Ruhin Jarumtaka littafin yaki

Ruhin Jarumtaka littafin yaki Gawurtattun littatafan Hausa novel masu dogon zango daga Umar Muhammad da Zahra A. Adamu
(3)

RAMIN MUGUNTA!*  MUGUWAR GASA!*Babi na 98: *Ku kamo shi!!!**Wannan chapter WhatsApp group ne s**a dauka muku nauyin ta. ...
31/07/2025

RAMIN MUGUNTA!

*

MUGUWAR GASA!

*

Babi na 98: *Ku kamo shi!!!*

*

Wannan chapter WhatsApp group ne s**a dauka muku nauyin ta. Kuyi joining domin hada karfi da karfe ana samun chapter kullum:

👇👇👇👇

https://chat.whatsapp.com/FbMgmm5lU8vKPQixKFVcyj?mode=ac_t

*

*Wannan littafin sadaukarwa ne ga Fatima Umar Muhammad*

*

Marubucin ✍️RUHIN JARUMTAKA ✍️
*

✍️✍️✍️ Marubucin littafin - Muhammad Umar Sangaru ✍️✍️✍️

*
*

Mamaki haɗe da bugun zuciya sau uku-uku ya baibaye Aiyini. Wannan babbar alama ce da zata nunawa mutum cewa, Aiyini ta san wannan sabuwar fasaha wadda Arshan yayi amfani da ita a yanzu.

A daƙiƙa ta gaba Arshan ya juye ya dawo ainihin mutum mai tsoka da jini. Arshan ya kwarara uban ihu wanda ba zaka kwatanta shi da komai ba, sai ihun fusataccen mutum.

Arshan ya sake afkowa Aiyini s**a ci gaba da fafatawa. Fuskar Aiyini ɗauke da gagarumin mamaki wanda yafi na kowanne lokaci ta fara kare hare-haren Arshan, ba tare da ta mayar masa da martani ba.

A wannan lokaci a cikin zuciyarta tunanin guduwa take yi saboda kashe Arshan bai da wani amfani a wajen ta.

Ya zamo mata dole ta koma gida ta bayar da labarin Arshan.

Sai da wannan kalmar ta ɗan tsaya mata a rai, wai kashe Arshan?!

Shi kuwa Arshan ƙoƙarin cika umarnin da Lasirina Ajamen ta bashi yake yi. Tabbas yaji muryar Lasirina Ajamen tana yi masa gargaɗi akan yayi gaggawar mallakar wannan sarƙa kuma ya koma wajen masoyiyarsa kafun wani mummunan abu ya faru da ita.

Arshan yana cikin wannan hali, yaga Aiyini ta fara yin baya-baya. Da farko bai gane abinda take nufi ba, ya ɗauka duk a cikin shiri ne. Amma bayan ɗan lokaci sai ya gano cewa, ƙoƙarin tserewa take.

Arshan na fuskantar haka ya fara ƙoƙarin dakatar da ita.

Aiyini ta sake tashi sama ta dira akan iska. Tana daga saman ta sake turowa Arshan irin wannan baƙar guguwa.

Arshan ya juye ya koma walƙiya. Walƙiyar ta ratsa ta cikin wannan guguwa kuma ta fice, ba tare da guguwar tayi mata komai ba.

Arshan yana fitowa daga cikin walƙiyar, ya kirawo ainihin ɗalasimin takobin Sikaí.

“[Sikaí]” inji Arshan.

Nan take sararin samaniya ta fara rawa. Wata irin walƙiya ta cika sararin samaniya gaba ɗaya. Babu abinda mutum zai gani, idan ya ɗaga kansa da ya wuce wannan walƙiya.

Takobin Sikaí ta ratso cikin walƙiyar ta taho da gudu ta dira akan hannun Arshan.

A wannan lokaci sinadaran walƙiya suna ta yawo a cikin jikin Arshan tamkar jinin jikin sa.

Aiyini tana ganin wannan abu dake shirin faruwa, ta fasa guduwa ta tsaya.

Ko babu komai ita 'yar ƙabilar Jorash ce. Kuma a yadda take ikirari ita 'ya ce a wajen Babban Sarki Dur'hamu.

Arshan yana ganin wannan budurwa ta juyo ta fuskance shi sai ya cika da tsananin farin ciki.

Aiyini ta buɗe hannayenta biyu take ta dira ƙasa akan turba. A daƙiƙa ta gaba ta shafi tufafin dake jikinta da hannunta guda.

Nan take tufafin s**a juye s**a koma baƙaƙe ƙirim. Duk bayan daƙiƙa sai kaga tufafin s**a ƙara duhu, duhu abun tsoro da firgitarwa.

Fatar jikin Aiyini ta fara haske da sheƙi tamkar wata daren goma sha-biyu.

Arshan ya haɗe gira. Wai tana nufin tun farko da s**a fara fafatawa bada ainihin ƙarfinta take yaƙar sa ba?

Wani guntun murmushi Aiyini tayi wanda ba zaka fassara shi da komai ba, sai na fidda raini.

Ƙwayar idanun Aiyini ta fara komawa jajawur. Kai kace duk bayan daƙiƙa sake hurata ake.

Tsantsar kafiya, ƙarfin iko da buwayar masu mulki ya cika waɗannan idanu.

Tabbas inda ace akwai wasu mutanen daban a wannan waje da tuni sun zube a gaban wannan budurwa suna ta mubaya'a ga waɗannan maɗaukakan idanu nata.

Arshan yaga gashin kan Aiyini ya ƙara tsaho tamkar wanda ake jan sa. Gashin ya tafi ƙasa da gudu kuma ya shige cikin ƙasar dake wannan daji.

Ƙasar dajin gaba ɗaya tayi girgiza na tsahon daƙiƙa biyu kacal. Ba don Arshan ya lura ba da abu ne mawuyaci ya gane hakan.

