Tijjaniyya Media News

Tijjaniyya Media News Tijjaniya Media News
Spreading Light • Promoting Unity • Inspiring Spiritual Growth. Islamic | Educational | Sufi | Community Awareness.

Visit: www.tijjaniyamedia.com
Follow us for authentic updates, teachings & spiritual insights.

SANADIYAR SHEIKH IBRAHIM INYASS (RTA) NE AKA SAKE BA MAULIDI MUHIMMIN MATSAYI A NAJERIYAAna ruwaito cewa Sheikh Ibrahim ...
25/08/2026

SANADIYAR SHEIKH IBRAHIM INYASS (RTA) NE AKA SAKE BA MAULIDI MUHIMMIN MATSAYI A NAJERIYA

Ana ruwaito cewa Sheikh Ibrahim Inyass (RTA) yana daga cikin manyan malaman da s**a taka muhimmiyar rawa wajen ganin an ba da muhimmanci ga ranar Maulidin Annabi Muhammad (SAW) a Najeriya.

Bayan Najeriya ta samu ’yancin kai a shekarar 1960, Sheikh Ibrahim Inyass (RTA) ya ziyarci Najeriya, inda ya gana da wasu daga cikin manyan shugabannin ƙasar, ciki har da Firayim Minista na farko, Sir Abubakar Tafawa Balewa.

A cewar wannan ruwaya, Sheikh Ibrahim Inyass (RTA) ya jaddada muhimmancin girmama ranar haihuwar Annabi Muhammad (SAW), inda ya shawarci Firayim Minista Tafawa Balewa cewa, kasancewarsa Musulmi, ya kamata a sanya ranar Maulidi ta zama ranar hutu ta ƙasa, kamar yadda ake ba da hutu a wasu muhimman ranakun addini.

Wasu bayanan tarihi da binciken ilimi sun kuma ambaci cewa Sheikh Ibrahim Inyass ya tattauna da Firayim Ministan Najeriya game da muhimmancin bikin haihuwar Annabi da kuma buƙatar a ba ranar hutu na gwamnati.

Daga baya, Maulidi ya kasance cikin ranakun da gwamnatin Najeriya ke amincewa da su a matsayin hutun jama'a. Wannan al’ada ta ci gaba har zuwa yau, inda Gwamnatin Tarayya ke ayyana ranar Maulidi a matsayin hutun ƙasa duk shekara.

Saboda haka, idan ana magana kan tarihin Maulidi a Najeriya, ya dace a tuna da gudummawar manyan malamai da shugabannin ƙasar da s**a taka rawa wajen tabbatar da girmama wannan rana.

Allah Ya saka wa Sheikh Ibrahim Inyass (RTA) da sauran malamai da shugabannin da s**a yi ƙoƙari wajen girmama Manzon Allah Muhammad (SAW) da mafificin alheri. Allah Ya ƙara mana soyayyar Manzon Allah (SAW), Ya ba mu ikon bin Sunnarsa da kyawawan ɗabi’unsa, Ya zaunar da zaman lafiya da haɗin kai a Najeriya, Ya albarkaci ƙasarmu da al’ummarta. Amin ya Rabbal Alamin.

KYAWAWAN HOTUNA: Sharifiya Malama Aisha Nyass Ta Jagoranci Taron Mauludi Da Addu'a A Ƙasar Senagal. Allah Ya Biya Bukata...
22/08/2026

KYAWAWAN HOTUNA: Sharifiya Malama Aisha Nyass Ta Jagoranci Taron Mauludi Da Addu'a A Ƙasar Senagal. Allah Ya Biya Bukatan Mu. Amiin

RASUWAR KHALIFA SHEIKH MUHAMMADUL EID AT-TIJANI AT-TAMASINIInnā lillāhi wa innā ilaihi rājiʿūn.Allah Ya karɓi rayuwar Kh...
20/08/2026

RASUWAR KHALIFA SHEIKH MUHAMMADUL EID AT-TIJANI AT-TAMASINI

Innā lillāhi wa innā ilaihi rājiʿūn.

Allah Ya karɓi rayuwar Khalifa Sheikh Muhammadul Eid At-Tijani At-Tamasini, wanda yake daga cikin manyan shugabannin Tijjaniyya, kuma Sheikh na Zawiyar Tamasini.

Rasuwar tasa babban rashi ce ga ‘yan uwa da almajiran Ɗariƙar Tijjaniyya, musamman waɗanda suke da alaƙa da Tamasini da kuma Ain Madhi.

Tarihin Tamasini da Ain Madhi

Muhimmancin matsayin Tamasini a cikin tarihin Ɗariƙar Tijjaniyya yana da alaƙa da Sidi Al-Hajj Ali At-Tamasini, babban Khalifan Sheikh Ahmad At-Tijani (RA).

