FBC

FBC Welcome to Fact Broadcasting Company's (FBC) page – We are "The Voice of the Voiceless"

Hon. Yusuf Sulaiman Jibia ya karbi ragamar k**a aiki daga tshowar kwamishinan Ilimin Firame da Sakandire Hajiya Zainab M...
30/10/2025

Hon. Yusuf Sulaiman Jibia ya karbi ragamar k**a aiki daga tshowar kwamishinan Ilimin Firame da Sakandire Hajiya Zainab Musa Musawa.

Ma’aikatar Ilimin Firamare da Sakandare ta Jihar Katsina ta gudanar da bikin mika ragamar aiki tsakanin sabon kwamishina, Hon. Yusuf Sulaiman Jibia, da tsohuwar kwamishina, Hajiya Zainab Musa Musawa, a dakin taron ma’aikatar ranar Alhamis, 30 ga Oktoba, 2025.

A jawabinsa, sabon kwamishinan, Hon. Yusuf Sulaiman Jibia, ya bayyana kudirinsa na yin aiki tukuru tare da hadin kan dukkan ma’aikatan ma’aikatar domin ciyar da harkar ilimi gaba. Ya kuma gode wa Gwamna Dikko Umar Radda bisa amincewa da ya nuna masa, tare da alkawarin mayar da hankali kan karfafa ilimin firamare, inganta jin dadin malamai, da kuma kyautata gine-ginen makarantu a fadin jihar.

Hon. Jibia ya bukaci Hajiya Zainab Musa Musawa da ta ci gaba da bayar da shawarwari da goyon baya domin dorewar nasarorin da aka cimma.

A nata bangaren, tsohuwar kwamishina Hajiya Zainab Musa Musawa, ta gode wa shugabanni da ma’aikatan ma’aikatar bisa hadin kai da goyon bayan da s**a nuna mata a lokacin aikinta. Ta bayyana wa’adinta a matsayin lokaci mai albarka wanda ya haifar da nasarori da dama, ciki har da sabunta manhajar karatu, gyaran makarantu, da horar da malamai. Hajiya Zainab ta yi addu’ar fatan alheri ga sabon kwamishinan tare da bayyana tabbacin cewa zai ci gaba da daga darajar ilimi a jihar Katsina.

Shi ma Shugaban Hukumar Ilimin Firamare ta Jihar Katsina (SUBEB), Dr. Kabir Magaji Gafia, ya yi maraba da sabon kwamishinan, inda ya bayyana kwarin gwiwa cewa kwarewarsa da jajircewarsa za su kawo sabuwar dama ga fannin ilimi. Ya tabbatar masa da cikakken goyon bayan hukumar wajen aiwatar da manufofi da za su inganta ilimi da tabbatar da samun damar koyo ga kowane yaro a jihar.

Shugaban Karamar Hukumar Jibia, Hon. Sirajo Ado, ya taya Hon. Yusuf Jibia murna bisa wannan sabon mukami, tare da yabawa Gwamna Radda bisa hangen nesansa na daga darajar Yusuf Jibia daga matsayin mai bai wa gwamna shawara na musamman zuwa kwamishina. Ya tabbatar da cewa babu shakka, harkar ilimi za ta samu gagarumar nasara a karkashin jagorancinsa.

Taron ya samu halartar manyan jami’an gwamnati, shugabannin hukumomi, ‘yan siyasa, ‘yan kasuwa, dangi, da magoya baya da s**a halarta domin taya sabon kwamishinan murna.

Gwamnatin Shugaba Tinubu, ta cire sunan Maryam sanda, Wadda ke jiran hukuncin kisa.
29/10/2025

Gwamnatin Shugaba Tinubu, ta cire sunan Maryam sanda, Wadda ke jiran hukuncin kisa.