“ASÉN X. AJAMEN!

“Mene ne abinda ya kawo ka duniyar mu?!”

Muryar Aiyini ta daki kunnuwan Arshan. Saɓanin yadda ta saba yi masa da farko.

A wannan lokaci akwai tsananin ƙarfin iko da sirrin nauyi a cikin muryar ta. Tabbas inda kunnuwan ƙaramin hatsabibi muryar ta shiga da tuni kunnuwansa sun fashe, jini ya fara zubowa.

To, amma duk wannan bai dami Arshan ba. Babban abinda ya bashi mamaki shi ne, jin ta kira shi da suna: Asén X. Ajamen.

Ba don Arshan ya taɓa wannan sarƙa ba da cikin sauƙi zai yi musun wannan suna saboda bai ma taɓa jin sunan ba, sai yau ɗin nan.

To, amma duk da haka zuciyar Arshan ta yarda cewa, shi ne Asén X. Ajamen. Duk da cewa shi kansa bai da cikakkiyar amsar wannan suna.

Arshan yayi gaggawar kawar da wannan tunani daga ransa. Muryar sa na fita ɗaiɗai kuma cike da nutsuwa da lissafi ya mayarwa Aiyini amsa.

“Ku 'ya'yan Hamu ku bani sarƙar da nazo nema!”

Aiyini ta ɗan yi shuru tana kallon wannan sarƙa dake wuyanta. Budurwar ta tuno yadda aka yi ta mallaki wannan sarƙa.

“Hmm!” tayi ajiyar zuciya cikin tsananin nutsuwa. Arshan ya nemi abinda yafi komai daraja a wajen ta.

Babu buƙatar ta bashi amsa. Kawai ɗaga ƙafarta guda tayi ta daki iska da ita.

Wani ƙatoton yanka ya bayyana a gabanta. Kai kace saran takobi-mai-tafiya aka ɗauko aka sari iska da ita. Sai da aka bari iskar ta tsage sa'annan aka aikowa shi Arshan.

Wani ƙaramin rami ya bayyana akan iska kuma ya yiwo kan Arshan da gudu. Tun kafun ya ƙaraso gaban Arshan yake ta haɗiye duk abinda yake shiga gabansa.

Abubuwan sun fara daga iska zuwa komai da komai.

A daƙiƙa ta gaba Arshan ya sari iska da takobin sa. Wani abu ya fice daga takobin k**ar tsuntsu mai fuka-fuki. Waɗannan hare-hare guda biyu suna haɗuwa da juna iska ta dare gida biyu.

A fusace Arshan ya ɗaga takobin Sikaí sama. Walƙiyar dake ta sukuwa a cikin sararin samaniya ta fara dunƙulewa a waje guda. Bayan ɗan lokaci walƙiyar ta samar da wani ƙatoton layi guda ɗaya na walƙiya. Kai kace bishiyar dabino ce saboda tsabagen kauri.

Ƙatoton layin ya taho da gudu ya haɗe da takobin Arshan, take takobin ta fara haske.

Arshan ya nuna Aiyini da wannan takobi. Nan take wannan ƙatoton layi na walƙiya yayi kan budurwar da gudu.

Tufafin dake jikin Aiyini s**a fara ƙonewa suna narkewa saboda tsananin zafin dake fitowa daga cikin wannan walƙiya.

Sai dai itama ba'a bar ta a baya ba. Tuni ta girgiza gashin kanta. Gashin kan ya tarwatse a cikin iska.

Kasancewar gashin a haɗe yake da ƙasar wannan daji yasa wani kaso na ƙasar shima ya warwartsu.

Ƙasar ta koma dunƙule-dunƙule. Cikin ƙiftawar ido fiye da dunƙule goma s**a haɗu a waje guda s**a samar da wani ƙatoton bango.

Bangon ya shiga tsakanin Aiyini da wannan walƙiya ta Arshan.

Dukkansu s**a zubawa abinda yake faruwa idanu. Cikin ƙasa da daƙiƙa goma walƙiyar ta daki wannan bango.

Kai inda ace mutum yana tsaye a wannan waje da tuni ya kurumce saboda masifaffen ƙaran da ya tashi sama. Kamar faɗowar aradu guda arba'in a lokaci guda.

Wannan daji yayi wata mahaukaciyar girgiza. Babu shiri ƙura ta tashi sama ta turnuƙe ko'ina.

Walƙiyar dake sararin samaniya ta fara tsatstsagewa tamkar zata tarwatse.

Jini ya fara zubowa daga bakin Arshan da hancinsa a karo na biyu saboda wannan mummunan gamo da s**a yi.

A ɓangaren guda itama Aiyini abinda yake faruwa da ita kenan. Tuni jini ya fara yoyo daga bakinta.

Jini na ɗiga akan ƙasa. Wani saƙo ya shigo allon ruhin Aiyini. Babu wanda yasan abinda s**a tattauna da koma wane ne.

Shi kuwa Arshan tunanin yadda zai tsinke wannan sarƙa daga wuyan Aiyini yake yi a wannan lokaci.

Bayan komai ya gama lafawa Arshan yayi arba da yadda ita kanta Aiyini ta jikkata sai ya cika da farin ciki.

Ko babu komai hakan zai taimaka masa sosai da sosai.

Wannan hari da Arshan yayi amfani da shi yanzu, hari mai matuƙar tsada. Shi kansa harin yana cinye sinadari ɗari nan take.

Saboda haka zaka iya cewa, Arshan ba zai sake maimaita irin wannan hari a yanzu ba. Saboda bai da isasshen sinadari.

“GIRGIZAR ƘASA!” inji Aiyini.

Wani haske ruwan ƙasa ya fito daga bakinta ya shige cikin gashin kanta. A hankali hasken ya rinƙa yin ƙasa har ya shige cikin wannan sahara da ta mamaye wannan daji.

