Ziyau Adamu

Ziyau Adamu I'm from Sardauna local government, Taraba state, Nigeria. Ni assalin Haifefin Gembu

07/09/2026

Gaskiya ne

Kusaurari 👂

WANNAN BAUTAR GUMAKAN JESUS DA MAHAIFIYARSA SHINE MA'ANAR ADDININ  KIRISTOCI MAI SUNA CHRISTIANITY . Kiristoci suna koya...
07/09/2026

WANNAN BAUTAR GUMAKAN JESUS DA MAHAIFIYARSA SHINE MA'ANAR ADDININ KIRISTOCI MAI SUNA CHRISTIANITY .

Kiristoci suna koya ma yaransu yadda zasu bautama Jesus wanda s**a ce shine Allahn su tun suna kananan yara har su girma .

Kuma suna koya musu yadda zasu bautama mahaifiyar Jesusmai suna Maryam tun suna kananan yara .

Sun kirkiro mutum mutumin Jesus da mahaifiyarsa a matsayin gumakan katako ko azurfa domin a rika bauta musu a matsayin Allolinsu guda biyu.

Wannan bautar gumaka da kiristoci keyi ya saba ma abinda ke rubuce acikin bible dinsu acikin Exodus 20 aya ta 1-5. Baibul yace kada a bauta ma gumaka ko ayi musu durkuso . Kuma kada a hada bautan Allah da kowa .

Kiristoci sun ki biyayya ga wannan umurni daga Allah dake cikin bible dinsu . Soboda haka kiristoci mushirikkai ne masu bautan wanin Allah .
Sun yiwa Allah kishiyoyi acikin abinda ya halitta .

Allah shi kara tsaremu daga bin addinin karya . Allah ya ceto kiristoci daga wannan addinin mai suna Christianity wanda ma ba sunansa acikin bible .
Musulunci shine addinin gaskiya wanda Allah ya yarda da shi .

Saboda haka duk wanda ya yarda ya shiga cikin addinin kirista ,abinda za a fara koya masa shine yadda zai fara bautan gumaka .

Hussieni Mabera

Wani Gini Ya Ruguje A Yankin Wuse Zone 4 Dake Abuja A Daren NanA halin yanzu, jami’an hukumar kashe gobara ta FCT suna g...
07/09/2026

Wani Gini Ya Ruguje A Yankin Wuse Zone 4 Dake Abuja A Daren Nan

A halin yanzu, jami’an hukumar kashe gobara ta FCT suna gudanar da aikin ceto a wurin. An kuma jibge motocin ɗaukar marasa lafiya guda uku a wurin.

Tun kafin ginin ya rushe Hukumar Kula da Tsara Ci gaban Birnin Abuja (Development Control) ta rufe ginin yau, tare da umartar mutanen da ke ciki da su fice.

AMFANI 30 NA YIN SADAKA A DUNIYA DA LAHIRASadaka ba iya  kuɗi kaɗai ba ce; abinci, tufafi, taimako, ilimi, ruwa, gina ma...
07/09/2026

AMFANI 30 NA YIN SADAKA A DUNIYA DA LAHIRA

Sadaka ba iya kuɗi kaɗai ba ce; abinci, tufafi, taimako, ilimi, ruwa, gina masallaci, taimakon marayu da marasa ƙarfi, har ma da kyakkyawar magana na iya zama sadaka idan an yi su saboda Allah.

Amfaninta a duniya

1. Tana kawo albarka a cikin dukiya.
Allah yana maye gurbin abin da aka bayar saboda Shi.
2. Tana zama sanadin samun arziki.
Allah Ya ce: “Duk abin da kuka ciyar, Shi ne zai maye gurbinsa.” (Saba’i: 39)
3. Tana kawar da bala’o’i da musibu da yardar Allah.
4. Tana taimakawa wajen samun lafiya da sauƙin rayuwa.
5. Tana tsarkake zuciya daga rowa da son duniya.
6. Tana ƙara soyayya tsakanin mutane.
7. Tana rage talauci da buƙata a cikin al’umma.
8. Tana taimaka wa marayu da zawarawa su samu abin dogaro.
9. Tana taimaka wa ɗalibai da masu neman ilimi.
10. Tana taimakawa wajen samar da abinci da ruwan sha ga mabukata.
11. Tana ƙarfafa zumunci, musamman idan an bai wa dangi.
12. Tana sa mutum ya ji daɗin taimakon wasu kuma ta ƙara masa tausayi.
13. Tana kare al’umma daga aikata laifuka da matsanancin talauci ke iya haifarwa.
14. Tana gina kyakkyawan suna ga mai bayarwa, saboda mutane suna tuna mai alheri da addu’a.
15. Tana zama sadaka jariya idan abin da aka bayar ya ci gaba da amfanar mutane.

