05/10/2025
RAMIN MUGUNTA!
*
MUGUWAR GASA!
*
Babi na 121: *Za mu ci gaba*
*
*Wannan littafin sadaukarwa ne ga Fatima Umar Muhammad*
*
Marubucin ✍️RUHIN JARUMTAKA ✍️
*
✍️✍️✍️ Marubucin littafi - Muhammad Umar Sangaru✍️✍️✍️
*
*
Sarki Bar Hu Wanjam yayi murmushi ya dubi Majanun ya ce.
“Mutumin da hatimin fasahar Lokaci kaso mafi rinjaye yake ɗamfare akan goshinsa shi ne, Jatraes!
“Sarki Jatraes ya mutu kimanin shekaru dubu ɗari da arba'in baya. Gaba ɗaya mutanen da s**a rayu s**a san zamanin sarki Jatraes sun ƙare daga duniya.
“Binciken kimiyya da fasaha ya gano zanen wani tsohon hatimi da aka zana a jikin wani dogon tsauni dake ƙarƙashin wata babbar teku a duniyar X.
“Masana tarihi da binciken fasahohi sun tabbatar mini da cewa, wannan zane shi ne wanda yake jikin miyurar sarki Jatraes.
“Idan kayi la'akari da haka, kaga mun gano inda zanen wannan hatimi yake. Hatimin fasahar Lokaci wanda zamuyi amfani dashi wajen saka fasahar Lokaci a cikin jikin ka.”
Maganganun Bar Hu Wanjam a wannan lokaci basa buƙatar ƙarin bayani ko tambaya saboda haka Majanun kasa kunne kawai yayi ya ci gaba da saurare.
Sarki Bar Hu Wanjam ya ci gaba da cewa, “Su kuwa waɗannan mutane guda uku da na baka labari. Salsa kenan. Na riga naji yanayin su a kusa da kai sa'adda kake cikin duniyar doron ƙasashe tara.
“Bari na nuna maka su ɗaya bayan ɗaya domin ka fuskanci zancen.”
Sarki Bar Hu Wanjam yana zuwa nan a zancensa ya nuna wannan allon gilashi da hannunsa guda.
Idanun Majanun, T'chai da Kilarà da Sairana s**a koma kan wannan allo dake gefe guda.
Allon yayi haske ya nuna k**annin wata jaruma wadda Majanun yayi mata farin sani.
A daƙiƙa ta gaba Majanun ya haɗe gira cikin mamaki.
“Sinarà Jani?!” inji Majanun. “Wannan ai ta daɗe da mutuwa. Ta mutu sa'adda naje ɗauko kwari da bakan Munàr E. Zogò!!” ya ƙarasa maganar sa yana kallon Bar Hu Wanjam.
Murmushi sarki Bar Hu Wanjam ya sake yi.
“Saurara ka ji. Idan baka manta ba, nace maka jini baya ƙarya.
“Wannan budurwa 'yar wata ƙabila ce da ake kira Zarjard k**ar yadda ta faɗa maka. To, amma abinda bata sani ba shi ne, ita ba 'yar ƙabilar Zarjard bane.
“Ita 'yar wata ƙabila ce da ake kira da suna, Sinarà.
“Mutanen wannan ƙabila suna da tsananin ilimi da sanin tarihin doron ƙasashe tara.
“Eh na yarda ta mutu amma akwai wata budurwa 'yar wannan ƙabila mai irin siffofin ta, zubinta da tsarin ruhin ta.”
Sarki Bar Hu Wanjam yana zuwa nan a zancensa ya nuna wannan allon gilashi da hannunsa guda. Take hoton Sinarà Jani ya ɓace, hoton wata kyakkyawar budurwa ya maye gurbin ta.
Inda ace Arshan da gimbiya Zonar suna wannan waje da sai sun riga kowa gano wannan budurwa.
Ba wata bace wannan budurwa sai Gimbiya Siyara Shauwat 'yar sarki Takuruku na birnin Mahajó dake doron ƙasa ta biyu.
Karo na farko da mai saurare yai arba da wannan budurwa yayi kwakwanto akan anya babu alaƙa tsakanin ta da Sinarà Jani wadda yarima Ra'alin ya kashe?
A yau, zaka iya cewa an amsa wannan tambaya.
To, amma shi Majanun bai san wannan budurwa ba. Bai taɓa kallonta ba, sai a wannan rana.
“Wace ce wannan budurwa wadda take tsananin k**a da Sinarà Jani?”