Arshan yaji ƙasar tayi wani irin motsi. Kafun ya sake ankara tuni ta fara girgiza tana farfashewa tana samar da manya-manyan ramuka.

Nan take ta fara zaizayewa tana haɗiye dukkan abinda ke samanta. Arshan ya dakawa Barbossa tsawa.

Take Barbossa yayi gaggawa fitowa daga wajen da yake ɓoye kuma ya ɗauki Arshan a gadon bayansa.

Zuwa yanzu Aiyini ta daina yiwa Arshan kallon komai sai hatsabibi. Duk wannan fafatawa da s**a yi, idan ka tuna cewa a cikin doron ƙasa ta farko suke sai kayi mamaki.

Wasu baƙaƙen mutum-mutumi waɗanda aka samar daga baƙar ƙasa s**a fara fitowa daga cikin ramukan da wannan girgizar ƙasa ta haifar.

Sai dai Arshan bai da lokacin ɓatawa wajen fafatawa da mutum-mutumi a wannan karon.

Cikin jimami wata murya ta yiwa Arshan magana a cikin allon ruhin sa.

“Ka tabbata zaka aikata abinda kake tunani!” zazzaƙar murya ce k**ar ta mace.

Arshan ya gyaɗa kai, kafun ya furta.

“Sikaí turu Andev!” Arshan yayi magana cikin wani tsohon yare wanda hatta waɗanda suke jin Dahamísh zaiyi wahala su gane abinda ya faɗa.

Idanun Arshan na dama wanda yake ɗauke da hoton tauraro Sairanàm ya fara zubar da jini. Duk da cewa zogi yana ratsa Arshan amma bai damu ba.

Zanen tauraro Sairanàm ya bayyana akan karfen takobin Sikaí. Jikin Arshan ya fara juyewa yana komawa walƙiya.

Jikin sa yana gama komawa walƙiya, Arshan ya kirawo fasahar sa ta Kabancan.

Walƙiya idan ta haɗu da sauri tafi ƙarfin idanu su ga abinda zai iya faruwa.

Aiyini tana tsaye bata san abinda ke faruwa ba, taji an shaƙo ta ta baya. Arshan yasa hannun sa ya tsinke sarƙar dake ɗaure a wuyan Aiyini.

Sarƙar tana tsinkewa wani mugun jiri ya ɗebi Aiyini. Kawai ta sulalo ƙasa sumammiya.

Arshan ya damƙe wannan sarƙa da kyau, yana jiran shima abinda zai faru gare shi saboda abinda ya aikata yanzu-yanzu.

Ganin Arshan ya fara yin hazo-hazo. Kafun daga bisani Arshan ya sulale ƙasa sumamme.

Aljani Barbossa yayi gaggawar ɗauke Arshan sa'annan ya fara sharara azababben gudu ɗauke da shi.

***

~Bayan kwanaki uku da faruwar wannan al'amari.
~Babbar shalkwatar mayaƙan Jorash.

***

A wani babban sansani na sojojin ƙabilar Jorash. Wani rukuni ne na wasu dakaru guda goma tsaitsaye.

Dukkansu sun wuce matakin Otaki mai inuwa, tuni sun karɓi muƙaman ƙananan kyaftin a cikin rundunar.

Wani babban soja wanda yake matakin kwamanda yana tsaye a gaban su, fuskar sa ɗauke da ɓacin rai da fushi.

A hannun sa yana riƙe da hoton Arshan guda ɗaya. Kwamandan ya nunawa waɗannan kyaftin guda goma dake gabansa hotunan Arshan ya ce.

“Sunan sa: Arshan.

“Muna buƙatar sa a raye ko kuma a mace!”

Waɗannan kyaftin guda goma s**a zaro takubbansu s**a ɗan risina a gaban wannan kwamanda. Alamun sun karɓi wannan aiki da ya basu.

Babu jimawa aka kawo ingarmun dawakai guda goma aka baiwa waɗannan kyaftin.

Take s**a hau dawakan sa'annan s**a zabure su da azababben gudu. Cikin ƙiftawar ido s**a fice daga wannan sansani sannan s**a tunkaro doron ƙasashen ƙasa.

A wannan rana babbar shalkwatar sojoji ta mayaƙan ƙabilar Jorash dake doron ƙasa ta biyu ta bayar da umarnin a kamo mata Arshan.

Kuma babban tashin hankalin har ƙananan kyaftin guda goma aka tura masa.

Muƙamin ƙaramin kyaftin yana gaba da matakin Otaki a ƙabilar Jorash. Duk wanda ya zamo ƙaramin kyaftin tofa ya fara gawurta a lamarin jarumtaka.

***

~Ɓangaren Aiyini.
~Wani sashe a cikin doron ƙasa ta farko.

***

A daidai wannan lokaci Aiyini tana tsaye a cikin wani ƙatoton lambu a gaban wani tafkin wanka ta juya ta baiwa wani kyakkyawan saurayi baya.

Daga inda take tsaye mutum zai na jiwo sautin sheshsheƙar kukanta.

“Kamar ni...?! Kamar ni...?!!” ba tare da ta ƙarasa magana sai kuka ya ƙwace mata, muryarta ta sarƙe.

“Kada ki damu, masoyiya ta.

“Kiyi sani cewa, kin fafata yaƙi ne da Asén wanda muka shafe fiye da shekaru ɗari muna jiran bayyanar sa.

“Kuma ba don ya tsere ba, na tabbata da ya shiga hannun ki...”

Aiyini tayi wata irin ajiyar zuciya...

“Kamar ni...?!!! Kamar ni...? Ace na gagara samun nasara akan wani...?!

“Ba zan yarda da hakan ba...?!”

Kyakkyawan saurayin ya taso yazo bayan Aiyini ya tsaya.

