Tijjaniyya Media News

Tijjaniyya Media News Tijjaniya Media News
Spreading Light • Promoting Unity • Inspiring Spiritual Growth. Islamic | Educational | Sufi | Community Awareness.

Visit: www.tijjaniyamedia.com
Follow us for authentic updates, teachings & spiritual insights.

27/05/2026

I got over 1,000 reactions on my posts last week! Thanks everyone for your support! 🎉

BARKANMU DA SALLAHA madadin Fityanu Islamic Centre, muna taya daukacin al’ummar Musulmi murnar zagayowar Eid-ul-Adha.Mun...
27/05/2026

BARKANMU DA SALLAH

A madadin Fityanu Islamic Centre, muna taya daukacin al’ummar Musulmi murnar zagayowar Eid-ul-Adha.

Muna roƙon Allah (SWT) Ya karɓi ibadunmu, addu’o’inmu, da layyoyinmu. Allah Ya sanya wannan lokaci mai albarka ya zama sanadin zaman lafiya, rahama, haɗin kai da albarka ga iyalanmu da al’ummarmu baki ɗaya.

Allah Ya ci gaba da shiryar da mu zuwa tafarki madaidaici, Ya kuma ba mu rabauta a duniya da Lahira.

BARKANMU DA SALLAH.

Babangida Alhaji Maina
Co-Founder, Fityanu Islamic Centre

Innalillahi Wa'inna Ilaihir Rajiu'un: Allah Ya yi wa Sayyadi Aliyu Muhammad Sufi Jos rasuwa bayan yayi fama da jinya.She...
25/05/2026

Innalillahi Wa'inna Ilaihir Rajiu'un: Allah Ya yi wa Sayyadi Aliyu Muhammad Sufi Jos rasuwa bayan yayi fama da jinya.

Sheikh Aliyu sufi shine shugaban Majma’u Aḥbabu Sheikh Ibrahim Niass reshen Jihar Filato, ya rasu ne a gidansa da ke Anguwan Rogo Yanzuma a birnin Jos, bayan fama da jinya.

Marigayin na daga cikin manyan malaman da s**a yi fice wajen jagoranci da wa’azi a tsakanin mabiya ɗariƙar Tijjaniyya a Jos da kewaye.

An gudanar da Jana’izarsa da ƙarfe 8:00 na safiyar yau Litinin, 25 ga watan Mayu, 2026, a gidansa da ke Anguwan Rogo Yanzuma.

Allah Ya jikansa da rahama, Ya gafarta masa, Ya sanya Aljannatul Firdausi ce makomarsa. Amin.

24/05/2026

Cikakken karatun wannan babban littafi mai suna Ash-Shama’ilul Muhammadiyya, wannan littafi mai albarka wanda yake bayani akan siffofi, halaye, dabi’u da rayuwar Ma’aikin Allah ﷺ.

Littafin Ash-Shama’ilul Muhammadiyya na daga cikin fitattun littattafan Hadisi da s**a tattaro kyawawan siffofin Annabi Muhammad ﷺ, domin ƙara soyayya da koyi da Sunnarsa mai tsarki.

Sheikh Imam Junaidu Abubakar Bauchi ne ya fassara karatun cikin sauƙi da fahimta domin amfanin al’ummar musulmi.

✨ Fa’idodin Karatun Littafin:
✔️ Ƙara sanin Manzon Allah ﷺ
✔️ Ƙarfafa soyayya ga Annabi ﷺ
✔️ Koyon kyawawan halaye da dabi’u
✔️ Fahimtar Sunnah cikin sauƙi

📲 Domin samun ƙarin bayani da sabbin karatu:

📞 WhatsApp/Telegram: 08032693330

🌍 Website:
https://fityanumedia.com/



Masana tarihi sun bayyana cewa an gina Masallacin Raya ne a wurin da aka kafa tantin Annabi ﷺ a lokacin Yaƙin Khandaq (A...
24/05/2026

Masana tarihi sun bayyana cewa an gina Masallacin Raya ne a wurin da aka kafa tantin Annabi ﷺ a lokacin Yaƙin Khandaq (Ahzab).