Amfaninta a lahira

16. Tana zama dalilin samun lada mai girma.
17. Tana zama kaffarar zunubai, musamman idan an yi ta da ikhlasi tare da tuba.
18. Tana zama kariya daga azabar Allah.
19. Tana zama inuwa ga mutum a ranar Alƙiyama, kamar yadda hadisi ya zo cewa sadaka tana zama inuwa ga mai ita.
20. Tana ƙara nauyin kyawawan ayyuka a Mizani.
21. Tana daga darajar mutum a wurin Allah.
22. Tana taimakawa wajen samun rahamar Allah.
23. Tana zama dalilin shiga Aljanna, tare da imani da sauran ayyukan ƙwarai.
24. Tana zama abin farin ciki ga mutum bayan mutuwarsa, idan ta kasance sadakar jariya.
25. Ladan sadakar jariya na iya ci gaba bayan mutuwa.
Annabi ﷺ ya ce idan ɗan Adam ya mutu, ayyukansa suna yankewa sai abubuwa uku, daga cikinsu akwai sadaka jariya.
26. Tana zama dalilin samun addu’ar waɗanda aka taimaka.
27. Tana kusantar da bawa zuwa ga Allah, domin tana nuna imani da dogaro da abin da Allah Ya tanada.
28. Tana koya wa mutum ikhlasi da sadaukarwa, musamman idan ya bayar ba tare da neman yabo ba.
29. Tana zama jarin da ba ya lalacewa.
Allah Ya ce:

“Duk wani alheri da kuka gabatar wa kanku, za ku same shi a wurin Allah.” (Al-Baqarah: 110)
30. Tana zama abin da mutum zai yi farin ciki da shi a ranar da dukiya da ‘ya’ya ba za su amfane shi ba, domin abin da ya bayar saboda Allah shi ne zai same shi a lahira.

Kada ka raina ƙaramar sadaka. Naira 100 da aka bayar da ikhlasi na iya zama mafi girma a wurin Allah fiye da miliyoyin da aka bayar don neman suna.

Ka yi sadaka yau—domin abin da ka bayar shi ne abin da ka tura wa lahirarka.
Shin kana yin sadaƙa ?
Sadaƙa maganin musiba.

Idan social media ta ci gaba da lalacewa, tare da yaɗuwar batsa, bayyana tsiraici da abubuwan da ba su dace da tarbiyya ...
07/09/2026

Idan social media ta ci gaba da lalacewa, tare da yaɗuwar batsa, bayyana tsiraici da abubuwan da ba su dace da tarbiyya ba, shin menene makomar yaran da za mu haifa a nan gaba?

Ta wace hanya za mu haɗa kai domin tsaftace social media?

Amsa:

Mutanen da ke ƙirƙirar content na zinace-zinace, rungume-rungume, batsa da bayyana tsiraici, sau da yawa suna samun ƙarfin gwiwar ci gaba ne saboda yadda muke mu’amala da abubuwan da suke wallafawa.

Mu ne muke musu likes, comments da shares.
Wannan yana ƙara musu reach da engagement, wanda hakan ke sa su ga cewa abin da suke yi yana samun karɓuwa, don haka su ƙara ci gaba.

Saboda haka, idan mutum ya wallafa abin da ba shi da amfani—kamar zagi, lalata tarbiyya, batsa ko cin mutunci—kar ku yi masa like, kar ku yi comment, kuma kar ku yi sharing.

Ku yi scrolling zuwa gaba, ko kuma ku yi reporting account ɗinsa

Ta wannan hanya ne za mu iya taimakawa wajen tsaftace social media.