“Ina baƙin ciki bisa rashin samun nasarar da kika yi. Amma baƙin cikin zubar da hawayen ki yafi kowanne a waje na.

“Kina matsayin khal kizo kina kuka akan wani ɗan ƙaramin jarumi?”

Aiyini tana jin batun wannan saurayi hankalinta ya ɗan kwanta. Ta goge hawayen dake zubowa daga idanunta. Ta juyo ta dube shi.

“Yaushe za'a sake ƙaddamar da kamfen?!” inji Aiyini.

Saurayin yayi guntun murmushi. “An kusa...”

“Yaushe?” Aiyini ta yamutse fuska.

“Ɗaya daga cikin ababe guda uku da zasu janyo a ƙaddamar da kamfen ya faru. Saura abubuwa guda biyu. Abubuwa guda biyun ma suna daf da faruwa!”

“Mene ne waɗannan abubuwa guda uku, Elanuyil?”

Sunan wannan saurayi Elanuyil. Koma wane ne shi zuwa yanzu ba'a bayyana ba. Amma ga dukkan alamu yana da tsananin kusanci a wajen Aiyini tunda shi ne mai kwantar mata da hankali.

“Abu na farko wanda MAJALISAR MANYA ta bayyana shi ne, mutuwar Ambahà!

“Babu wanda yasan abubuwa guda biyun, sai Babban Sarki da Waziri da kuma Yarima!”

Elanuyil ya kamo kafaɗun Aiyini ya fuskance ta ya fara bata labari mai daɗin gaske.

“Tuni na shigar da ƙorafi a babbar kotun doron ƙasa ta biyu. Zuwa yanzu an ɗauki tsatstsauran matakin da ya dace akan Asén.

“Babbar shalkwata dake doron ƙasa ta biyu ta tura mayaƙa muƙamin ƙananan kyaftin har guda goma su kamo shi kuma su gurfanar dashi.”

Aiyini tana jin wannan labari ta cika da tsananin farin ciki. Aiyini ƙaramar yarinya ce ko matakin Otaki mai inuwa bata wuce ba. Ballantana ta shiga matakin ƙaramar kyaftin.

Abu na ƙarshe da ya faru shi ne, fara sumbatar juna tsakanin Aiyini da wannan saurayi mai suna Elanuyil!

Wannan kenan.

****

THANKS FOR READING 🤗✍️

RAMIN MUGUNTA!*  MUGUWAR GASA!*Babi na 97: *Fasahar Turbaya**Wannan chapter WhatsApp group ne s**a dauka muku nauyin ta....
30/07/2025

RAMIN MUGUNTA!

*

MUGUWAR GASA!

*

Babi na 97: *Fasahar Turbaya*

*
Wannan chapter WhatsApp group ne s**a dauka muku nauyin ta. Kuyi joining domin hada karfi da karfe ana samun chapter kullum:

👇👇👇👇

https://chat.whatsapp.com/FbMgmm5lU8vKPQixKFVcyj?mode=ac_t

*Wannan littafin sadaukarwa ne ga Fatima Umar Muhammad*

*

Marubucin ✍️RUHIN JARUMTAKA ✍️
*

✍️✍️✍️ Marubucin littafin - Muhammad Umar Sangaru ✍️✍️✍️

*
*

Zaka iya cewa, wannan shi ne karo na farko da Arshan ya taɓa yin arba da irin wannan inuwa. Duk da cewa bai san abinda wannan inuwa take nufi ba amma dai yana ji a jikin sa. Lallai akwai wani sharri a tattare da ita.

Arshan ya rintse idanunsa yayi duba izuwa cikin allon ruhin sa. Hankalin Arshan gaba ɗaya yafi karkata izuwa shingen Furfelo wajen da aljani Barbossa yake tara masa sinadari a asusun sa.

Zaka iya cewa, Arshan ya ga amfanin wannan sinadari sa'adda yake fafatawa da Kotegà ne. Kuma wannan zai iya kasancewa babban dalilin da ya ja hankalin sa zuwa wajen.

Akwai sinadari ɗai-ɗai har sittin da uku a cikin wannan asusu. Lamarin da yasa Arshan yayi farin ciki kenan saboda a ganinsa wannan sinadari ya ishe shi ya turnuza hancin wannan maras kunya mai suna Aiyini.

Arshan ya fara buɗe idanunsa. Hankalinsa yana barin kallon allon ruhin a hankali.

Abu na ƙarshe da Arshan yai tsinkaye dashi shi ne, allon takobin Sikaí.

Idan dai har ba za'a manta ba. Takobin Sikaí tana da allo nata na musamman wanda yake ɗauke da bayananta.

***
~O'ta: Sikai.
~Sinadari: 100.
~Matakin (sarrafawa): Sara da s**a, Siwod-dans, Saran takobi-mai-tafiya da Siwod-siwin.
~Asusu: Sinadari 63.
~Saƙo na musamman: ‘Cikakken shiri’
***

Ya k**ata mai saurare ya gano abu guda. Akwai alaƙa tsakanin aljani Barbossa da sinadarin da wannan takobi take amfani dashi.

Barbossa baya taɓa tara sinadari a cikin wannan asusu har sai sinadarin da takobin take buƙata ya cika ɗari daidai.

***

Wani murmushi ne ya cika fuskar Arshan bayan ya karanta waɗannan bayanai.

Duk da cewa wadda take tsaye a gabansa, babbar jaruma ce kuma hatsabibiya shima fa ba'a bar shi a baya wajen yin shiri ba.

Aiyini ta ɗaga wannan takobi dake hannunta ta sari iska da takobin. Mafi yawancin lokuta idan aka kai sara daga nesa, faifai ne yake fitowa a samfurin saran takobi-mai-tafiya ya ƙaddamar da mutum.

