02/06/2026
Abin mamaki ne yadda wasu s**a mayar da Mai gidan mu Malam Nasir El-Rufai tamkar shi kadai ne matsalar abin da ya faru da ‘yan Shi’a.
Mu daina yaudarar kanmu.
Rikicin Zaria na 2015 ba aikin gwamnatin jihar Kaduna bane. Aikin rundunar sojojin Najeriya ne, karkashin ikon gwamnatin tarayya. Wannan gaskiya ce da babu wanda zai iya canzawa.
Amma saboda siyasa da son zuciya, sai a juya a fara dora komai kan El-Rufai.
Tambaya mai sauki:
Shin El-Rufai ne shugaban sojoji?
Shin shi ne ya bada umarnin harin?
Idan amsar ita ce a’a, to me yasa ake kokarin jingina masa abin da bai da alaka kai tsaye da shi?
A matsayinsa na gwamna, ya dauki matakan da ya kamata domin tabbatar da doka da oda a Kaduna. Duk wata gwamnati mai hankali a duniya ba za ta bari wata kungiya ta rika karya doka, ta toshe hanyoyi, ta jefa mutane cikin hadari ba.
Ko muna son gaskiya ne ko muna son a yaudari kanmu?
Wasu suna kuka da “hakkin dan Adam”, amma suna manta cewa hakkin sauran ‘yan kasa na tafiya lafiya, na rayuwa cikin zaman lafiya, shima hakki ne.
Ba za ka iya karya doka ba sannan ka ce gwamnati ta kyale ka saboda suna kiran ka wata kungiya. Gaskiya mai daci ita ce: Mutane suna neman wanda za su dora wa laifi ne kawai, ba wai suna neman gaskiya ba.
Idan za a yi magana, a yi da gaskiya: Ba adalci bane a dauki laifin tsarin tsaro na kasa gaba daya a dora shi kan mutum daya saboda kawai suna ko siyasa.
Idan har za mu kasance masu gaskiya, to dole mu daina amfani da sunan El-Rufai wajen boye gaskiyar abin da ya faru.
Ko dai mu fadi gaskiya gaba daya, ko kuma mu ci gaba da yaudarar kanmu.
Ni na zabi gaskiya.
Kai fa?
✍️ BABA SAEED ✍️