Sakatariyar Jam'iyyar PDP a Abuja ta ki sayarwa tsohon gwamnan Jigawa, Sule Lamido takardar neman tsayawa takarar shugab...
27/10/2025

Sakatariyar Jam'iyyar PDP a Abuja ta ki sayarwa tsohon gwamnan Jigawa, Sule Lamido takardar neman tsayawa takarar shugabancinta a zaben da za'ayi a ranar 15 ga watan Nuwamba mai zuwa a lbadan.

Rahotanni sun ce matakin ya biyo bayan fidda ɗan takara guda da gwamnonin PDP daga Arewa da kuma wasu jiga jigan jam'iyyar s**a yi wajen bayyana tsohon ministan ayyuka na musamman, Barr Tanimu Turaki a matsayin ɗan takara ɗaya tilo daga yankin.

Lamido ya sha alwashin daukar duk matakan das**a dace, ciki har da zuwa kotu idan bukatar haka ta taso domin neman hakkin sa.

Rahoto/ RFI Hausa.

Paul Biya ya sake lashe zaben kasar Kamaru.Daga Auwal Isah Musa Hukumar Zaɓe ta ƙasar Kamaru (ELECAM) ta bayyana cewa Pa...
27/10/2025

Paul Biya ya sake lashe zaben kasar Kamaru.

Daga Auwal Isah Musa

Hukumar Zaɓe ta ƙasar Kamaru (ELECAM) ta bayyana cewa Paul Biya ne ya lashe zaɓen shugaban ƙasa na ƙasar, wanda aka gudanar a farkon watan Oktoba.

Sanarwar ta fito ne jim kaɗan bayan Kotun Tsarin Mulki ta kammala sauraron ƙorafe-ƙorafen da jam’iyyun adawa s**a shigar, inda ta tabbatar da sahihancin sak**akon da hukumar za6e ta gabatar.

A cewar hukumar k**ar yadda Jaridar Taskar Labarai ta bibiya, Paul Biya ya samu fiye da 53.66% na ƙuri’un da aka kada, yayin da babban ɗan'adawa Isah Tchiroma Bakary ya samu kusan 35.19%.

Yanzu haka dai magoya bayan jam’iyyar CPDM ta shugaban ƙasar sun fara murnar nasarar a wasu sassan birnin Yaoundé, duk da cewa jami’an tsaro sun sanya dokar hana taro domin guje wa barkewar rikici.

Paul Biya, wanda ke mulki tun 1982, zai ci gaba da jagorantar ƙasar Kamaru a sabon wa’adinsa na takwas a jere inda zai yi shekaru bakwai a gaba kafin sake gudanar da wani zaben, wanda hakan kuma ke bayyanar cewar ya mulki kasar na kusan tsawon rabin karni

Da duminsa; Majalisar Tarayya ta aminta da ƙirƙiro sabbin jihohi 6, yanzun Nijeriya za ta koma tana da jihohi 42Haɗaɗɗiy...
26/10/2025

Da duminsa; Majalisar Tarayya ta aminta da ƙirƙiro sabbin jihohi 6, yanzun Nijeriya za ta koma tana da jihohi 42

Haɗaɗɗiyar kwamitin majalisar dattawa da ta wakilan Najeriya kan yi wa kundin tsarin mulkin ƙasar garambawul ta amince da a ƙirƙiro jihohi guda shida.

Wannan na cikin matsayar da aka cimmawa a ƙarshen taron ƙara wa juna sani na kwana biyu, wanda mataimakin majalisar dattawa Sanata Barau I. Jibrin da mataimakin shugaban majalisar wakilai, Benjamin Kalu s**a jagoranta a jihar Legas.

Kwamitin ya tattauna ne kan buƙatu guda 69, ciki har da buƙatar ƙirƙirar jihohi 55 da buƙatar a ƙirƙirar ƙananan hukumomin 278 k**ar yadda jaridar Daily Trust mai zaman kanta ta ruwaito.

A game da buƙatar ƙirƙirar jihohi 55 da aka gabatar a ranar Asabar, kwamitin ya amince da ƙirƙirar jihohi guda shida a duk shiyoyin ƙasar guda shida.