Da dama zasu yi tsammanin abinda zai faru a wannan lokaci ma kenan. Sai dai a daƙiƙa ta gaba, wata ƙawanyar turbaya ta bayyana akan iska kuma ta tunkaro Arshan cikin azababben gudu.

Cikin rabin daƙiƙa ta juye daga ƙaramar ƙawanya ta koma ƙatoton bango na ƙasa akan iska.

Cikin sauƙi wannan bango zai yi kaca-kaca da naman Arshan idan ya dira akansa.

Arshan ya ɗaga Sikaí ya sari iska da takobin shima.

Wani tartsatsin walƙiya ya fice daga tsinin takobin a guje.

Abinka da gudun abu irin walƙiya, cikin ƙiftawar ido yayi karo da wannan bango wanda yake saukowa ƙasa.

Hare-haren guda biyu s**a tarwatse a sama. Ruɓurɓushin tokar su ya zubo ƙasa.

Idanun Aiyini s**a sake cika da mamaki.

Gaba ɗaya hare-haren da ta aikawa Arshan a ɗazu, ba da takobi tai amfani ba.

Idan ka tuno yadda ta samar da wannan takobi dole zaka yi mamaki.

Ganin takobin Arshan tana iya kare hare-haren ta cikin sauƙi yafi jan hankalin budurwar fiye da komai.

Duk wannan tunani zata yi shi ne, idan tana da lokaci domin kuwa tuni a wannan lokaci wani dunƙulen walƙiya mai kaurin gaske ya tunkaro ta da gudu.

Komai kallon ƙurillan mutum bai isa ya wassafa siffar wannan walƙiya ba. A cikin daƙiƙa guda tana gudu na gaban kwatance kuma hatta iskar dake tsayawa a gaban wannan walƙiya itama konewa take tana darewa.

Cikin ƙanƙanin lokaci tazarar dake tsakanin walƙiyar da Aiyini ta zamo 'yar kaɗan.

A gaggauce Aiyini ta tura bangwayen ƙasa har guda uku su tare wannan walƙiya.

Walƙiyar ta ruguza bango na farko ta fice ta bayansa, ta ruguza na biyu shima ta fice ta bayansa, ana na ukun ne s**a tarwatse tare.

Aiyini tayi ajiyar zuciya karo na farko tun bayan bayyanar Arshan. Ga dukkan alamu ta raina Arshan da yawa wanda hakan kuma zai iya zamowa babban kuskuren da zata yi.

Daga bisani tayi wani irin juyi a sama tamkar wadda zata yi amfani da Rawar Takobi samfurin Rantsuwa, ta sauƙar da wani bahagon sara da takobin ta.

Wata iska mai ƙarfi ta fito daga cikin takobinta. Iskar tana dira akan ƙasa ta samar da wata irin baƙar guguwa wadda Arshan bai taɓa ganin k**ar ta ba.

Saboda tsabagen duhun wannan guguwa baka ganin komai dake cikinta. Ƙasa ta fara murza kanta tana shigewa cikin wannan guguwa.

Guguwar ta yiwo kan Arshan da gudu.

Kafun Arshan ya gama fuskantar wannan guguwa kuma harma yayi tunanin matakin da ya k**ata ya ɗauka a kanta.

Tuni wannan inuwa dake saman kan Aiyini ta bar kanta kuma tazo daidai saman Arshan ta tsaya.

Inuwar ta baje ta samar da wani ƙaramin hadari. Maimakon walƙiya da tsawa a cikin wannan hadari yashi ne mai kaurin gaske.

Kafun Arshan ya ankara tuni wannan hadari ya fara kwararo masa da yashi. An kwaɓa yashin da wata ƙasa mai danƙo.

Duk wannan abu ya ɗauki tsawon lokaci wajen bayani amma a zahiri a cikin daƙiƙa goma sha-biyar kacal komai ya faru.

Saboda haka Arshan yana shirin afkawa wannan guguwa, ba zato yaji wata irin ƙasa mai danƙo ta zubo kansa.

Take ta riƙe Arshan a waje guda ta hana shi motsa koda hannun sa wanda yake riƙe da takobin Sikaí.

A daƙiƙa ta gaba wannan guguwa ta taho cikin azababben gudu ta lulluɓe Arshan.

Wani guntun murmushi yazo kan fuskar Aiyini ya tsaya. Kamar irin murmushin nan da babba zai yi idan yaga yaro yana yin wani abu wanda ba'a yi tsammani ba.

Wannan guguwa ta ci gaba da tafiya da gudu a cikin wannan daji. Aiyini ta fara bin guguwar a hankali a hankali. Tana jira taga sak**akon da zai fito daga cikin wannan guguwa wadda take ta wujijjiga Arshan.

Al'amarin Arshan kuwa, ya tsinci kansa a cikin baƙar guguwa mai kaurin gaske. Saboda kaurin wannan guguwa baya iya ganin koda tafin hannun sa.

Abun zai iya zuwa da sauƙi, idan aka ce iya tafin hannun sa ne baya iya kallo. Amma a lokaci guda wannan guguwa take ta jan sa da gudu. Iskar dake cikin guguwar tana ta shiga cikin jikinsa ta dukkan kofofin jikinsa.

Wannan zai iya zuwa da sauƙi, idan kayi arba da abinda ya sake faruwa a daƙiƙa ta gaba.

Waɗansu hannaye samammu daga turbaya s**a fara fitowa daga cikin wannan guguwa suna kaiwa Arshan cafka.

Duk da cewa Arshan baya cikin hayyacinsa sosai kuma baya kallon abunda ke faruwa sosai amma a hakan ya rinƙa kakkaucewa waɗannan hannaye.

Tsahon daƙiƙa goma ana ta kaiwa da komowa tsakanin Arshan da waɗannan hannaye.