Sarki Bar Hu Wanjam ya ce, “Wannan budurwa ana kiranta da suna Siyara Shauwat.
“Ta kasance 'ya kuma gimbiya a wajen sarki Takuruku na birnin Mahajó dake doron ƙasa ta biyu.”
Sarki Bar Hu Wanjam ya ɗan yi shuru sa'adda yazo nan a zancensa.
Majanun ya ce, “Idan zata maye gurbin Sinarà Jani, meye amfanin nuna min Sinarà Jani wadda ta riga ta mutu?”
“Saboda na nuna maka kuskuren da ka aikata!” inji Bar Hu Wanjam a taƙaice. “Makamin Munàr E. Zogò dole ne ya kasance a kusa da kai, a kowanne lokaci.
“Saboda makami ne wanda ɗaya daga cikin salsanka zai na sarrafawa!”
Majanun yayi shuru yana tunani. Kuskure? Shin wanne kuskure ya aikata?
A tunaninsa wajen ɓatar Munàr E. Zogò ko kaɗan babu laifin sa.
“Bani da hannu wajen ɓatar Munàr E. Zogò, meye kuskuren da na aikata?”
Karo na farko sarki Bar Hu Wanjam ya haɗe gira, “Rashin bincike! Meyasa baka yi bincike akan wanda ya kashe Sinarà Jani ba?
“Ka riga ka san cewa, wannan kwari da baka ba zai tafi da ƙafafunsa ba. Dole wani ne yazo ya ɗauke shi kuma ya sare kan Sinarà Jani.”
Majanun yana jin haka ya fara tuno lokacin da wannan abu ya faru. A wancan lokacin sun je sun samu gawar Sinarà Jani; shi da Asnaki Jayà.
Majanun yayi tunanin mutanen ƙabilar H'ƙamru ne s**a kashe ta, hakan yasa ya tuhume su.
To, amma daga baya sun yi masa rantsuwa akan ba su bane. Majanun yasan zai yi wahala suyi masa rantsuwa akan ƙarya.
Ba zato ba tsammani! Yanayin wannan mutumi wanda Majanun yaji a kusa da su sa'adda s**a dauko Munàr E. Zogò a cikin kogon Zogoros ya faɗo ransa.
Majanun ya rintse idanu. A wancan lokaci Majanun ya so yayi bincike akan wannan mutumi amma sai Sinarà Jani ta hana shi.
Majanun ya sake tuno cewa, Kilarà ya ce masa zasuyi bincike akan wannan mutumi daga baya. Shi dai kawai ya riƙe yanayin jikin mutumin.
Majanun ya juya ya dubi Kilarà ya ce masa, “Wane ne wannan mutumi wanda kace na riƙe yanayin sa, zamuyi bincike akan sa daga baya?”
Kilarà yana jin wannan tambaya ya tako yazo gaban Majanun ya tsaya. Daga can ya dubi sarki Bar Hu Wanjam ya ce.
“Mun ɗauki babbar shaida wadda zamu gano makashin Sinarà Jani kuma ɓarawon Munàr E. Zogò da ita!”
Sarki Bar Hu Wanjam ya ɗan yi shuru yana kallon su, kafun ya dubi Kilarà ya ce, “Mece ce shaidar taku?”
Kilarà yayi taku uku gaban wannan sarki, ya tafa hannayensa sau uku. Take Majanun yaga wani akwatin haske ya bayyana akan iska.
Kilarà ya ɗan juyo da kansa ya dubi Majanun ya ce, “Ƙaraso nan!” Majanun ya ƙarasa.
Majanun yana zuwa ya baiwa Majanun umarnin ɗora hannunsa guda akan wannan akwatin haske.
Majanun ya ɗora hannunsa. Yanayin wannan mutumi wanda Majanun ya jiwo sa'adda s**a ɗauko Munàr E. Zogò ya fara fitowa daga cikin allon ruhin sa yana biyo jijiyoyin jikinsa.
A hankali ya ƙaraso cikin hannun Majanun sa'annan ya shige cikin wannan akwatin haske. Wata 'yar girgiza wannan akwati yayi, kafun ya tarwatse.
Siffar yarima Ra'alin ta bayyana a daidai wajen da akwatin ya tarwatse.
Wata babbar fasaha Kilarà yayi amfani da ita a yanzu wajen gano wannan mutumi. Fasahar ta juyar da yanayin wannan mutumi wanda Majanun ya ajiye a cikin allon ruhinsa izuwa siffofin ainihin mutumin.