Idan aka amince da ƙirƙirar sababbin jihohi, Najeriya za ta zama tana da jihohi 42 ke nan.

Sojojin Sama Sun Kuɓutar da Mutane 62 daga Hannun Ƴan Bindiga a KatsinaGwamnatin Jihar Katsina ta tabbatar da kuɓutar mu...
18/08/2025

Sojojin Sama Sun Kuɓutar da Mutane 62 daga Hannun Ƴan Bindiga a Katsina

Gwamnatin Jihar Katsina ta tabbatar da kuɓutar mutane 62 da aka yi garkuwa da su, bayan wani luguden wuta na sojojin saman Najeriya da ya kai farmaki a sansanin fitaccen ɗan fashi Muhammadu Fulani da ke Jigawa Sawai, Ƙaramar Hukumar Danmusa, wacce ke iyaka da Jihar Zamfara. Harin da aka kai da misalin ƙarfe 5:10 na yamma ranar Asabar ya tilasta wa ‘yan bindiga barin sansaninsu, abin da ya bai wa waɗanda aka yi garkuwa da su damar tserewa.

Rahotanni sun nuna cewa mutane 12 daga cikin waɗanda s**a kuɓuta na samun kulawa a Asibitin Gwamnati na Matazu, yayin da wasu 16 ke tsare a sansanin sojoji na FOB da ke Kaiga Malamai. Gwamnati ta tabbatar da cewa za a haɗa waɗannan mutanen da iyalansu bayan an kammala binciken lafiya.

A cewar wasu daga cikin waɗanda aka ceto, ‘yan bindigar sun watse bayan luguden wutar da aka kai musu, abin da ya sa mutane kusan 62 s**a samu damar tserewa ta wurare daban-daban. Mafi yawan waɗanda aka sace an ɗauke su ne daga ƙauyen Sayaya a daren Litinin, 11 ga Agusta, 2025, lokacin da ‘yan bindigar Fulani s**a kai hari. Kungiyar ta dade tana addabar Matazu, Kankia, Dutsinma da wasu sassa na Jihar Kano.

Domin magance maimaita hare-haren ‘yan bindiga a ƙananan hukumomin Matazu da Bakori, gwamnatin jihar ta tura rundunar Quick Response Wing ta sojojin sama don dawo da zaman lafiya. Rundunar tsaro na ci gaba da sa ido a yankin domin gudanar da ƙarin aikin ceto. An bayyana cewa yankin na ci gaba da kasancewa cikin natsuwa.

Kwamishinan Tsaron Cikin Gida da Harkokin Gidaje na Jihar Katsina, Dr. Nasir Mu’azu, ya yaba da ƙoƙarin jarumtakar dakarun tsaro a madadin Gwamna Dikko Umaru Radda. Ya jaddada kudirin gwamnatin jihar na kawo ƙarshen matsalar ta’addancin ‘yan bindiga a Katsina tare da tabbatar da zaman lafiya mai ɗorewa.

FEC Imposes 7-Years Ban on New Federal Higher InstitutionsThe Federal Executive Council (FEC) has placed a seven-year mo...
14/08/2025

FEC Imposes 7-Years Ban on New Federal Higher Institutions

The Federal Executive Council (FEC) has placed a seven-year moratorium on the establishment of new federal tertiary institutions.

The moratorium covers universities, polytechnics and colleges of education.

Addressing State House correspondents after the FEC meeting on Wednesday, Minister of Education, Dr Olatunji Alausa, said the move was aimed at curbing the proliferation of under-utilised institutions and refocusing resources on improving existing ones.

Alausa disclosed that the decision was reached after available statistics showed that access to tertiary education in Nigeria was “no longer the problem,” rather the unchecked duplication of federal tertiary institutions had led to inefficiencies, poor infrastructure, inadequate staffing, and declining student enrolment.

He said several federal universities operate far below capacity, with some having fewer than 2,000 students, adding that in one institution, there are 1,200 staff serving fewer than 800 students.