Bayan wafatin Sheikh Ahmad At-Tijani, Sidi Al-Hajj Ali At-Tamasini ya aiwatar da wasiyyar da Sheikh Ahmad At-Tijani ya yi masa game da ‘ya’yansa. Ya tafi da Sidi Muhammad Al-Kabir At-Tijani da Sidi Muhammad Al-Habib At-Tijani daga Fes zuwa yankin Ain Madhi, domin su zauna a ƙasar da ta dace da yanayin rayuwarsu da kuma ci gaban Ɗariƙar.

An ruwaito cewa Sheikh Ahmad At-Tijani ya ce game da ‘ya’yansa:

«أولادي لا تليق بهم إلا الصحراء»

Ma’ana: “‘Ya’yana ba ta dace da su sai Sahara.”

Wannan wasiyya ta taka muhimmiyar rawa wajen komawar iyalan Sheikh Ahmad At-Tijani zuwa Ain Madhi da kuma ƙarfafa tushen Ɗariƙar Tijjaniyya a wannan yanki.

Matsayin Khalifancin Tamasini

Tamasini ta kasance ɗaya daga cikin manyan cibiyoyin tarihi na Ɗariƙar Tijjaniyya. Bayan rasuwar Sidi Al-Hajj Ali At-Tamasini a shekara ta 1844, an ci gaba da gadon wannan matsayi ta zuriyarsa. Majiyoyin tarihi sun bayyana cewa ya zaɓi Sidi Muhammadul Eid a matsayin wanda zai gaje shi a shugabancin Tamasini.

A tsarin tarihi na Tijjaniyya, an samu manyan cibiyoyi uku masu muhimmanci: Ain Madhi, inda zuriyar Sheikh Ahmad At-Tijani suke da matsayi na musamman; Fes, cibiyar da ta kasance muhimmiyar gida ga zuriyar Sheikh; da Tamasini, wadda ta shahara da matsayin khalifancin zuriyar Sidi Al-Hajj Ali At-Tamasini.

Saboda haka, rasuwar Sheikh Muhammadul Eid At-Tamasini ba wai kawai rasuwar wani malami ba ce, amma rasuwar wani babban mutum da ke da alaƙa da dogon tarihin khalifancin Tamasini da tarihin Ɗariƙar Tijjaniyya.

Dangantakar Ain Madhi da Tamasini

Dangantakar Ain Madhi da Tamasini tana da tushe mai zurfi a tarihin Ɗariƙar. Sidi Al-Hajj Ali At-Tamasini ya kasance babban mutum a tarihin kafa da kare matsayin zuriyar Sheikh Ahmad At-Tijani a Ain Madhi.

A yau ma, ana ci gaba da kallon Tamasini a matsayin ɗaya daga cikin manyan cibiyoyin tarihi da ruhaniya na Tijjaniyya, musamman saboda gadon zuriyar Sidi Al-Hajj Ali At-Tamasini da kuma tarihin khalifancin da ya samo asali daga gare shi.

Ta’aziyya

Muna miƙa ta’aziyyarmu ga iyalan marigayi Khalifa Sheikh Muhammadul Eid At-Tamasini, da zuriyar Sidi Al-Hajj Ali At-Tamasini, da ‘yan uwa, almajirai da ɗaukacin mabiya Ɗariƙar Tijjaniyya.

Muna roƙon Allah Maɗaukakin Sarki Ya gafarta masa, Ya jiƙansa da rahamarSa, Ya sanya shi cikin bayinSa salihai, Ya ɗaukaka darajarsa, Ya kuma ba iyalansa da almajiransa haƙurin jure wannan babban rashi.

Allah Ya gafarta masa, Ya sa Aljanna ce makomarsa. Āmīn, Yā Rabbal ʿĀlamīn.

Shugaban Darikar Tijjaniyya na Duniya Sharif Ali bel Arabi R.T.A,ya Sauka a Nijeriya Domin Halartar Gagarumin Maulidin S...
07/08/2026

Shugaban Darikar Tijjaniyya na Duniya Sharif Ali bel Arabi R.T.A,ya Sauka a Nijeriya Domin Halartar Gagarumin Maulidin Shehu Ahmadu Tijjani R.T.A da za a Gudanar a Birnin Kano.

Shugaban Darikar ya samu Tarba daga Sarkin Kano na 15 Alh. Aminu Ado Bayero,da Khalifan Tijjaniyya na Nijeriya Sayyadi Ibrahim Sheikh Dahiru Usman Bauchi da Sauran yan'uwa musulmai masoya.