Koda sarki Bar Hu Wanjam yaga wannan mutumi sai ya miƙe tsaye cikin tsananin mamaki.
“Luka?!” inji sarki Bar Hu Wanjam.
Al'amarin da ya baiwa su Majanun mamaki kenan. Wane ne kuma Luka?
Sarki Bar Hu Wanjam ya ƙaraso gaban mutum-mutumin ya ɗora hannun sa guda akansa.
Nan take mutum-mutumin ya juye daga hoto ya koma ainihin siffofin yarima Ra'alin. Kai kace ɗauko yarima Ra'alin aka yi, aka kawo shi wannan waje.
Majanun bai taɓa kallon yarima Ra'alin ba a rayuwar sa, saboda haka bai san wane ne shi ba.
“Wane ne wannan mutumi?” inji Majanun.
“Sunan sa Yarima Ra'alin ɗan uwan sarki Kam'alin na doron ƙasa ta takwas.” Bar Hu Wanjam ya amsa masa wannan tambaya a taƙaice.
“Ra'alin?” inji Majanun. “To, amma meyasa ka kira shi da suna Luka a ɗazu?”
Sarki Bar Hu Wanjam ya gyaɗa kai ya ce, “Shi Ra'alin ɗan wata ƙabila ce wacce ake kira Luka... Tana daga cikin ƙabilun da aka tsine musu tun a zamanin ɗan uwa Dahasàm.”
Nan take Bar Hu Wanjam ya kwashe labarin ƙabilar Luka k**ar yadda Tairiy ta karanta a ɗakin karatun sarki Amuru ya zayyane musu.
Al'amarin da ya baiwa su Majanun mamaki kenan saboda basu taɓa tsammanin hakan ba.
“Idan mutum yayi la'akari da abinda ya faru a shekarun baya. Tabbas makamin Munàr E. Zogò yana hannun Ra'alin. Saboda da makamin aka yi amfani wajen kashe ɗan uwansa.”
Majanun ya ce, “Saboda haka zamu ƙwato makamin a hannun sa kenan!”
Sarki Bar Hu Wanjam ya gyaɗa kai, “Eh amma sai bayan wani lokaci!”
“Na fahimta!” Majanun ya ce.
“Gimbiya Siyara Shauwat zata maye gurbin Sinarà Jani kuma ita ce, Salsa-3.”
Koda yake Majanun bai san gimbiya Siyara Shauwat ba, bai san mahaifinta ba. Amma ya san doron ƙasa ta biyu da hatsarin ta.
Hasalima doron ƙasa ta biyu da doron ƙasa ta farko ba'a kiransu doron ƙasashen ƙasa. Sai dai ace doron ƙasashen sama. Ba don komai ba sai domin ɗaukakar da mutanen dake rayuwa a cikinsu s**a samu.
Majanun ya ce, “Ta ya ya zan mayar da Siyara Shauwat salsa ɗina, ba tare da na fuskanci matsala daga wajen mahaifinta ba da al'ummar doron ƙasa ta biyu ba?”
Sarki Bar Hu Wanjam ya ce, “Saura sa'a guda kacal a fara gwabza wani azababben yaƙi.
“Wannan yaƙi zai shafi gaba ɗaya doron ƙasashe tara. Akwai yiwuwar al'ummar doron ƙasashen sama da kansu su saka hannu.
“Idan kuwa zasu saka hannu, sarki Takuruku mahaifin gimbiya Siyara Shauwat yana gaba-gaba. Saboda an ci mutuncin 'yar sa watannin baya.
“Za kuyi amfani da wannan dama wajen kutsawa birnin Mahajó. Idan dai, Siyara Shauwat tayi arba da Sabon Farin Watan dake kan goshinka. Zance ya ƙare. Dolenta zata yi maka biyayya saboda ruhinta ne zai yi hakan.”
Majanun yana jin wannan batu ya gyaɗa kai cikin fahimta. Matsala ta farko an shawo kanta.
Saura matsala ta biyu da ta uku.
Majanun ya ce, "Wane ne salsa na biyu kuwa?"
Sarki Bar Hu Wanjam yayi murmushi tamkar wanda yake jin daɗin yadda Majanun ya fahimci abinda yake nufi, ba tare da tambayoyi ba.
Sarki Bar Hu Wanjam ya sake nuna wannan allon gilashi da hannunsa guda. Nan take hoton gimbiya Siyara Shauwat dake jikin allon ya disashe.