“This is a waste of government resources. Today, we have 199 universities where fewer than 100 candidates applied through JAMB for admission. In fact, 34 universities recorded zero applications,” he said.

Mai girma Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda, PhD, CON, zai dauki hutu na tsawon makonni uku domin kula da l...
13/08/2025

Mai girma Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda, PhD, CON, zai dauki hutu na tsawon makonni uku domin kula da lafiyarsa.

Za a fara wannan hutun dubar lafiyar ne daga Litinin, 18 ga Agusta, 2025. Gwamna Radda ya nuna godiyarsa ga goyon baya, fahimta da addu’o’in al’ummar Jihar Katsina.

Ya jaddada kudurinsa na komawa bakin aiki da sabuwar kuzari da jajircewa bayan kammala wannan hutu na dubar lafiya.

“Ina mika godiya ta ga kowa bisa kalaman alheri da goyon bayan da kuke nuna min. Yin wadannan matakai na kula da lafiya yana da muhimmanci domin in ci gaba da gudanar da ayyuka yadda ya k**ata tare da yanke sahihan hukunci domin ci gaban jiharmu. Ina fatan dawowa bakin aiki nan da zarar na kammala binciken lafiyata,” in ji Gwamna Radda.

Domin tabbatar da ci gaban mulki ba tare da tangarda ba, an nada Mataimakin Gwamna, Malam Faruk Lawal, HCIB (Sarkin Fulanin Jobe), domin rike ragamar mulki a matsayin mukaddashi yayin wannan hutu.

Gwamna Radda ya bayyana kwarin gwiwarsa cewa Mataimakin Gwamna zai ci gaba da tafiyar da al’amuran gwamnati da irin wannan jajircewa da kishin kasa.

Muna tabbatar wa jama’a cewa dukkan shirye-shirye, tsare-tsare da ayyukan ci gaba za su ci gaba da tafiya yadda aka tsara ba tare da katsewa ba.

Tun farkon wa’adinsa, Gwamna Radda ya kasance jarumi wajen aiwatar da “Building Your Future Agenda”, inda jagorancinsa ya taka muhimmiyar rawa wajen bunkasa manyan manufofin jihar.

Gwamnatin jiha na sa ran dawowarsa cikin koshin lafiya domin ci gaba da hidima ga al’umma.

Bala Salisu Zango, PhD
Kwamishinan Yaɗa Labarai da Al’adu na Jihar Katsina

KIRA GA GWAMNATI: HALIN DA MAZABAR WAKILIN GABAS II KE CIKIAssalamu alaikum wa rahmatullah.Kamar yadda Maigirma Shugaban...
07/08/2025

KIRA GA GWAMNATI: HALIN DA MAZABAR WAKILIN GABAS II KE CIKI

Assalamu alaikum wa rahmatullah.

Kamar yadda Maigirma Shugaban Kasar Najeriya 🇳🇬 ya bayar da umarni cewa a kula da kowace mazaba daga cikin mazabun 774 da ke fadin kasar nan, abin takaici ne yadda mazabar Wakilin Gabas II, da ke cikin karamar hukumar Katsina, ke ci gaba da fuskantar koma baya da wulakanci.

A maimakon a tattauna don samar da mafita ga matsalolin al’umma, shugabannin wasu taruka sun watsa taro bisa wasu ikirari da korafe-korafe da s**a shafi jin dadin kansu, ba na al’umma ba. Wannan al’amari ya kara jefa jama’a cikin damuwa da rashin kwarin gwiwa.

Al’ummar wannan mazaba na bukatar a saurare su tare da daukar matakan gaggawa kan manyan matsalolin da s**a dade suna fama da su. Wasu daga cikin bukatun sune:

MUHIMMAN BUKATUN AL’UMMAR MAZABAR WAKILIN GABAS II

1. Gyaran makarantu:

Makarantar Firamare ta Dutsin Amare

Makarantar Firamare ta Kofar Marusa
Domin yimasu ginin sama (bene)

2. Gina makarantar gaba da sakandire a cikin mazabar domin cigaban ilimi.

3. Samar da fitilun t**i (solar lights) a manyan hanyoyin mazabar.

4. Gyaran hanyoyi da kwatoci a unguwanni k**ar:

Katsira

Dutsin Amare zuwa tafkin Rakati

Kerau

Unguwar ‘Yan Wanki, da sauransu.

