...
04/05/2025

Gwamnatin Nijeriya Ta Goyi Bayan Amfani Da Ƙirƙirarrar Basira Cikin Ɗa'a A Aikin Jarida - Idris

Gwamnatin Nijeriya ta bayyana ƙudirin ta na amfani da Ƙirƙirarrar Basira (AI) a aikin jarida cikin ɗa'a, tare da mayar da hankali kan 'yancin faɗin albarkacin baki, bin ƙa'idojin aikin jarida da kuma koyar da jama'a ilimin kafafen watsa labarai.

An ƙarfafa wannan ƙudiri ne a taron bikin Ranar 'Yancin Jarida ta Duniya na shekarar 2025, wanda aka gudanar a otal ɗin Sheraton da ke Abuja a ranar Juma'a, ƙarƙashin jagorancin Konrad Adenauer Stiftung (KAS) da Cibiyar Ƙirƙire-Ƙirƙiren Jarida da Cigaba (CJID).

Taken taron shi ne: “Rahoto a Sabuwar Duniya – Tasirin AI Kan 'Yancin Jarida da Kafafen Yaɗa Labarai,” inda aka tattauna yadda Ƙirƙirar Basira take sauya salon aikin jarida da ƙalubalen da ke tattare da hakan.

A cikin jawabin sa a taron, Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya bayyana wasu manyan fa’idoji da kuma irin barazanar da ke tattare wajen amfani da AI a cikin ɗakunan buga labarai.

Ya ce duk da cewa AI na taimaka wa 'yan jarida a Nijeriya wajen saurin bayar da rahoto, da nazarin bayanai da gudanar da bincike, yana da matuƙar muhimmanci a yi amfani da wannan sabuwar fasahar cikin hankali da bin ƙa’idoji.

Ya ce: “A yayin da muke rungumar aikin jarida da fasahar AI, dole ne mu tabbatar da cewa ba za a tauye 'yancin jarida ba, illa ma a ƙara ƙarfafa shi.”

Ministan ya kuma ba da sanarwar cewa Nijeriya za ta kafa Cibiyar Ilimin Kafafen Watsa Labarai ta UNESCO a Buɗaɗɗiyar Jami'ar Nijeriya (NOUN), inda Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya riga ya amince da kuɗin kafa cibiyar.

Ana sa ran wannan cibiyar za ta kasance cibiyar ƙasa da ƙasa da za ta inganta aikace-aikacen kafafen watsa labarai cikin gaskiya da tunani mai zurfi a fannin dijital.

Haka kuma, ya bayyana cewa Nijeriya tana kan hanyar ƙaddamar da tsarin dokar ƙasa kan amfani da AI a cikin aikin jarida.

Wannan tsari zai ƙarfafa ƙirƙire-ƙirƙire amma ba tare da tauye 'yancin jarida ko karya ƙa'idojin aikin ba.

Idris ya buƙaci haɗin gwiwa tsakanin 'yan jarida, da masana fasaha, da kafafen yaɗa labarai, da 'yan siyasa da ƙungiyoyin farar hula domin samar da ƙa’idojin amfani da AI, da koyar da sababbin dabaru, da tabbatar da gaskiya, da kuma faɗakar da al'umma.

A nata jawabin, Marija Peran, wakiliyar KAS a Nijeriya, ta jaddada irin damar da AI ke bayarwa ga aikin jarida, tare da yin kashedi kan haɗurran da ke tattare da hakan.

Ta ce: “Yana da muhimmanci mu kare 'yancin kafafen yaɗa labarai a duk duniya, musamman yanzu da AI ke ƙara shiga aikin jarida.

“A matsayin ta na ƙungiya mai kishin dimokiraɗiyya da doka da oda, KAS tana tare da kafafen yaɗa labarai wajen fuskantar wannan sabon yanayi.”

Taron ya samu halartar mutane daban-daban, ciki har da Shugaban Kwamitin Harkokin Yaɗa Labarai da Hulɗa da Jama’a na Majalisar Wakilai, Honarable Akintunde Rotimi Jr.; da wakilan kafafen yaɗa labarai, da ƙungiyoyin farar hula da kuma abokan hulɗa na ƙasa da ƙasa.

Rahoto/ Madubi - H

Governor Radda Hosts President Tinubu to State Dinner in KatsinaGovernor Dikko Umaru Radda hosted President Bola Ahmed T...
03/05/2025

Governor Radda Hosts President Tinubu to State Dinner in Katsina

Governor Dikko Umaru Radda hosted President Bola Ahmed Tinubu to a dinner at the State Banquet Hall in Katsina last night.

The dinner was part of lineup activities for the President's two-day working visit to the state and it showcases Katsina's renowned hospitality and rich cultural heritage.