Hoton wani ƙaramin yaro wanda ba zai wuce shekaru goma sha-shida ba ya maye gurbin sa.
Majanun ya zaro idanunsa ya ƙurawa wannan yaro idanu. Yana ta ƙoƙarin tuno inda ya san wannan yaro.
Bayan ɗan dogon lokaci yana ta tunani gami da nazari, sai fuskar wannan yaro ta faɗo masa.
Sai da Majanun ya sake bude idanunsa cikin mamaki. A waje guda ya taɓa kallon wannan yaro.
Wajen da s**a je ɗaukar makamin takobin Saif-al-Ƙamr, kogon Danishin na ƙabilar H'Ƙamru kenan.
Majanun ya ɗauke idanunsa daga kan wannan allon gilashi sannan ya dubi mahaifinsa ya ce.
"Wane ne wannan yaro?
"Ta ya ya alaƙa zata shiga tsakanina dashi, alhali ni ne wanda ya kashe masa mahaifinsa?
"Shin akwai wani abu na musamman a tattare da wannan yaro ne?"
Koda sarki Bar Hu Wanjam ya ji waɗannan tambayoyi sai yayi guntun murmushi.
Ba tare ya ce komai ba, ya sake nuna wannan allon gilashi da hannun sa guda.
Nan take hoton wannan yaro ya disashe. Wani faifan bidiyo ya fara gudana akan wannan allon gilashi.
Wannan yaro aka nuno a gaban ɗaruruwan jama'ar su yana yi musu wani jawabi.
Majanun, Kilara, Tchai da Sairana s**a nutsu suna sauraren abinda wannan yaro yake cewa.
"Ya bayyana," abinda kunnuwan su Majanun s**a fara jiyo musu kenan.
"Mutumin da ke ɗauke da miyurar abar bauta Rekaza, Luru da Zogosh ya bayyana.
"Koda zamu shekara arba'in muna yaƙi da wannan mutumi, ba zamu taɓa samun nasara akansa ba.
"Wannan shi ne dalilin da ya sa na dakatar da ku daga afka masa da yaƙi.
"Bari na taƙaice muku bayani, wannan mutumi shi ne Yarima Na Musamman.
"Magajin Duniya Ta Musamman - maɗaukakiyar duniya inda ababen bautar mu suke!"
Lokacin da wannan yaro yazo nan a zancen sa sai wani mutum daga cikin mutanensu ya dube shi ya ce.
"Ta ya ya aka yi ka gano waɗannan manyan sirruka waɗanda mahaifinka da kansa bai gano su ba, dukda cewa ya fafata yaƙi da wannan saurayi?"
Yaron yana jin wannan tambaya ya dubi mutumin cikin nutsuwa ya ce, "Mahaifina ya faɗa min cewa, a duk lokacin da takobin Saif-al-Ƙamr ta shiga hannun wanda ya dace. Miyurar Rekza, Luru da Zogosh zata bayyana a goshin sa."
Wannan mutumi yana jin wannan batu, jikinsa yayi sanyi ya samu gamsuwa a ransa bisa jin wannan amsa.
Kusan mutanen ƙabilar H'Ƙamru gaba ɗayan su sun kalli miyurar dake goshin Majanun sa'adda zai yaƙe su da takobin Saif-al-Ƙamr.
Abu na ƙarshe da su Majanun s**a gani a wannan faifan bidiyo shi ne, wannan yaron yana tabbatarwa mutanen sa cewa, zasu yiwa Majanun biyayya kuma zasu nemo shi a duk inda yake domin kuwa ya kasance Na Musamman daga wajen ababen bautar su.
Lokacin da wannan faifan bidiyo yazo wannan waje sai sarki Bar Hu Wanjam ya sake nuna wannan mudubin gilashi da hannunsa guda.
Faifan bidiyon na ɗaukewa, hankalin su Majanun ya koma kan Bar Hu Wanjam suna jiran ƙarin bayani akan abinda s**a gani a wannan faifan bidiyo.
Sarki Bar Hu Wanjam yayi ajiyar zuciya ya fara bayani.
"Sunan wannan yaro sunansa Selenos.
"Ya kasance na musamman kuma ɗan ƙabilar H'Ƙamru.
"Alaƙar dake tsakanin ka dashi ita ce, Sabon Farin Wata Wata.
"Kaine babban hadimi kuma mutum na musamman wanda Rekza, Luru da Zogosh s**a san da zamansa.