A lokacin sai wannan guguwa ta fara matsewa a waje guda. Lamarin da yasa waɗannan hannaye s**a ci gaba da kusantar Arshan kenan.

Kafun Arshan ya ankare tuni wani hannu ya taho ta baya ya damƙi kwalar sa.

Wani irin ƙarfi Arshan yaji ya ɗaga shi zai fyaɗe shi da ƙasa. Cikin ƙwarewa Arshan ya juya hannunsa wanda yake riƙe da takobin Sikaí ya sari wannan hannu da ita.

Ita kanta wannan guguwa sai da tayi girgiza kuma ta tsaya na tsahon daƙiƙa biyu kacal.

Hannun da yake riƙe da Arshan ya narke ya bi iska, Arshan ya faɗo ƙasa a cikin wannan guguwa.

A daidai lokacin hannaye fiye da hamsin s**a bayyana a jikin wannan guguwa.

Guguwar ta ƙara duhu, wani irin yashi ya fara feshi daga cikin ta yana shigewa cikin iskar da ake shaƙa.

Lamarin da yasa numfashin Arshan ya fara sarƙewa kenan. Koda Arshan ya ga mutuwa muraran sai ya ruga da gudu zai fasa wannan guguwa.

Babbar matsalar da ya fuskanta ita ce, wajen da yake so ya fasa ɗin a cike yake da tarin hannaye.

Hannayen s**a buɗe zasu damƙe shi, Arshan yai turjiya ta bazato. A wannan lokaci tuni ya fara tari.

Kafun ya ankare tuni hannaye fiye da goma sun cafe shi kuma sun ɗaga shi sama sun fyaɗa shi da ƙasa.

Arshan yana faɗowa ya sume. Wannan guguwa ta ci gaba da jan sa har zuwa ƙarshen wannan daji.

Guguwar ta gwara kan Arshan da wani ƙaramin dutse. Take kansa ya tsage jini ya fara zubowa.

A daidai wannan lokaci ne guguwar ta baje a cikin iska. Komai ya fara lafawa.

Arshan ya bayyana kwance a karshen wannan daji. Kansa yana ta zubar da jini.

Aiyini ta bayyana a can nesa guda. A hankali budurwar ta tunkaro Arshan.

“Ka ɗauki sarƙan nan, ka koma wajen masoyiyar ka cikin gaggawa. Kafun mummunan abu ya faru da ita!” muryar Lasirina Ajamen ta shiga kunnuwan Arshan.

A daƙiƙa ta gaba Arshan yaji wani irin masifa da bala'i yana tunkaro shi. Kai kace gaba ɗaya masifa da bala'in dake duniya aka tattaro kuma aka turo masa.

Firgigit! Arshan ya farka daga wannan hali da yake.

Abu na farko da ya fara yiwa Arshan sallama bayan ya buɗe idanunsa shi ne, wannan sarƙa dake wuyan Aiyini.

Tuni sarƙar ta fara fitar da wani irin haske wanda ya wuce na ka'ida. Ita kanta Aiyini sai da ta tsaya ta ƙurawa sarƙar idanu.

Kan Arshan nayi masa nauyi saboda buguwar da yayi amma a hakan ya miƙe tsaye.

Ganin Arshan ya miƙe tsaye ya sake jan hankalin Aiyini.

Zuwa yanzu idan kayi la'akari da fafatawar da ta gudana tsakanin Aiyini da Arshan zaka fuskanci cewa, wannan budurwa turbaya take sarrafawa.

Tun daga kan farkon hare-haren ta har zuwa ƙarshe, turbaya ne.

Bayan Aiyini ta ɗan tsaya tayi mamaki wanda bai wuce na daƙiƙa sittin ba, sai ta ci gaba da tunkaro Arshan.

Ga dukkan alamu a wannan lokaci zaka iya cewa, ta yanke shawarar fafatawa da Arshan gaba da gaba maimakon kai masa hare-hare daga nesa.

Arshan ya gyara tsayuwa dukda cewa har ya ɗan fara jin jiri sak**akon jinin da ya zuba daga jikin sa.

Wani murmushin mugunta ya bayyana akan fuskar Aiyini.

Murmushin bai ɓace ba Arshan ya aika mata wani irin sara. Faifan walƙiya ne wanda saboda tsabagen kaurinsa har wasu jajayen layuka ne suke kewaye shi.

Aiyini bata kauce ba kuma bata yi ƙoƙarin kare kanta ba. Haka wannan hari yazo ya dira a jikinta.

Wata baƙar wuta ta k**a jikin Aiyini tana ta babbake ta. Duk da cewa tana konewa amma bata fasa kusantar Arshan ba.

Cikin daƙiƙa goma wutar ta kashe kanta. Aiyini ta bayyana lafiyarta ƙalau. Ko ɗigon toka babu a jikinta b***e ayi tunanin ta ƙone.

“Ehye!” Arshan ya buɗe baki. Aiyini ita ce halitta ta farko da takobin Sikaí ta gagara yi mata lahanin komai.

Sai da Aiyini ta matso gaban sa ne ya ƙarewa takobin dake hannunta kallo.

An samar da takobin daga turbaya saɓanin baƙin ƙarfe. A jikin takobin akwai zanen doron ƙasashe tara. Tun daga kan doron ƙasa ta farko har zuwa doron ƙasa ta tara.

Ita kuwa Aiyini lulluɓe take a cikin ƙaramar alkyabba irin ta mayaƙan ƙabilar Jorash.

Aiyini tana ƙarasowa gaban Arshan ta kawo masa wawan sara a wuya, Arshan yasa takobin Sikaí ya kare wannan sara.

Kash! Rashin sani yafi dare duhu!!

Lokacin da takobin Aiyini ta sauƙa akan takobin Arshan sai yaji wani irin azababben nauyi ya danne shi.