Allah yasa ayi taro lafiya

Wurin da Annabi ﷺ Ya Yi Sujadar Godiya ga AllahWannan shi ne Kogon Sujada (Gharus-Sajdah), wanda ake kira kuma Kogon Ban...
05/08/2026

Wurin da Annabi ﷺ Ya Yi Sujadar Godiya ga Allah

Wannan shi ne Kogon Sujada (Gharus-Sajdah), wanda ake kira kuma Kogon Banu Haram. A nan ne Annabi Muhammad ﷺ ya yi sujadar godiya ga Allah bayan Mala'ika Jibrilu (AS) ya kawo masa bushara cewa Allah Maɗaukakin Sarki ba zai kunyata shi game da al'ummarsa ba. An kuma ruwaito cewa Annabi ﷺ ya yi sallar raka'a biyu a wannan wuri a lokacin Yaƙin Khandaq.

Kogon yana kan Dutsen Sala'a (Jabal Sala') a Madina, kusa da Masallacin Banu Haram. An ruwaito cewa Sayyidina Umar bn Abdul'aziz (RA) ya gina kubba da masallaci a wurin da Annabi ﷺ ya yi salla, kuma shugabanni bayan sa s**a ci gaba da kula da wurin har zuwa zamanin Daular Usmaniyya.

Wannan ya nuna girman matsayin sujada a wajen Allah, domin Annabi ﷺ ya yi ta ne a matsayin godiya ga wannan babbar bushara. Saboda haka, sujada tana daga cikin manyan hanyoyin kusantar Allah Maɗaukakin Sarki.

Allah Ya ba mu albarkar Annabi Muhammad ﷺ, Ya karɓi ibadunmu, Ya sanya mu cikin masu cin moriyar cetonsa a ranar Alƙiyama. Āmīn Yā Rabbal-'Ālamīn.

Fityanu Islamic Centre
05 August, 2026

Cikakken Karatun Fassarar Littafin Shama'ilul Muhammadiyya Wanda Sheikh Imam Junaid Abubakar Ya Gabatar Har Karshen Litt...
02/08/2026

Cikakken Karatun Fassarar Littafin Shama'ilul Muhammadiyya Wanda Sheikh Imam Junaid Abubakar Ya Gabatar Har Karshen Littafin.

Shamā'ilul Muḥammadiyyah littafi ne na hadisan da Imam Abu Isa al-Tirmidhi ya tattara, wanda ke bayani game da siffofi, ɗabi'u, halaye, ibada da rayuwar yau da kullum ta Manzon Allah ﷺ.

Manufar littafin ita ce ta sa Musulmi su ƙara sanin Manzon Allah SAW, su ƙaunace shi, sannan su yi koyi da kyawawan halayensa da sunnarsa.

Domin sauraro/saukewa👇👇⬇️

https://fityanumedia.com/profile/audio/sheikh-imam-junaidu-abubakar/shama-ilul-muhammadiyya

*Join Our Site For More Updates:

🌍 *Website:
https://fityanumedia.com/

Wannan Shi Ne Kabarin Sayyidatuna Asma'u Yar Sayyiduna Abubakar As-Ṣiddīq RTA (Zātun-Niṭāqayn) Wannan shi ne kabarin Say...
01/08/2026

Wannan Shi Ne Kabarin Sayyidatuna Asma'u Yar Sayyiduna Abubakar As-Ṣiddīq RTA (Zātun-Niṭāqayn)

Wannan shi ne kabarin Sayyida Asma'u bint Abu Bakr As-Siddiq RTA da ke makabartar Ma'alah a Makkah.

Asma'u RA ta kasance 'yar Sayyidina Abu Bakr As-Siddiq, kuma 'yar'uwar Uwar Muminai Sayyida A'isha RA. Ta taka muhimmiyar rawa a hijirar Manzon Allah ﷺ zuwa Madinah, inda ta yaga ɗamararta gida biyu domin ɗaure kayan tafiya. Saboda haka aka yi mata laƙabi da Zātun-Niṭāqayn (Mai Ɗamarar Biyu).

Allah Ya yarda da ita da sauran Sahabban Manzon Allah ﷺ. Amiin Yaa ALLAH

Fityanu Islamic Centre
August 01, 2026

Martani Kan Shigar Malamai SiyasaMalam Phantami ya kira Prof Maqari. jahilin addini bayan Prof. ya ce:«"Bai kamata malam...
31/07/2026

Martani Kan Shigar Malamai Siyasa

Malam Phantami ya kira Prof Maqari. jahilin addini bayan Prof. ya ce:

«"Bai kamata malamin addini ya shiga siyasa ba. Idan kuwa zai shiga, ya ajiye matsayin malanta a gefe, sannan ya sanya rigar ɗan siyasa."»