Wurin yana kan wani ƙaramin tsauni daga Dutsen Sala’ wanda ake kira Jabal Dhubab wannan wuri ne da Muhājirai da Ansaru s**a haɗu wajen haƙa ramin khandaq.

Muna addu'an Allah SWT ya bamu albarkan Annabi SAW, ya sanya Aljannah Fidausi ce makomar mu baki daya. Amiin Yaa ALLAH

Daga: Fityanu Islamic Centre
May 24, 2026

Tun daga zamanin Manzon Allah SAW, wasu kabilu s**a zauna a wurin Dutse mai suna Sal.Dutsen Sal’ yana da matsayi na tari...
21/05/2026

Tun daga zamanin Manzon Allah SAW, wasu kabilu s**a zauna a wurin Dutse mai suna Sal.

Dutsen Sal’ yana da matsayi na tarihi mai girma, domin abubuwa masu muhimmanci da dama sun faru a gefensa ko kusa da shi, mafi shahara daga cikinsu kuwa shine yaƙin Khandaƙi.

A zamanin Daular Usmaniyya kuwa, an gina wasu gine-gine na sojoji a saman dutsen, kuma har yanzu ana iya ganin ragowar ginin. A wannan zamani, gine-ginen birni sun kewaye dutsen ta ko’ina, har ya zama wani ɓangare na iyakar yankin tsakiyar birnin Madina.

Allah SWT ya bamu albarkan Annabi Sallallahu Alaihi Wasallam. Amiin Yaa ALLAH

Daga: Fityanu Islamic Centre
May 21, 2026

Wasu matasa ‘yan bindiga biyu sun bude wuta a ranar Litinin a cibiyar Musulunci ta San Diego da ke jihar California, ind...
20/05/2026

Wasu matasa ‘yan bindiga biyu sun bude wuta a ranar Litinin a cibiyar Musulunci ta San Diego da ke jihar California, inda s**a kashe maza uku a wajen masallacin a kasar American daya daga cikinsu jami’in tsaro ne, kafin daga baya aka samu gawarwakin wadanda ake zargin sun kashe kansu da bindiga, kamar yadda ‘yan sanda s**a bayyana.

Dukkan yara da suke halartar makarantar yini da ke cikin harabar masallacin — wanda shi ne mafi girma a gundumar San Diego — an tabbatar da suna lafiya bayan harbe-harben da s**a faru jim kadan kafin karfe 12 na rana agogon PDT (1900 GMT), a cewar shugaban ‘yan sandan San Diego, Scott Wahl.

Wahl ya ce an kira hukumar FBI domin taimakawa binciken lamarin, wanda hukumomi suke dauka a matsayin harin kiyayya ga addini (hate crime).

Jami’an tsaro masu yawa da aka tura zuwa cibiyar Musuluncin sun tarar da gawarwakin maza uku da aka harbe har lahira a wajen ginin, ciki har da wani jami’in tsaro wanda Wahl ya ce mai yiwuwa ya taimaka wajen hana karin zubar da jini.

Bayan wani dan lokaci kuma, ‘yan sanda sun gano gawarwakin wasu samari biyu masu shekaru 17 da 19 a cikin wata mota da ke tsakiyar t**i, inda aka ce sun mutu ne sakamakon harbin kansu da s**a yi, kamar yadda shugaban ‘yan sandan ya bayyana a taron manema labarai da rana.

AllAllah ubangiji madaukakin sarki ya jikan su da rahma, ya gafarta masu. Amiin Yaa ALLAH

A dai-dai wannan wuri Annabi saw ya tsaya lokacin fita Yaƙin Badar, inda ya duba rundunar sa kuma Allah Ya yi masa alƙaw...
20/05/2026

A dai-dai wannan wuri Annabi saw ya tsaya lokacin fita Yaƙin Badar, inda ya duba rundunar sa kuma Allah Ya yi masa alƙawarin nasara.