Bisa dole Arshan ya durƙusa akan gwiwar sa guda. A daƙiƙa ta gaba nauyin ya ninka kansa ya koma tamkar nauyin tsauni guda.

Take Arshan ya fara karkarwa yana ƙoƙarin bindiga izuwa filla-filla. A daƙiƙa ta gaba nauyin ya sake ninka kansa tamkar nauyin tsauni guda goma.

Ƙasar da Arshan yake kanta ta rufta ciki tare dashi. Wannan ita ce sa'ar da Arshan ya taka, ba don haka ba da tuni an niƙe shi.

Aiyini tayi wani irin juyi da takobinta, take ƙasa ta harbo Arshan daga cikin ta.

Arshan yana dira bisa turba Aiyini taga tuni ya jikkata. Bakinsa da hancinsa duk sun fashe jini yana ta zubowa.

Budurwar ta fashe da dariya ta sake ɗaga takobinta ta ruga kan Arshan.

A wannan lokaci kafun ta ƙaraso Arshan ya daka tsalle sama a saman ya juya jikinsa ya baiwa hannunsa wanda yake riƙe da takobi dama.

Arshan ya saukarwa Aiyini wawan sara a kafaɗa. Saura ƙiris takobin ta haɗu da kafadar Aiyini ta k**a da wuta.

Ƙarr! Ƙarar haɗuwar takobin Arshan da takobin Aiyini ya tashi sama.

Cikin wata irin ƙwarewa Aiyini tayi wani irin juyi tasa gwiwar ƙafarta ta daki ƙirjin Arshan.

Arshan ya faɗo acan nesa. Jini ya ci gaba da zubowa daga bakinsa da hancinsa. Saboda tsabagen wahalar da Arshan ji yake k**ar ya kira fasahar Kabancan ya tsere.

To, amma ba lallai ya sake samun dama irin wannan ba. Ga dai abinda ya fito nema nan a gabansa.

Ya zamo dole a gare shi ya zage damtse kuma ya kwaci wannan sarƙa.

Arshan yana cikin wannan tunani yaga Aiyini ta tashi sama k**ar tsuntsuwa kuma ta kawo masa wawan s**a da tsinin takobin ta.

Arshan bai ankara ba saida ya rage saura kaɗan takobin ta fasa cikinsa.

Arshan ya turo sinadarin walƙiya cikin tafukan hannayensa, ya samar da wata ƙaramar garkuwa ta kariya. Kamar irin fasahar Najasin ta garkuwar dutse.

Tsinin takobin Aiyini yana haɗuwa da wannan garkuwa, garkuwar ta fara tsatstsagewa tamkar gilashi.

Wani mahaukacin nauyi wanda yafi na farko ya fara danna Arshan ƙasa. Kafun kace me wannan daidai inda yake kwance ya fara nutsewa yana ƙoƙarin ruftawa.

Arshan ya tattaro ƙarfinsa gaba ɗaya ya mirgina gefe guda. Sai da Arshan ya kwarara uban ihu saboda tsananin zogin da yaji. Saboda ji yayi tamkar tsauni guda ya ture daga kansa.

Arshan yana samun nasarar mirginawa gefe guda ya tofar yawun jini daga bakinsa.

Cikin baƙin zafin nama wanda zaka iya kwatanta shi da walƙiya, Arshan ya daka tsalle ya kaiwa sarƙar dake wuyan Aiyini cafka.

Cikin daƙiƙa biyu kacal hannunsa ya samu nasarar taɓa kan ainihin tsakiyar wannan sarƙa wanda yake kan ƙirjin Aiyini.

To, amma kasancewar ta motsa kuma bai riƙe sarƙar da kyau ba yasa hannun Arshan ya zame daga jikinta.

Sai dai ɗan taɓa sarƙar da Arshan yayi. Shi kaɗai ma ya ishe shi alkhairi.

Wani tsohon al'amari wanda ya faru kimanin shekaru ɗari biyu da hamsin baya, ya faɗo kan Arshan.

Take Arshan ya manta da dukkan raɗaɗi da zogin da yake ji. Hasalima ya gagara gaskata abinda ya tuno.

Daga can Arshan yayi ajiyar zuciya ya tuno cewa, a filin daga yake. Ƙa'idar filin daga kuwa, ba'a wasa ko tunani ko kuma tuno tsohon al'amari.

Abu guda ake yi a filin daga shi ne, gwabza yaki mai ƙarfi ya kwaci kansa.

Zaka iya cewa, taɓa wannan sarƙa da Arshan yayi ya tuno masa da wani tsohon ilimi wanda ya shafe shekaru yana ta koya domin dai, ya amfanar dashi anan gaba.

Aiyini taga Arshan ya ƙame k**ar gunki. Lamarin da yasa zuciyar ta ta cika da tsananin farin ciki kenan.

Cikin mugun nufi ta daka wawan tsalle sama ta kawowa Arshan sara a kafaɗa da nufin ta tsarge shi gida biyu.

To, a ɓangaren Arshan kuwa, gaba ɗaya walƙiyar dake cikin takobin Sikaí ya zuƙo.

***

Ƙarin Bayani:

Sinadarin walƙiya wanda Barbossa yake tarawa Arshan a cikin asusun sa. Yana cikin shingen Furfelo ne.

Sinadarin takobin wanda take amfani dashi kai-tsaye yana cikin idanun Arshan na dama wanda ya riga ya juye kuma ya koma tauraro Sairanàm.

Saboda haka idan sinadarin dake cikin idanunsa ya ƙare, dole ne ya zuƙo wanda yake cikin shingen Furfelo ya turo shi cikin idanun domin baiwa takobin damar amfani dashi kai-tsaye.

Shi kansa Arshan bai gano hakan ba, sai a yanzu da ya samu nasarar taɓa wannan sarƙa.

