10/05/2025
Sen. Rabi'u Musa Kwankwaso, Ph.D., FNSE, ya karɓi digirin digirgir na girmamawa daga Jami’ar Kimiyya da Fasaha ta Aliko Dangote, waccce akafi sani da Kano University of Science and Technology, Wudil. Ragowar wanda aka bawa sun haɗa da:
Alhaji Dahiru Barau Mangal
Engr. Prince Arthur Ikpechukwu Eze, OFR
Barr. Ahmad Adeniyi Raji, SAN
Alhaji Mustapha Ado Muhammad
Jagoranmu abin alfaharinmu shine wanda yayi:
1. Shugaban ƙungiyar ɗaliban ta KADPOLY
2. Tsohon ma'aikacin gwamnati tsahon shekaru 17
3. Mataimakin shugaban majalisar wakilai ta ƙasa (1992)
4. Ɗan komitin gyaran kundin mulkin Nigeria (1994-1995)
5. Tsohon gwamnan jihar Kano sau biyu (1999-2003 da 2011-2015)
6. Babban ministan tsaro Nigeria (2003-2007)
7. Ɗan komitin sulhun Dafur da Somalia (2003-2007)
8. Sanatan ƙasar Nigeria (2015-2011)
9. Takarar zangon farko na tsayawa shugaban Nigeria (2015 da 2019)
10. Jagoran NNPP kuma ɗan takararta na shugaban ƙasa (2023)
11. Shine wanda ya ƙirƙiro tagwayen jami'o'in nan na Kano KUST (2000 & 2012)
12. Shine babu gwamnati yakai manyan Scholars su 370 zuwa ƙasashen waje na Dubai, India and Sudan ta gidauniyar Kwankwasiyya
13. Ya kuma kafa ƙungiyar nan ta Kwankwasiyya mai albarka.
A jawabinsa, yace yayi abubuwa da yawa na cigaban al'umma, amma yana so jama'a su tuna dashi a matsayin sa na wanda ya ƙirƙiro tagwayen jami'o'i a Kano. Sannan ya sadauƙar da digirin ga al'ummar Kano, Nigeria da kuma masu son cigaban jami'a a duk inda suke. Madugu kenan, Allah Ya kara lafiya, nisan kwana da ɗaukaka.
Ni dai Jagora ya burgeni ta hanyar kai matasa 370 zuwa ƙasar waje, ku kuma ta ina yafi burgeka?
Arewa Ayau.