Ya'u Buba G ventures

Ya'u Buba G ventures Business

31/03/2025

Na samu kiraye kiraye daga al’ummar yankina da ‘yan Najeriya da dama dangane da mummunan kisan gilla da aka yi wa bayin Allah da basu ji ba basu gani ba a Jihar Edo. Ina Allah wadai da wannan ta’asa, kuma na yi tir da wannan kisan gilla da aka yi wa wadannan bayin Allah.

Ina kira ga hukumomin tsaro da su gaggauta daukar matakin k**a wadannan azzalumai tare da tabbatar da cewa an hukunta su daidai da girman laifin da s**a aikata.

Najeriya ƙasa ce mai yalwar kabilu da addinai daban-daban. Saboda haka, dole ne mu zauna lafiya da juna, mu rungumi juna a matsayin ‘yan uwa domin ci gabanmu da zaman lafiyarmu.

Allah Madaukakin Sarki ya jikan wadanda s**a rasa rayukansu, ya ba su Aljannatul Firdaus. Allah ya ba iyalansu hakuri da juriya.

Insha Allah, za mu tabbatar da cewa an yi adalci, kuma wadannan azzalumai ba za su tsira ba.

Zan kuma gabatar da kudiri a zauren Majalisar Dattawa kan wannan lamari.

- Sanata Barau Ibrahim Jibrin
Mataimakin Shugaban Majalisar Dattijai

Address

NO 21 Pantami Quarters
Gombe State

Telephone

08035680373

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Ya'u Buba G ventures posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share