The high-profile gathering attracted influential leaders including former Governors Ibrahim Shehu Shema and Aminu Bello Masari. Nigerian Governors' Forum Chairman and Kwara State Governor Abdulrahman Abdulrazaq led a powerful delegation of governors including Mai Mala Buni of Yobe, Mohammed Inuwa of Gombe, Umar Namadi of Jigawa, Uba Sani of Kaduna, and Aliyu Sokoto of Sokoto.

The dinner was also attended by Members of the State Executive Council, State Legislators, LG Chairmen, traditional rulers and business tycoons.

KTTV

Shugaba Tinubu Ya Bayyana Dikko Radda a Matsayin ‘Gwamna Mai Gaskiya, Riƙon Amana, da Ƙwazo’Shugaban Ƙasar Najeriya, Bol...
03/05/2025

Shugaba Tinubu Ya Bayyana Dikko Radda a Matsayin ‘Gwamna Mai Gaskiya, Riƙon Amana, da Ƙwazo’

Shugaban Ƙasar Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, ya yabawa Gwamnan Jihar Katsina, Dikko Umaru Radda, bisa ga irin salon jagorancin da yake yi a jihar Katsina, inda ya bayyana shi a matsayin “gwamna mai gaskiya, amana, da ƙwazo.”

Wannan yabon ya zo ne lokacin da ya ke jawabi a wurin ƙaddamar da Cibiyar Samar da Kayan Aikin Noma ta Zamani ta Jihar Katsina, da kuma hanyar da ta zagaye garin Katsina ta ɓangaren gabas (Eastern Bypass).

Shugaba Tinubu ya jinjina wa gwamnatin Gwamna Radda bisa ga irin gagarumin ci gaban da ta samu cikin shekaru biyu kacal, musamman a fannin noma, samar da kayayyakin more rayuwa, da ci gaban al’umma.

A nasa jawabin, Gwamna Radda ya bayyana cewa tun bayan karɓar rantsuwar k**a aiki shekaru biyu da s**a gabata, gwamnatinsa ta mayar da hankali ne kan noma, samar da kayayyakin more rayuwa, tsaro, da samar da ayyuka.

Ya kuma jaddada muhimmancin sabuwar cibiyar samar da kayan aikin noma ta zamani wajen tallafawa manoman jihar, tare da sanar da shirye-shiryen gwamnatin sa k**ar raba takin zamani da samar da injinan ban ruwa ma su amfani da hasken rana.

Gwamnan ya kuma yi bayani dalla-dalla game da manyan ayyukan kayayyakin more rayuwa da gwamnatin sa ta samat, ciki hadda sabunta biranen jihar da samar da ruwa.

Haka zalika ya kuma bayyana godiyar sa ga Shugaba Tinubu bisa ga goyon bayan da gwamnatin tarayya ke ba shi wajen yaƙi da matsalar tsaro.

Daga karshe ya kuma yi godiya ga sauran masu ruwa da tsaki a jihar da shugabannin gargajiya bisa gudummuwar su wajen ci gaban jihar.

Manyan bakin da s**a halarci taron sun hada da Gwamnonin Kaduna da Borno, tsaffin Gwamnonin jihar Katsina da s**a hada da Barista Ibrahim Shema da Rt. Hon. Aminu Bello Masari, Ministoci, ƴan majalisar tarayya da na jihar Katsina daban-daban, shugabannin hukumomin gwamnati da dama da shugabannin jam’iyyar APC a matakai daban-daban da dai sauran su.

Rahoto / Katsina Post

Kungiyar Kiristoci ta Najeriya (CAN), reshen jihohin  19 na arewacin Najeriya, da Babban Birnin Tarayya (FCT), ta bayyan...
30/04/2025

Kungiyar Kiristoci ta Najeriya (CAN), reshen jihohin 19 na arewacin Najeriya, da Babban Birnin Tarayya (FCT), ta bayyana damuwa kan abin da ta kira yunkurin bata suna da ake yi wa Seyi Tinubu, ɗan Shugaba Bola Ahmed Tinubu, ta hanyar kafafen yada labarai.

A cikin wata sanarwa da shugaban CAN na yankin, Fasto John Joseph Hayab, ya fitar, kungiyar ta jaddada bukatar gujewa yada labarun da bashi da tushe da asali.

Ya kara da cewa, “Saboda Seyi ɗan Tinubu ne, bai k**ata a rika bata sunansa ba, da yaɗa ƙaryar da za tayi barazanar halaka rayuwars shi. Rayuwa za ta ci gaba bayan mulkin mahaifinsa,” in ji Hayab.

ATP Hausa

Address

Area (A) Last Road, Nyanay Abuja
Garki
900001

Telephone

+2349128230649

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when FBC posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to FBC:

Share