Tijjaniyya Media News

Tijjaniyya Media News Tijjaniya Media News
Spreading Light • Promoting Unity • Inspiring Spiritual Growth. Islamic | Educational | Sufi | Community Awareness.

Visit: www.tijjaniyamedia.com
Follow us for authentic updates, teachings & spiritual insights.

Masallacin Da Annabi Muhammadu SAW Ya Taba Yin Sallah A Cikinsa Dake Birnin MadinaWadin Al-Farʿ yana kudu da birnin Madi...
29/12/2025

Masallacin Da Annabi Muhammadu SAW Ya Taba Yin Sallah A Cikinsa Dake Birnin Madina

Wadin Al-Farʿ yana kudu da birnin Madina Munawwara, nisan kimanin kilomita 120 a kan babban titin da ke tsakanin Madina da Makka.

Wadin Al-Farʿ yanki ne na noma, yawon buɗe ido da kuma tarihi. A da, hanya ce ta tsofaffin ayarin kasuwanci tsakanin Madina da Makka. Ya shahara da noman kowane irin dabino, inda a da yake da fiye da rijiyoyi hamsin (50) masu gudana da ke shayar da dubban dabino. Sai dai da tafiyar lokaci, yawancin waɗannan rijiyoyi sun lalace, kuma abin da ya rage su ne rijiya uku kacal: Ayn Al-Madiq, Ayn Abi Dibaʿ, da Ayn Umm Al-ʿIyal.

Masallacin Al-Burūd (Masallacin Annabi saw)
Masallacin Al-Burūd yana a Wadin Al-Gharb, a ƙauyen Al-Madiq daga arewacin yankin. Mutanen yankin suna saninsa da sunan Masallacin Annabi saw. Yana ɗaya daga cikin masallatai uku da Annabi SAW ya yi sallah a cikinsu.

Bayanin Hukumomi da Masana Tarihi
Gwamnan Wadin Al-Farʿ, Mubarak Al-Muraqi, ya bayyana cewa Masallacin Al-Burūd sananne ne a wajen mutanen yankin da sunan Masallacin Annabi SAW, kuma yana daga cikin muhimman wuraren tarihi a yankin. Yana cikin Wadin Al-Gharb a ƙauyen Al-Madiq, ɗaya daga cikin ƙauyukan da ke ƙarƙashin gundumar. Ya ƙara da cewa yankin na ɗauke da wuraren tarihi masu shekaru da dama; wasu har yanzu suna nan ana kula da su ta hannun al’umma da kuma sa ido daga hukumomi, yayin da wasu ba a ganin komai face ragowar alamominsu.

Marubuci Abdul-Muttalib Al-Badrani ya ce: Masallacin Al-Burūd na daga cikin muhimman wuraren tarihi a Al-Madiq, Wadin Al-Farʿ. Yana a kan tsaunin Wadin Al-Gharb gaba ɗaya. Yana ɗaya daga cikin masallatan da Annabi saw ya yi sallah a cikinsu lokacin da ya ratsa Wadin Al-Farʿ. Ya ƙara da cewa wasu mutane sun canja sunansa zuwa Al-Barīd (ƙaramin Al-Burūd), amma har yanzu mutanen yankin na kiran sa Masallacin Annabi SAW, kuma har zuwa kwanan nan suna gudanar da Sallar Idi a cikinsa.

Allah SWT ya sanya alkhairi, ya bamu albarkan wannan Masallaci, Amiin Yaa ALLAH

Daga: Fityanu Islamic Centre
29, December 2025

Daga Bida Niger state Wakilin Khalifa Sheikh Ibrahim Sheikh Dahiru Bauchi Alramma Mallam Fatahu umar pandogari Ya isa Ji...
20/12/2025

Daga Bida Niger state

Wakilin Khalifa Sheikh Ibrahim Sheikh Dahiru Bauchi Alramma Mallam Fatahu umar pandogari Ya isa Jihar Niger Domin jabatar da Waliman Mahaddata Alqu’ani Mai Girma mutum hamsin da biyar 55 a makarantan Shehu dake Bida Wanda take Karkashin Jagorancin Mallam Tijjani Salihu Ahmad Markazi,

Allah yasa Antashi taro lafiya,
Maulana Sheikh Allah ya kara jaddada masa Rahma,
Khalifa Allah yayi riko da Hannun sa acikin Wannan Jagorancin,

