ABUH Farhan BExclusive Sunnah

ABUH Farhan BExclusive Sunnah the digital version ���

AURE KAMAR TUƘIN MOTA NE Aure kamar tuƙin mota ne; ba a farawa  da gudu,ana farawa ne da natsuwa da koyon hanya. Mai tuƙ...
15/05/2026

AURE KAMAR TUƘIN MOTA NE

Aure kamar tuƙin mota ne; ba a farawa da gudu,ana farawa ne da natsuwa da koyon hanya. Mai tuƙi mai hankali yana farawa da saka learner, yana koyon yadda ake sarrafa mota kafin ya shiga babban t**i. Haka ma rayuwar aure take.

Idan ma’aurata s**a shiga aure ba tare da ilmi, haƙuri, fahimta da sanin hakkokin juna ba, to za a rika samun:

* karo da hatsaniya,
* guga da saɓani,
* gudun wuce gona da iri wajen fushi,
* da kuma haɗarin da zai iya lalata zaman lafiya.

Aure yana buƙatar:

1. Haƙuri da juriya
2. Fahimtar juna
3. Sauraron juna
4. Girmama ra’ayin abokin zama
5. Kula da kalamai da ɗabi’a

Kamar yadda direba ke koyon dokokin hanya kafin ya iya tuƙi lafiya, haka ma ma’aurata suke buƙatar koyon kimiyyar zaman aure kafin shiga cikinsa.

Duk wanda ya yi gaggawa wajen tuƙi ba tare da ƙwarewa ba, hatsari zai iya samun shi.
Haka ma wanda ya shiga aure ba tare da shiri da ilmi ba, zai iya shiga rikice-rikice masu yawa.

Allah Ya sa a dace da zaman aure mai albarka, soyayya da fahimtar juna. 🤲

Annabi (ﷺ) Yace:"Hakika Allah ba Ya duban surar ku ko dukiyoyinku, sai dai yana duban zukatanku da ayyukanku."حَدَّثَنَا...
09/05/2026

Annabi (ﷺ) Yace:

"Hakika Allah ba Ya duban surar ku ko dukiyoyinku, sai dai yana duban zukatanku da ayyukanku."

حَدَّثَنَا عَمْرٌو النَّاقِدُ، حَدَّثَنَا كَثِيرُ بْنُ هِشَامٍ، حَدَّثَنَا جَعْفَرُ بْنُ بُرْقَانَ، عَنْ يَزِيدَ بْنِ، الأَصَمِّ عَنْ أَبِي هُرَيْرَةَ، قَالَ قَالَ رَسُولُ اللَّهِ صلى الله عليه وسلم ‏ "‏ إِنَّ اللَّهَ لاَ يَنْظُرُ إِلَى صُوَرِكُمْ وَأَمْوَالِكُمْ وَلَكِنْ يَنْظُرُ إِلَى قُلُوبِكُمْ وَأَعْمَالِكُمْ ‏"‏ ‏.‏

Sahih Muslim 2564

Wannan hadisin daga Sahih Muslim (2564) yana nuna muhimmiyar darasi a cikin Musulunci cewa:

Allah ba ya kallon zahirin mutum ko dukiyarsa, sai dai zuciyarsa da ayyukansa.

Wato: Allah (ﷻ) ba ya la’akari da kyawun sura ko yalwar dukiya, sai dai yana kallon tsarkin zuciya da kyawun ayyukan bawa.

Wannan hadisin yana karfafa mahimmancin niyya da aiyuka masu kyau, yana kuma karantar da cewa tsarkin zuciya da kyakkyawan aiki su ne ginshikin karɓuwa a wurin Allah.

09/05/2026

゚viralシfypシ゚

09/05/2026

"Saurara Kaji 🧏"

゚viralシfypシ゚

AMFANIN HAƊIN KAI GUDA GOMAAllah Maɗaukaki ya ce:“ ku yi riƙo da igiyar Allah gaba ɗaya, kada ku rarraba.”— Al-Qur'an 3:...
09/05/2026

AMFANIN HAƊIN KAI GUDA GOMA

Allah Maɗaukaki ya ce:

“ ku yi riƙo da igiyar Allah gaba ɗaya, kada ku rarraba.”

— Al-Qur'an 3:103
Annabin Rahma (saw) ya ce:

“Muminai a cikin soyayya da tausayi da jinƙai kamar jiki guda ne.”

( Sahih al-Bukhari da Sahih Muslim)

Abubuwa goma da Hadin kai yake kawowa :

1. Samun ƙarfi da ɗaukaka

Haɗin kai yana sa al’umma ta zama mai ƙarfi, abin girmamawa da tsaro.

