30/10/2025
Hon. Yusuf Sulaiman Jibia ya karbi ragamar k**a aiki daga tshowar kwamishinan Ilimin Firame da Sakandire Hajiya Zainab Musa Musawa.
Ma’aikatar Ilimin Firamare da Sakandare ta Jihar Katsina ta gudanar da bikin mika ragamar aiki tsakanin sabon kwamishina, Hon. Yusuf Sulaiman Jibia, da tsohuwar kwamishina, Hajiya Zainab Musa Musawa, a dakin taron ma’aikatar ranar Alhamis, 30 ga Oktoba, 2025.
A jawabinsa, sabon kwamishinan, Hon. Yusuf Sulaiman Jibia, ya bayyana kudirinsa na yin aiki tukuru tare da hadin kan dukkan ma’aikatan ma’aikatar domin ciyar da harkar ilimi gaba. Ya kuma gode wa Gwamna Dikko Umar Radda bisa amincewa da ya nuna masa, tare da alkawarin mayar da hankali kan karfafa ilimin firamare, inganta jin dadin malamai, da kuma kyautata gine-ginen makarantu a fadin jihar.
Hon. Jibia ya bukaci Hajiya Zainab Musa Musawa da ta ci gaba da bayar da shawarwari da goyon baya domin dorewar nasarorin da aka cimma.
A nata bangaren, tsohuwar kwamishina Hajiya Zainab Musa Musawa, ta gode wa shugabanni da ma’aikatan ma’aikatar bisa hadin kai da goyon bayan da s**a nuna mata a lokacin aikinta. Ta bayyana wa’adinta a matsayin lokaci mai albarka wanda ya haifar da nasarori da dama, ciki har da sabunta manhajar karatu, gyaran makarantu, da horar da malamai. Hajiya Zainab ta yi addu’ar fatan alheri ga sabon kwamishinan tare da bayyana tabbacin cewa zai ci gaba da daga darajar ilimi a jihar Katsina.
Shi ma Shugaban Hukumar Ilimin Firamare ta Jihar Katsina (SUBEB), Dr. Kabir Magaji Gafia, ya yi maraba da sabon kwamishinan, inda ya bayyana kwarin gwiwa cewa kwarewarsa da jajircewarsa za su kawo sabuwar dama ga fannin ilimi. Ya tabbatar masa da cikakken goyon bayan hukumar wajen aiwatar da manufofi da za su inganta ilimi da tabbatar da samun damar koyo ga kowane yaro a jihar.
Shugaban Karamar Hukumar Jibia, Hon. Sirajo Ado, ya taya Hon. Yusuf Jibia murna bisa wannan sabon mukami, tare da yabawa Gwamna Radda bisa hangen nesansa na daga darajar Yusuf Jibia daga matsayin mai bai wa gwamna shawara na musamman zuwa kwamishina. Ya tabbatar da cewa babu shakka, harkar ilimi za ta samu gagarumar nasara a karkashin jagorancinsa.
Taron ya samu halartar manyan jami’an gwamnati, shugabannin hukumomi, ‘yan siyasa, ‘yan kasuwa, dangi, da magoya baya da s**a halarta domin taya sabon kwamishinan murna.