Yaƙin Zatur-Riqaʿ yaƙi ne da Manzon Allah saw ya yi da kabilun Ghaṭafān. Al'ummar Musulmai sun sha wahala sosai saboda ƙ...
20/12/2025

Yaƙin Zatur-Riqaʿ yaƙi ne da Manzon Allah saw ya yi da kabilun Ghaṭafān. Al'ummar Musulmai sun sha wahala sosai saboda ƙarancin raƙuma da ƙasa mai duwatsu, har s**a ɗaure zannuwa a ƙafafunsu daga nan ne aka samo sunan yaƙin wato Yakin Zatur-Riqa. Ba a yi yaki ba, Amma musulmai sun samu nasara. Allah SWT ya bawa addinin Musulunci kariya. Amiiiin

Daga: Fityanu Islamic Centre

19/12/2025
Masallacin da Annabi SAW ya yi sallah a cikin sa, Masallacin yana kan hanyarsa zuwa Badar, a lokacin rasuwar Sayyaduna U...
17/12/2025

Masallacin da Annabi SAW ya yi sallah a cikin sa, Masallacin yana kan hanyarsa zuwa Badar, a lokacin rasuwar Sayyaduna Ubaida bin al-Harith RA. An binne shi ne a gabashin wannan kusa da masallacin dake gefen rijiya, a ƙasan Wadin Dhafran, wanda a yau ake kira As-Safira.

An haƙa wata rijiya a wajen masallacin, wadda a yau ake kira Rijiyar ‘Assaf. Wannan rijiya tsohuwa ce ƙwarai, kuma Ibn Ziyala ya ambace ta a tarihinsa a shekara ta 199 (H), ya kuma ruwaito hakan daga wani sahabin Manzon Allah SAW mai suna Sayyiduna Fadala RA.

Allah SWT ya bamu albarkan wannan Masallaci ya bamu ikon ziyarta Amiin Yaa ALLAH.

Daga: Fityanu Islamic Centre
Rana: December 17th, 2025

Gonar Salman Al-Farisi (RA) Wanda Annabi SAW Ya Shuka Da Hannun Sa A Garin MadinahA wannan gonar mai albarka, Annabi SAW...
15/12/2025

Gonar Salman Al-Farisi (RA) Wanda Annabi SAW Ya Shuka Da Hannun Sa A Garin Madinah

A wannan gonar mai albarka, Annabi SAW da Hannunsa mai tsarki ya shuka dabino domin Salman Al-Farisi (RA), kuma duk dabinon sun ba da ‘ya’ya a shekarar da aka shuka su.

Al-Samhoudi (RA) ya ruwaito daga Ibn ‘Abdul-Barr cewa Annabi SAW ya sayi Salman daga Yahudawa da kudi kaza da kaza, tare da sharadin a shuka dabino kaza da kaza, Salman ya yi aiki a gonar har sai dabinon sun girma. Manzon Allah SAW shi da kansa ya shuka dukkan dabinon.

Sahabin Annabi SAW Al-Samhoudi RA Na tsaya na zagaya gonar da lambun Salmanu, na kuma ji a zuciyata yadda Masoyi saw ya shuka waɗannan itatuwa a wancan lokaci, har sai na yi kamar ina ganin inda yatsun Manzon Allah ﷺ s**a ratsa suna jujjuya ƙasa suna shuka iri.

Al-Samhoudi RA yace shukar dabinon Salman (RA) babu wani daga cikin dabinon da ya lalace ko ya mutu. Daga baya Allah Ya mayar da wannan gona ga ManzonSa ﷺ, ta zama Sadakar Annabi SAW, wato Sadakar Al-Mithab (wanda ake kira Al-Faqir). Wannan wuri yana nan har zuwa yau, akwai rijiya a ciki, da wata masallaci, sai dai masallacin ya rushe. Yana bayan wata tashar mai ta bangaren gabas, kusa da Al-Kharijiyyah. An kuma gina wata babbar makaranta kusa da wurin karkashin Hukumar Ilimi. A yau wurin yana kewaye da shinge daga Hukumar Yawon Buɗe Ido da Tarihi, sai dai masallacin ya shiga cikin filin makarantar.

Ana wajen da suna Al-Faqir. A wurin akwai rijiya da kuma Masallacin Al-Faqir. An ruwaito cewa Annabi ﷺ ya taɓa yin salla a wannan Masallaci.