2. Nasara akan maƙiya

Idan mutane s**a haɗu s**a zama tsintsiya maɗaurinki ɗaya, maƙiya ba sa samun damar rarraba su.

3. Yawaitar soyayya da ƙauna

Haɗin kai yana kawar da ƙiyayya, hassada da gaba tsakanin mutane.

4. Sauƙaƙa ayyuka masu wahala

Aiki idan an haɗa hannu ana samun sauƙi da saurin kammalawa.

5. Samun ci gaba a al’umma

Duk wata al’umma mai haɗin kai tana samun bunƙasa a ilimi, tattalin arziki da tsaro.

6. Karfafa addini da gaskiya

Haɗin kai tsakanin masu gaskiya yana taimakawa wajen ɗaukaka addini da yaɗa alheri.

7. Kawo zaman lafiya

Inda akwai haɗin kai ana samun kwanciyar hankali da zaman lafiya.

8. Taimakon juna a lokacin buƙata

Haɗin kai yana sa mutane su riƙa taimakon juna cikin wahala da damuwa.

9. Kariya daga fitina da rikice-rikice

Rarrabuwar kai tana kawo fitina, amma haɗin kai yana hana hakan.

10. Samun yardar Allah

Musulunci ya ƙarfafa haɗin kai da kauce wa sabani

Haɗin kai ginshiƙi ne na ci gaban al’umma da nasararta. Duk inda aka samu haɗin kai, za a samu ƙarfi, zaman lafiya da albarka. Amma rarrabuwar kai tana jawo rauni da koma baya.

Allah ya haɗa kanmu akan gaskiya.

DALILAN SHIGA ALJANNAH1. Tauhidi da Ikh'lasi2. Ciyarwa don Allah3. Kyawawan ɗabi'u4. Dai-daitawa da kyautatawa mutane5. ...
09/05/2026

DALILAN SHIGA ALJANNAH

1. Tauhidi da Ikh'lasi

2. Ciyarwa don Allah

3. Kyawawan ɗabi'u

4. Dai-daitawa da kyautatawa mutane

5. Kauda abin cutarwa/ƙazanta daga hanya

6. Son masu imani don Allah
7. Kunya

8. Ambaton Allah maɗaukaki

9. Kyautatawa maƙobci

10. Godewa Allah kan ni'imarsa

11. Yawan sujjada/sallar nafila

12. Ƙan-ƙan da kai ga Allah

13. Sadar da zumunta

14. Biyayya ga iyaye

15. Karatun Al-ƙur'ani da aiki dashi

16. Umarni da kyakkyawan aiki da hani da mummunan aiki

17. Sauƙaƙawa dabbobi

18. Ambaton Allah bayan sallolin farillah

19. Yima Manzon Allah ﷺ biyayya

20. Haƙuri

21. Gaskiya

22. Kiyaye sallolin farillah

23. Gaishe da mara lafiya

24. Addu'a

25. Yawaita sallama da ciyar da abinchi

26. Koyan Al-ƙur'ani da koyar dashi

27. Yima Manzon Allah ﷺ salati

28. Taimakekeniya akan aikin ƙwarai da tsoron Allah

29. Kira ga tafarkin Allah

30. Kyautatawa Allah zato

Ka yaɗa wannan saƙon don ya zama sadaƙa mai gudana a gareka.

سبحانَك اللهمَّ وبحمدِك أشهَدُ أن لا إلهَ إلّا أنت أستغفِرُك وأتوبُإإل

A koyarwar Musulunci, halal ne kuma ya halatta mutum ya yi barci yana da janaba har zuwa asuba, amma hakan ya saba wa ko...
09/05/2026

A koyarwar Musulunci, halal ne kuma ya halatta mutum ya yi barci yana da janaba har zuwa asuba, amma hakan ya saba wa koyarwar mafificiyar sunnah ta Manzon Allah (SAW).
Ga cikakken bayani dalla-dalla dangane da hukuncin da kuma abin da ya kamata mutum ya yi idan zai kwanta a cikin wannan babi:
1. Halaccin Yin Barci Da Janaba

* Ya halatta: Babu laifi ko zunubi idan mutum ya kwanta barci yana da janaba har gari ya waye, matukar bai fita daga lokacin sallar asuba ba.
* Hujja: An rawaito daga Aisha (RA) cewa: "Manzon Allah (SAW) ya kasance yana yin barci yana da janaba ba tare da ya shafi ruwa ba (wato bai yi wanka ba)" (Hadisin Abu Dawud).