"Selenos da mutanensa ba su da abun bauta wanda ya wuce waɗannan sunaye guda uku da na amabata.
"Kaga dole zasu yiwa mutumin da yazo na musamman daga wajen ababen bautar su biyayya.
"Wannan shi ne alaƙar dake tsakanin ka da shi.
"Abu na musamman dake tattare da Selenos shi ne, shi ne kaɗai mahaluƙin da zai iya sarrafa makamin Azmir."
Lokacin da sarki Bar Hu Wanjam yazo nan a zancensa sai yayi shuru, ya baiwa Majanun damar yin tunani.
Daga cikin wannan abubuwa da s**a tattauna, Majanun ya tsinto tarin tambayoyi waɗanda yake buƙatar a amsa masa kuma idan da hali ayi masa ƙarin bayani.
Majanun ya dubi sarkin ya ce, "Mene ne Rekza, Luru da Zogosh? Ban taɓa jin waɗannan sunaye ba, sai fa yanzu da nazo wajenka.
"Ina son cikakken bayani akan waɗannan sunaye waɗanda kace na zamo hadimi kuma mutum na musamman daga wajen su.
"Abu na biyu, ina son sanin wanne makami ne Azmir wanda kace iya Selenos ne zai sarrafa shi?
"Abu na uku, ka faɗa min yadda zan mayar da Siyara Shauwat ɗaya daga cikin salsa ɗina.
"Amma baka faɗa min yadda zan mayar da Selenos ba."
Sarki Bar Hu Wanjam yana jin waɗannan tambayoyi, ya ja dogon numfashi,
"Amsar tambaya ta farko, amsa ce mai tsaho. Aƙalla zata iya ɗaukar mu tsahon sa'a uku kafun na gama amsa maka wannan tambaya.
"Bayani akan Rekza, Luru da Zogosh bayani mai tsaho.
"Idan nace zan yi maka bayaninsu hakan zai ɗauke mu dogon lokaci wanda zai iya janyo a kammala wannan yaƙi.
"Mu kuma muna so ana tsaka da fafata wannan yaƙi, kuje doron ƙasa ta biyu ku ɗauko Salsa ta uku.
"Saboda haka zan amsa maka wannan tambaya amma sai gaba. Ka tuna min idan na manta."
Majanun yana jin abinda sarkin ya gyaɗa kai cikin fahimta.
Saura sa'a guda jal a fara gwabza azababben yaƙi wanda zai shafi gaba ɗaya doron ƙasashe tara.
Su Majanun zasu yi amfani da wannan dama wajen zuwa doron ƙasa ta biyu, su ɗauko Siyara Shauwat.
Wannan ita ce kaɗai damar su, saboda indai ba wannan yaƙi ake gwabzawa ba. Shiga doron ƙasa ta biyu su ɗauko gimbiya guda, ba ƙaramin aiki bane.
"Shi kuwa makami Azmir," Bar Hu Wanjam ya ci gaba da bayani. "Wasu tagwayen takubba ne guda biyu. Guda ana ce masa Az, guda kuwa Mir. Idan ka haɗa su zasu baka Azmir.
"Az - Wata takobi ce mai bala'in kaifi, hasalima tun lokacin da aka ƙirƙiro ance babu abinda ya gagareta yankawa. Walau dutse, ƙarfe ko itace. Duk abinda aka sara da wannan takobi saiya tsarge gida biyu.
"Mir kuwa- Wata siririyar takobi ce mai bala'in tsini. Duk abinda aka cakawa wannan takobi sai ya ɓule koda kuwa menene.
"Idan Selenos ya mallaki waɗannan takubba guda biyu zai sarrafa su tamkar yadda zai sarrafa jikin sa."
Lokacin da Bar Hu Wanjam yazo nan a zancensa sai ya duba wani agogon gilashi dake hannun sa.
Yanayin fuskar sa ya sauya ya ɗago kansa ya dubi Kilara, Tchai da Sairana ya ce.
"Lokaci yana neman ƙurewa. Ku je birnin Mahajo ku ɗauko Shauwat."
Sarkin ya dubi Majanun ya ce, "Idan kuka dawo zamuci gaba da tattaunawa!"
Da wannan s**a tsayar da wannan tattaunawa ta musamman, akan yarjejeniyar idan s**a dawo tare da Siyara Shauwat 'yar sarki Takuruku zasu ci gaba da tattaunawa.
*****
THANKS 4 READING.