A wannan wuri ne Manzon Allah SAW ya tsaya domin hutawa. Wurin yana da suna Wādī Nakhla, kuma yana daga cikin manyan kwa...
14/12/2025

A wannan wuri ne Manzon Allah SAW ya tsaya domin hutawa. Wurin yana da suna Wādī Nakhla, kuma yana daga cikin manyan kwarurukan birnin Makkah.

Manzon Allah ﷺ ya zauna a wannan wuri domin hutawa ta hanyar ibada, inda yake karanta Alƙur’ani Mai Tsarki. A lokacin, aljanu (da yardar Allah) suna sauraron karatun Alƙur’ani cikin nutsuwa da ladabi.

Wādī Nakhla yana raba Makkah da Ṭā’if ta ɓangaren As-Sayl al-Kabīr. Wannan kwari yana da rassan ruwa guda biyu:

- ɗaya a kudu ana kiransa Wādī Nakhla al-Yamāniyya,
- ɗaya a arewa ana kiransa Wādī Nakhla ash-Shāmiyya.

Haka kuma, wannan kwari yana da alaƙa da Al-Hadā a Ṭā’if ta wani kwari da ake kira Al-Kafw, wanda ruwansa ke gangarowa zuwa Wādī Nakhla al-Yamāniyya.

A zamanin da, kabilu da dama sun taɓa zama a wannan kwari, amma mafi shahara daga cikinsu su ne kabilar Hudhayl, wadda har zuwa yau yankin nasu ne. Haka kuma Banu Sa‘ad daga kabilar Kināna, da kuma Al-Ḥārith sun taɓa zama a wurin.

Allah Maɗaukakin Sarki Ya ba mu albarkar Fiyayyen Halitta Annabi Muhammadu ﷺ. Amiin Yā Allāh.

Daga: Fityanu Islamic Centre
Rana: 14 ga Disamba, 2025

Wannan shine Kabarar Sayyida Asmā’ yar Abī Bakr As-Ṣiddīq, ƙanwace ga Sayyida ‘A’isha (RA) A MadīnaAsmā’ bint Abī Bakr (...
11/12/2025

Wannan shine Kabarar Sayyida Asmā’ yar Abī Bakr As-Ṣiddīq, ƙanwace ga Sayyida ‘A’isha (RA) A Madīna

Asmā’ bint Abī Bakr (27 kafin Hijira – 73 Hijira) 595 – 692 Miladiyya, Sahabiyya ce daga farkon wadanda s**a shiga Musulunci. Ita ce ‘yar Abū Bakr As-Ṣiddīq (RA), kuma matar Az-Zubair bin al-‘Awwām (RA), kuma ‘yar’uwar Sayyida ‘A’isha (RA), matar Annabi (SAW).

Asmā’ ta fi ‘A’isha girma da shekaru fiye da goma, kuma ita ce mahaifiyar Abdullāh bin Az-Zubair, wanda aka yi masa bay’a da halifanci, kuma shi ne ɗan farko da Muhajirun s**a haifa a Madīna.

An yi mata lakabi da Dhatun-Niṭāqayn (“wadda ta yi ninkakken igiya biyu”) saboda ta yanka igiyarta ta ɗaure kayan abincin Manzon Allah (SAW) da na Abū Bakr (RA) lokacin da s**a fita yin hijira zuwa Yathrib wadda daga baya ta zama Madīnatul-Munawwara.

Allah ya bamu albarkan Annabi SAW, ya bamu albarkan su bamu ikon ziyartan wannan wuri. Amiin Yaa ALLAH

Daga: Fityanu Islamic Centre
Rana: December 11, 2025

Za'a Gudanar da Gagarumin Taron Horas da ’Yan Agaji na Kasa Karo na 2 – a Jihar GombeDaga Fityanu Initiative MediaKungiy...
10/12/2025

Za'a Gudanar da Gagarumin Taron Horas da ’Yan Agaji na Kasa Karo na 2 – a Jihar Gombe

Daga Fityanu Initiative Media

Kungiyar Fityanul Islam Initiative ta Kasa za ta gudanar da Taron Horas da ’Yan Agaji na Kasa karo na biyu (2) a Jihar Gombe, daga 19 zuwa 27 ga Disamba, 2025.

Wannan gagarumin taro na horaswa an shirya shi ne domin:

- Inganta tarbiyya, zamantakewa da ilimin addinin islama a tsakanin al’umma.