2. Sunnah Kafin Kwanciya Barci (Alwala)

* Yin Alwala: Idan mutum ba zai iya yin wankan janaba ba kafin ya kwanta, sunnah ce mai ƙarfi (Mustahabbai) ya wanke gabansa sannan ya yi alwala irin ta sallar asuba kafin ya kwanta.
* Hujja: Umar bin Khattab (RA) ya tambayi Manzon Allah (SAW) cewa: "Shin ɗayanmu zai iya yin barci yana da janaba?" Manzon Allah (SAW) ya ce: "E mana, idan ya yi alwala zai iya yin barci." (Hadisin Bukhari da Muslim).

3. Haɗarin Kwanciya Har Zuwa Asuba

* Kwadayin Lada: Barci cikin janaba ba tare da alwala ba yana rage samun albarka da kariya ta mala'iku a cikin barci.
* Kurewar Sallar Asuba: Babban hadarin shi ne idan barci ya kwashe mutum har rana ta fito bai yi salla ba. Yin hakan da gangan kuma saboda rago babban zunubi ne.

1. Mafi kyau (Daraja ta ɗaya): Yin wankan janaba kafin a kwanta barci.
2. Na tsakiya (Daraja ta biyu): Wanke gaba da yin alwala kafin a yi barci, sannan a yi wankan idan asuba ta yi.
3. Wanda aka halatta (Amma ba a so): Yin barci kai tsaye ba tare da wanka ko alwala ba, matukar za a tashi a yi wanka kafin lokacin salla ya fita.

Kana bukatar Lada Mai yawa kyauta Ka Turawa Yan Uwa Dan su anfana Kai ma Kayi Sadakah 🙏

LOKUTA (16) WANDA ALLAH YAKE AMSA ADDU'O'IN BAYINSA.01- Ko wane daya bisa uku (1/3) na dare ana amsa addu'a kamar yadda ...
09/05/2026

LOKUTA (16) WANDA ALLAH YAKE AMSA ADDU'O'IN BAYINSA.

01- Ko wane daya bisa uku (1/3) na dare ana amsa addu'a kamar yadda hadisi ya nuna hakan.

02- Ana amsa addu'a a tsakanin kiran sallah da tayar da iƙama, kamar yadda hadisi ya nuna hakan.

03- Ana amsa addu'a a ƙarshen kiran kowacce sallah ta farilla.

04- Ana amsa addu'a ya yin saukar ruwan sama, kamar yadda hadisai s**a nuna hakan.

04- Ana amsa addu'a a lokacin da aka yi sahu-sahu za a tafi yaƙin ɗaukaka kalmar allah ﷻ da kuma ya yin da aka yi sahun kafin a fara yaƙin, kamar yadda hadisai s**a nuna hakan.

05- Ana amsa adu'a a ranar juma'a a wani lokaci musamman ma bayan sallar juma'ar zuwa faɗuwar rana.

06- Ana amsa addu'a ya yin da za a sha ruwan zamzam tare da kyakykyawar niyyah, kamar yadda hadisi ya nuna.

07- Ana amsa addu'a a cikin sujjada, kamar yadda hadisi ya tabbata a cikin hadisi.

08- Ana amsa addu'ar wanda ya kwaikwayi irin addu'ar da Annabi ﷺ Yunusa ya yi, it ace: “La'ilaha illa anta subhanaka inni kuntu minaz zalimin.”

09- Ana amsa addu'a a cikin tahiyyar sallah ta ƙarshe, kamar yadda hadisi ya yi bayani a kan hakan.

10- Idan Musulmi ya yiwa ɗan uwansa Musulmi addu'a ba tare da ya sani ba, ita ma karɓaɓɓiyar addu'a ce, kamar yadda hadisi ya tabbatar da hakan.

11- Addu'ar ranar arfa ita ma karɓaɓɓiya ce, kamar yadda hadisi ya tabbata a kan hakan.

12- Idan musulmai s**a haɗu wasu suna addu'a wasu suna cewa amin, ita ma wannan addu'ar karɓaɓɓiya ce, kamar yadda hadisi ya yi bayani a kan hakan.

13- Ana amsa addu'a a ya yin da mutum ya fuskanci Allah ﷻ da tsarkin zuciya, wato iklasi mai ƙarfi

14- Addu'a bayan an gama alwala, ita ma karɓaɓɓiya ce, kamar yadda hadisi ya yi bayani a kan hakan.