Bayan wannan furuci na Prof., sai na ga ana tattaunawa da Phantami game da shigarsa siyasa a matsayinsa na malamin addini. Sai ya ce duk wanda ya ce kada malami ya shiga siyasa, jahilin addini ne. Ya kafa hujja da faɗin Annabi Yusuf (A.S.):

«﴿اجعل لي على خزائن الأرض إني حفيظ عليم﴾»

Sannan ya kawo Hadisin Manzon Allah (ﷺ):

««كانت بنو إسرائيل تسوسهم الأنبياء»»

A ganina, abin da Prof. ya hango kenan yake bayyana. Domin istidlalin da aka yi da labarin Annabi Yusuf (A.S.) da wannan Hadisi ba ya nuna cewa za a daidaita su da irin ƙazamar siyasar da ake yi a wannan zamani. Wannan yana nuna kamar ba a fahimci ma'anar ayar da Hadisin yadda ya kamata ba kafin a jingina su da yanayin siyasar yau.

Akwai irin tasiri (capacity) da mutum zai iya samu ba tare da ya shiga siyasa kai tsaye ba, amma ya fi ɗan siyasa tasiri. Hasali ma, 'yan siyasa su ne za su nemi goyon bayansa.

Misali, a Jihar Katsina akwai Alhaji Dahiru Barau Mangal. Ba ɗan siyasa ba ne, amma duk wani ɗan siyasa da ke son samun nasara yana ƙoƙarin neman goyon bayansa. Saboda irin tasirin da yake da shi, abin da ya bayyana wa talakawa su yi yana da matuƙar tasiri a gare su.

Da a ce Phantami ya bi irin wannan salo, da tasirinsa da ƙarfinsa sun fi yadda suke yanzu.

— Sheikh Shafee'u Yusuf

Wannan ne Wurin da Manzon Allah ﷺ Ya Wuce Lokacin Hijira zuwa Birnin Madinatul Rasul.An gano wani tsohon rubutun Thamuda...
29/07/2026

Wannan ne Wurin da Manzon Allah ﷺ Ya Wuce Lokacin Hijira zuwa Birnin Madinatul Rasul.

An gano wani tsohon rubutun Thamudawa a Ain Darij (عين ضارج), da ke kusa da Al-Abwa' a kudancin Madina.

Masana tarihi suna ganin cewa wannan shi ne Ain Darij da aka ambata tun zamanin Jahiliyya, kuma yana daga cikin wuraren da Manzon Allah ﷺ ya bi ta cikinsu a lokacin hijira zuwa Madina. An kuma ambaci wannan wuri a cikin waƙoƙin mashahurin mawaƙin Jahiliyya Imru'ul Qais, abin da ke nuna tsohon tarihinsa da muhimmancinsa.

Lallai waɗannan wurare suna tuna mana da tafiyar hijirar Manzon Allah ﷺ da kuma tarihin ƙasashen Musulunci."

Allah ubangiji madaukakin sarki ya bamu albarkacin wannan wuri, ya biya mana bukatar mu. Amiin

Daga: Fityanu Islamic Centre
29 July, 2026

Wannan shi ne ɗaya daga cikin gashin Annabi Muhammad ﷺ da ake adanawa a gidan kayan tarihi na Topkapi da ke birnin Istan...
27/07/2026

Wannan shi ne ɗaya daga cikin gashin Annabi Muhammad ﷺ da ake adanawa a gidan kayan tarihi na Topkapi da ke birnin Istanbul, ƙasar Turkiyya.

Gidan kayan tarihin Topkapi yana ɗaya daga cikin wuraren da ake adana wasu kayayyakin tarihi masu matuƙar daraja da ake dangantawa da Manzon Allah ﷺ, ciki har da wasu gashin kansa, takobinsa, bakansa, da sauran kayan tarihi na Musulunci.

Musulmi a faɗin duniya suna girmama irin waɗannan kayayyaki saboda alaƙarsu da Manzon Allah ﷺ. Duk da haka, abin da ya fi muhimmanci shi ne bin koyarwarsa, yin aiki da Al-Qur'ani da Sunnarsa, da ƙaunarsa fiye da komai.

Allah Maɗaukakin Sarki Ya sanya ƙaunar Annabi ﷺ ta ƙaru a cikin zukatanmu, Ya ba mu ikon bin tafarkinsa, Ya sanya albarka a rayuwarmu, kuma Ya kawo zaman lafiya, haɗin kai da ci gaba a ƙasarmu Najeriya.

اللهم صل وسلم وبارك على سيدنا محمد وعلى آله وصحبه أجمعين.

Ya Allah, don darajar AnnabinKa Muhammad ﷺ, Ka ba Najeriya da sauran ƙasashen Musulmi zaman lafiya, tsaro, haɗin kai da albarka. Amin Ya Rabbal 'Alamin.

Daga: Fityanu Islamic Centre
July 27, 2026

Address

Pantami
Gombe
760253

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Tijjaniyya Media News posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Tijjaniyya Media News:

Shortcuts

Share