5. Kammala ginin outpost don inganta tsaro da kariya ga al’umma.

6. Samar da ayyukan yi da sana’o’i ga matasa da mata domin rage zaman banza da rashin aikin yi.

7. Gyaran tashoshin sufuri na:

Kofar Marusa

Kofar Durbi

Da kuma samar da motocin gwamnati domin saukaka sufuri ga jama’a.

8. Gyaran makarantu na tsangaya, islamiyyu da masallatai a unguwanni daban-daban.

9. Karin taranfomomi da inganta wutar lantarki a cikin unguwanni.

10. Farfado da asibitin ‘dispensary’ da ke cikin makarantar Dutsin Amare domin kulawa da lafiya.

11. Kammala ginin tsohon gidan mai martaba Sarkin Katsina da ke unguwar Shaiskawa, domin adana tarihin al’ada da cigaba.

KARSHEN KIRA

Muna amfani da wannan dama domin kira da roko ga Maigirma Gwamnan Jihar Katsina, da sauran masu ruwa da tsaki – 'yan siyasa, jami’an gwamnati, da masu hannu da shuni – da su dubi wannan mazaba da ido na tausayi da adalci.

Duk da kasancewar Wakilin Gabas II daya ce daga cikin mazabun Jihar Katsina, abin takaici ne cewa babu wata mazaba da ta fi ta komawa baya a fannin ci gaba da walwala.

Muna fatan wannan kira zai kai ga daukar matakan da s**a dace, domin a ba wannan mazaba kulawar da sauran mazabu ke samu a Najeriya.

Allah ya taimaka, ya ba da ikon aiwatarwa.

Nura Nura Garkuwa

Katsina Govt Provides Relief to Banditry VictimsThe Katsina State Government has disbursed over ₦11 million to families ...
06/08/2025

Katsina Govt Provides Relief to Banditry Victims

The Katsina State Government has disbursed over ₦11 million to families affected by banditry attacks in Bakori and Faskari Local Government Areas.

Fact Broadcasting Company (FBC) reports that this assistance is part of the government's efforts to combat terrorism, armed robbery, cattle rustling, and kidnapping.

The beneficiaries include families of those killed, injured, kidnapped, or whose properties were destroyed by bandits. The Senior Special Assistant to the Governor on Victims of Banditry and Internally Displaced Persons (IDPs), Hon. Saidu Ibrahim Danja ‘Kogunan Jibia’, led the distribution of the assistance. The families of military, police, and Community Watch Corps personnel who lost their lives received ₦1 million, while families of slain bandit officers received ₦500,000.

In addition to the financial assistance, the State Emergency Management Agency (SEMA) provided relief items, including food and other essentials, to the victims. The relief items included 50 bags of rice, 20 bags of beans, and other necessities.

Stakeholders, including Hon. Abdurraham Ahmad Kandarawa, commended the government's initiative, praising its commitment to ending security challenges and ensuring the safety of lives and properties. The Deputy Chairman of Bakori Local Government Area also expressed gratitude for the government's efforts.

The Katsina State Government's commitment to supporting the victims of banditry demonstrates its compassion and concern for the families affected. The assistance aims to provide relief and promote peace and stability in the state.

The beneficiaries expressed their happiness and vowed to use the financial support wisely. The handover ceremony, attended by politicians, security officials, and others, marked a significant step towards providing relief to those affected by the banditry attacks.

Address

Area (A) Last Road, Nyanay Abuja
Garki
900001

Telephone

+2349128230649

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when FBC posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to FBC:

Share