15. Lokacin da aka gama karatun Alqur'ani ko wa'azi ko wata koyarwa ta ilimi. Shima lokacin karbar addu'a ne.

16. Lokacin da akaji zakara yayi chara. Shima lokacin amsar
addu'a ne kamar yazo a hadisi.

Allah ya amsa dukkan buqatun mu na alkhairi, na sharri kuma ya maida mana su na alkhairi.

09/05/2026

MUHAMMADUR'RASULULLULAH' SALLALLAHU'ALAIHIWASALLAMMM 🙏
゚viralシfypシ゚

*KA NEMI KARIYAR ALLAH DAGA ABUBUWA HUƊU*Professor Mansur Isa Yelwa Hafizuhullah🥀🥀🥰🥰"Anso idan mutum ya gama tahiyyar ƙa...
07/05/2026

*KA NEMI KARIYAR ALLAH DAGA ABUBUWA HUƊU*Professor Mansur Isa Yelwa Hafizuhullah🥀🥀🥰🥰

"Anso idan mutum ya gama tahiyyar ƙarshe a sallarsa, ya nemi tsari da kariyar Allah daga sharrin abubuwa guda huɗu, domin sune abubuwa mafi sharri a gareshi a rayuwarsa da kuma mutuwarsa"

"Manzon Allah ﷺ, yace: idan ɗayanku ya gama tahiyyar ƙarshe, to ya nemi tsarin Allah daga abubuwa guda huɗu:"
Sahih Muslim

Abubuwan nan kuwa sune kamar haka a zaiyyane:

💧Daga azãbar (wutar) jahannama.
💧Da kuma azabtar cikin ƙabari.
💧Da fitinar rayuwa da mutuwa.
💧Da kuma sharrin ad-dajjal (dujal).

"Muna roƙon Allah Subhanahu Wa Ta'ala da ya tsaremu daga sharrin waɗannan abubuwan, da kuma waɗanda suke

Sunnah Academic
Sautin Gaskiya

AZKAR Na SAFE GUDA BIYU MASU GIRMAN LADAWAƊANDA YA DACE KA LIZIMTA A KULLUM1. اللَّهُمَّ أَنْتَ رَبِّي لَا إِلَهَ إِلَّا...
07/05/2026

AZKAR Na SAFE GUDA BIYU MASU GIRMAN LADA
WAƊANDA YA DACE KA LIZIMTA A KULLUM

1.
اللَّهُمَّ أَنْتَ رَبِّي لَا إِلَهَ إِلَّا أَنْتَ، خَلَقْتَنِي وَأَنَا عَبْدُكَ، وَأَنَا عَلَى عَهْدِكَ وَوَعْدِكَ مَا اسْتَطَعْتُ، أَعُوذُ بِكَ مِنْ شَرِّ مَا صَنَعْتُ، أَبُوءُ لَكَ بِنِعْمَتِكَ عَلَيَّ، وَأَبُوءُ لَكَ بِذَنْبِي فَاغْفِرْ لِي فَإِنَّهُ لَا يَغْفِرُ الذُّنُوبَ إِلَّا أَنْتَ

Allahumma Anta Rabbi la ilaha illa Anta, khalaqtani wa ana 'abduka, wa ana 'ala 'ahdika wa wa'dika mastata'tu, a'udhu bika min sharri ma sana'tu, abu'u laka bini'matika 'alayya, wa abu'u laka bidhanbi faghfir li fa-innahu la yaghfirudh-dhunuba illa Anta. (Sau ɗaya a safe da yamma)
-
Manzon Allah (SAW) ya ce “Duk wanda ya yi wannan addu’a da safe da yamma yana mai yaƙini da ita, idan ya mutu kafin maraice, to yana ɗaya daga cikin mutanen Aljanna. Idan kuma ya yi addu’ar da yamma yana mai yaƙini da ita, idan ya mutu kafin asuba, to yana ɗaya daga cikin mutanen Aljanna.” (Sahih Bukhari, 6306)

2.
سُبْحَانَ اللَّهِ وَبِحَمْدِهِ
Subhanallahi wa bihamdihi. (Sau ɗari 100)
-
Manzon Allah (SAW) ya ce “Duk wanda ya ce 'Subhanallahi wa bihamdihi' sau ɗari za a kankare masa zunubansa koda kuwa sun kai yawan kumfar teku.” (Sahih Bukhari, 6405)

Allah ya ba mu ikon lizimtar waɗannan azkar don samun gafararSa da kuma kyakkyawan ƙarshe.

Abdullahi Aliyu Boza ✍️

Address

Sabon Gari Ward
Gashua
671101

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when ABUH Farhan BExclusive Sunnah posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share