A wurin ne Annabi ﷺ ya yi sallah kuma ya yi addu’ar albarka ga mutanen Madina. An gina masallaci a wurin sannan aka mai suna “Suqya” saboda kusancinsa da rijiyar Suqya, wadda ta kasance mallakin Sahabi Sa'd ibn Abi Waqqas.

Annabi ﷺ yana amfani da ruwan rijiyar saboda daɗinsa. Masallacin yana cikin Medina kusa da tsohuwar tashar jirgin ƙasa ta Hijaz.

Allah SWT ya albarkace mu da ziyartan wannan wuri albarkan Annabi SAW. Amiin Yaa ALLAH

Wannan shine Masallacin Sayyidina Aliyu Bin Abi Ṭalib (Allah Ya yarda da shi) yana gabashin Masallacin Sayyada Fatima (A...
18/05/2026

Wannan shine Masallacin Sayyidina Aliyu Bin Abi Ṭalib (Allah Ya yarda da shi) yana gabashin Masallacin Sayyada Fatima (Allah Ya yarda da ita), a kan wani tudu mai ɗan tsawo mai siffar murabba’i mai tsayi. Tsawonsa mita 8.5 ne, faɗinsa kuma mita 6.5, kuma yana da ƙaramin mataki. An gina wannan masallaci kuma an sabunta shi ne, mafi rinjaye tare da Masallacin Fathu.

Ana ruwaya cewa Sayyidina Aliyu (Allah Ya yarda da shi) ya kashe Amru bn Wudd Al-‘Āmirī a wannan wuri, wanda ya ketare ramin yaƙi (khandaq) a lokacin Yaƙin Ahzab.

A wannan zamani, an gyara dukkan waɗannan masallatai tare da kiyaye fasalinsu na tarihi da al’ada. Haka kuma Hukumar Birnin Madina ta inganta yankin tare da dasa bishiyoyi, har ya zama kamar babban lambu mai faɗi wanda ƙananan gine-gine suke cikinsa.

Allah SWT ya bamu ikon ziyartan. Amiin

Daga: Fityanu Islamic Centre

Gidan Tarihin Masu Tsarki yana Makkah, ƙarƙashin Hukumar Kula da Harami da Masallacin Annabi SAW.An kafa shi a 1999 domi...
14/05/2026

Gidan Tarihin Masu Tsarki yana Makkah, ƙarƙashin Hukumar Kula da Harami da Masallacin Annabi SAW.

An kafa shi a 1999 domin nuna tarihin Haramai biyu da ci gaban gine-ginensu. Yana ɗauke da dakuna bakwai masu nuna samfuran Haramai, tsofaffin rubuce-rubuce, hotuna, kayan tarihi masu daraja, da kayayyakin Ka’abah da masallacin Annabi Sallallahu Alaihi Wasallam, ciki har da wasu tsofaffin ginshiƙai da kayan Zamzam.

Allah SWT ya bamu ikon ziyartan wannan wuri cikin aminci albarkan Annabi SAW. Amiin

INNA LILLAHI WA'INNA ILAIHI RAJI'UN: Daya Daga Cikin Mahaddata Kuŕ'ani Na Farko A Jihar Kogi, Gwani Pa-Ochalifu Ya Rasu....
12/05/2026

INNA LILLAHI WA'INNA ILAIHI RAJI'UN: Daya Daga Cikin Mahaddata Kuŕ'ani Na Farko A Jihar Kogi, Gwani Pa-Ochalifu Ya Rasu.

Marigayin, wanda ya kasance babban limami a yankin Okotonwa da ke ƙaramar hukumar Idah a Kogi, ya shahara wajen koyar da addini da haddar Alƙur’ani tsawon shekaru.

Allah ya jikan sa da rahma ya gafarta masa, Allah yasa Alkur'ani mai girma ya cece shi. Amiiiin Yaa ALLAH

Address

Manawachi Pantami
Gombe
760253

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Tijjaniyya Media News posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Tijjaniyya Media News:

Share