Idan kuwa muka ci gaba da tallafa wa irin waɗannan abubuwan ta hanyar engagement, watarana za mu iya fuskantar wani yanayi da social media zata zamo ɗaya daga cikin abubuwan da ke lalata tarbiyyar ƙannenmu da ’ya’yan da ke tasowa.

Tsaftace social media ba aikin mutum ɗaya ba ne. Alhakinmu ne gaba ɗaya.

امر بالمعروف و نهى عن المنكر

Alhassan Mai Lafia

Alhamdulillahillazi bi ni'imatihi tatimmul salihat
07/09/2026

Alhamdulillahillazi bi ni'imatihi tatimmul salihat

Matatar Man Dangote ta ƙaddamar da hannun jari na IPO na Naira tiriliyan 2.15 kan Naira 525 ga kowane hannun jariMatatar...
07/09/2026

Matatar Man Dangote ta ƙaddamar da hannun jari na IPO na Naira tiriliyan 2.15 kan Naira 525 ga kowane hannun jari

Matatar man Dangote ta ƙaddamar da wani shirin sayar da hannun jari karo na farko ga al'umma , wanda ta yi wa laƙabi da IPO na Naira tiriliyan 2.15, domin tara jari don faɗaɗa ayyukan.ta tare da bai wa al'umma damar mallakar hannun jari a kamfanin.

Babban Daraktan Kamfanin, Alhaji Aliko Dangote, ya ce hannun jarin zai bai wa ‘yan Najeriya da sauran ‘yan Afirka damar sayen hannun jari a matatar mai ƙarfin tace ganga dubu 700,000 a kowace rana.

Shirin ya ƙunshi hannun jari guda biliyan 4.1, inda za a sayar da kowane hannun jari kan Naira 525, yayin da mafi ƙarancin adadin da mutum zai iya saya shi ne hannun jari 10, wanda darajarsa ta kai Naira 5,250.

“Wannan IPO ne na jama'a. Babu wani bambanci kan wanda zai iya mallakar hannun jarin,” in ji Dangote.

A cewarsa, matatar man, wacce ke yankin Lekki Free Zone na da ƙarfin tace ganga 700,000 a kowace rana.

Dangote ya ce wannan IPO, wanda shi ne karon farko da matatar ta fara sayar da hannun jari ga jama'a tun bayan ƙaddamar da ita a shekarar 2023, shi ne mafi girma a Afirka.

Ya bayyana cewa wannan mataki zai bai wa mutane da dama damar shiga cikin ci gaban kamfanin.

Ana sa ran shirin zai samar da ƙarin jari domin shirin faɗaɗa matatar, tare da ƙara yawan masu hannun jari a kamfanin.

Daily Nigeria Hausa

ABIN FARINCIKI:Yara Musulmanai ’Yan Kabilar Igbo Ke Koyan Karatun Alƙur’ani a Wata Makaranta a Jahar EnuguAn bayyana hot...
07/09/2026

ABIN FARINCIKI:Yara Musulmanai ’Yan Kabilar Igbo Ke Koyan Karatun Alƙur’ani a Wata Makaranta a Jahar Enugu

An bayyana hotunan ’yan yara Musulmanai ’yan asalin Igbo suna karatun Alƙur’ani a wata makarantar Islamiyya da Markaz a jihar Enugu.

Wannan lamari na nuna yadda koyarwa da karatun Alƙur’ani ke ci gaba da bunƙasa tsakanin al’ummar Musulmi a yankin Kudu maso Gabashin Najeriya.

Allah Ya ƙara musu ilimi, Ya sa Alƙur’ani ya zama haske da shiriya a rayuwarsu. 🤲📖
Rahotanni a kafafen sada zumunta sun kuma taɓo batun yara Musulmanai ’yan Igbo da s**a kammala karatun Alƙur’ani a Enugu. �

07/09/2026

Wani bayan da Sheik Nurul Khalid yakara akan yaronsa

Ameeeen Ya Hayyu Ya Qayyum 🤲
07/09/2026

Ameeeen Ya Hayyu Ya Qayyum 🤲

Address

Mamalele Street
Gembu
M

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Ziyau Adamu posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Shortcuts

Share