- Karfafa sana’o’in hannu, bunkasa tattalin arziki, da ganin matasa sun samu dabarun dogaro da kai.

- Koyar da hanyoyin inganta tsaro da zaman lafiya a cikin al’umma.

Ana sa ran halartar mutane 3,000 – maza da mata – daga sassan Najeriya daban-daban.

Akwai gudanar da muhadarori da darussa daga manyan malamai a kowace rana, tsakanin sallar Magrib zuwa Isha’i.

Taron zai gudana ne a Makarantar kimiyya ta Gwamnatin Jihar Gombe (Science I), Gombe, daga 19 zuwa 26 ga Disamba, 2025.

Muna roƙon Allah Madaukakin Sarki ya yi wa taron albarka, ya ba da nasara, ya kuma sanya a gudanar da shi cikin kwanciyar hankali da zaman lafiya. Amin, summa Amin.

Ɗarikan Tijjaniya da Qadiriya a Jihar Kaduna sun yi Allah wadai da abin da s**a kira ban-garanci daga Gwamnatin Jihar Ka...
10/12/2025

Ɗarikan Tijjaniya da Qadiriya a Jihar Kaduna sun yi Allah wadai da abin da s**a kira ban-garanci daga Gwamnatin Jihar Kaduna.

Inji Imam Dr. Hamza Assudaniy (Sakataren Malamai ta Tijjaniyya).

Yan Darikun Sufaye na Tijjaniya da Qadiriya a Jihar Kaduna sun bayyana takaicinsu kan yadda ake mu’amala da su, tare da mayar da su saniyar ware a Ofishin Gwamnatin Jihar Kaduna da kuma Ofishin Sifikan Najeriya mai wakiltar Karamar Hukumar Zariya.

Sun bayyana cewa ba a gudanar da harkokin addinin Musulunci tare da su yadda ya kamata, kuma babu wani abu na gani-na-fadi da ake baiwa mabiya Tijjaniyya ko Kadiriyya.

An ce an bai wa wasu 'yan uwanmu mabiya Izala muƙamai na gani-na-fadi, amma Tijjaniya da Qadiriya ba su san matsayinsu ba a cikin Gwamnatin Jihar Kaduna da Ofishin Sifikan Najeriya.

Don haka suke aika saƙo cewa:
“Kifi na kallon ka mai jar ƙoma, akwai ranar kin dillanci.”

Allah Ya sa mu ji kuken al’ummar da suke wakilta. Amiin Yaa Allah.

Sheikh Malam Mijinyawa cikakken sunan sa Sheikh Abubukar Muhammad Abdullahi Tijjani.Sheikh Mijinyawa cikakken dan jihar ...
09/12/2025

Sheikh Malam Mijinyawa cikakken sunan sa Sheikh Abubukar Muhammad Abdullahi Tijjani.

Sheikh Mijinyawa cikakken dan jihar Kano ne, an haife shi a shekara 1313 kafin zuwan turawa kasar kano da shekara takwas (8).

Babban Malamin Yayi rubuce-rubuce da dama a bangaren addinin Musulunci kamar Fiqhu, Nahwu, Tafsir, Lunga da sauran su. ya bada gudumawa sosai don yada addinin Musulunci a yammacin Africa tare da amfanar da dukkan al'umma wurin zamantakewa, mu'amala da kuma rayuwa.

Tarihin ya tabbatar da cewa lokacin da Sharif Muhammad Alami Yazoo Najeriya a shekara ta 1923, Malam Mijinyawa shine yake masa tarjama zuwa yaren Hausa tare da sakatare.

Sheikh Abubukar Mijinyawa ya rasu a ranar 4/03/2/1946 wanda yayi dai-dai da 11/03/1366 an masa makwancin sa a jihar kano.

Muna addu'an Allah ya jikan sa da rahma ya gafarta masa ya jaddada rahma a gare shi, Allah ya kara masa kusanci da Manzon Allah SAW. Amiin Yaa ALLAH

Daga: Babangida A. Maina
Founder Tijjaniyya Media News
Rana: December 09, 2025

I've just reached 30K followers! Thank you for continuing support. I could never have made it without each and every one...
09/12/2025

I've just reached 30K followers! Thank you for continuing support. I could never have made it without each and every one of you. 🙏🤗🎉

Address

Manawachi Pantami
Gombe
760253

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Tijjaniyya Media News posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Tijjaniyya Media News:

Share