***

Arshan ya haɗa harda sinadarin dake cikin shingen Furfelo ya fara kewaye jikinsa dasu.

Duk ɓangaren jikinsa da yaga dama sai kawai kaga sinadarin yaje wajen.

Kafun takobin Aiyini ta dira akan kafadar Arshan, tuni ya tura sinadarin zuwa goshinsa.

Sinadarin ya shiga har cikin miyurar sa ya zuƙo tauraro guda daga cikin taurarin dake kewaye miyurar.

Bayan rabin daƙiƙa sinadaran dake jikin tauraron s**a tarwatse ko'ina a cikin jikin Arshan.

Nan take wani babban abun al'ajabi ya fara faruwa. Jikin Arshan ya fara juyewa daga tsoka da jini yana komawa walƙiya.

Cikin ƙiftawar ido Arshan ya juye daga mutum mai tsoka da jini zuwa walƙiya. Gangar jikin walƙiya.

Takobin Aiyini ta ratsa ta cikin walƙiyar ta fice fit. Ba tare da ta yiwa Arshan koda ƙwarzane ba.

“Ehye!” inji Aiyini baki a buɗe.

***

THANKS FOR READING 🤗✍️

RAMIN MUGUNTA!*  MUGUWAR GASA!*Babi na 96: *Aiyini**Wannan chapter WhatsApp group ne s**a dauka muku nauyin ta. Kuyi joi...
29/07/2025

RAMIN MUGUNTA!

*

MUGUWAR GASA!

*

Babi na 96: *Aiyini*

*

Wannan chapter WhatsApp group ne s**a dauka muku nauyin ta. Kuyi joining domin hada karfi da karfe ana samun chapter kullum:

👇👇👇👇

https://chat.whatsapp.com/FbMgmm5lU8vKPQixKFVcyj?mode=ac_t

*

*Wannan littafin sadaukarwa ne ga Fatima Umar Muhammad*

*

Marubucin ✍️RUHIN JARUMTAKA ✍️
*

✍️✍️✍️ Marubucin littafin: Muhammad Umar Sangaru ✍️✍️✍️

*
*

~Wani waje a cikin doron ƙasa ta farko.

*

Ƙatoton daji ne wanda sahara ta cika shi ta ko'ina. Iyakacin hangen mutum gabas da yamma, kudu da arewa sahara ce.

Wani wajen ya taso yayi tudu tamkar tsauni. Wani wajen kuwa yayi gangare k**ar kwari.

Lokaci bayan lokaci iska tana kaɗawa. Iskar dake ɗeban wannan sahara tana watsar da ita. Wani lokacin sai kaga gagarumar guguwa ta taso ta turnuƙe sararin samaniya ba'a ganin komai sai ita.

Wasu baƙaƙen tsuntsaye suna ta yawo a cikin wannan sahara suna neman abin taɓawa.

Gaba ɗaya wajen ya ɗauki zafi ta yadda cikin sauƙi, abu mai rai zai iya mutuwa. Ba ma tare da ya ankare ba. Wannan ne yasa waɗannan tsuntsaye suke ta yawo ko zasu tsinci gawar wani.

Ga dukkan alamu haƙan waɗannan tsuntsaye ya kusa ya cimma ruwa domin acan wani waje mai nisan gaske s**a hango wani mutum a wurge.

Cikin gaggawa s**a saki fuka-fukinsu s**a sauƙo ƙasa gaban wannan mutumi.

Duk da cewa ƙura ta ɓata siffofin mutumin amma ginannen jikinsa na jarumai yana nan. Kuma inda zaka lura da kayi arba da wani baƙin ƙyalle ɗaure a goshinsa. Baƙin ƙyallen ya zagayo ta bayan kansa.

Idan ka san Arshan wanda ya fafata da Kotegà harma yayi amfani da fasahar Kabancan batare da shiri ba. Zaka tarar cewa, shi ne a wannan waje ba wani ba.

Arshan yana kwance a sume bai ma san abinda ke faruwa ba, waɗannan baƙaƙen tsuntsaye s**a kewaye shi a tsakiya.

Kai kace waɗannan tsuntsaye sun kasance masu hankali da tunani s**a fara dudduba Arshan, suna so su tabbatar da yana da sauran rai ko kuma ya mutu.

Bayan ɗan lokaci Arshan bai motsa ba, guda daga cikin waɗannan tsuntsaye ta matso kusa da fuskarsa a hankali.

Tsuntsuwar ta sa dogon bakinta mai tsini ta caki ƙuncin Arshan. Take wajen ya fashe jini ya fara tsiyayowa.

Zaka yi tsammanin zogin da zai ratsa Arshan zai sa ya farfaɗo daga wannan suma da yayi. Amma ina hasalima ko motsawa bai ba.

Lamarin da ya baiwa wannan tsuntsuwa ƙwarin gwiwa kenan tayi azama wajen sake kaiwa Arshan wani s**an.

Sai dai a daidai lokacin ne, babu zato ba tsammani wani ƙarfin iko mai ƙarfin gaske ya kaɗa.

Babu shiri waɗannan tsuntsaye s**a buɗe fuka-fukinsu s**a tashi sama gaba ɗayan su.

Duk da cewa wannan daji yana cike da yanayin zafi amma sai da wani sabon zafi mai ƙarfin gaske ya sake lulluɓe shi.

Arshan yana kwance kawai zufa ta fara kwararowa daga jikin sa. Jikinsa ya ɗauki zafi lamarin da yasa nan take ya farfaɗo daga wannan suma da yayi.

Arshan na dawowa hayyacinsa kafun ya buɗe idanunsa. Hotunan al'amuran da s**a faru dashi a rayuwarsa s**a fara faɗowa kansa.

Abun ya fara tun daga lokacin da yake yaro ɗan shekaru huɗu sa'adda baba Andas ya tsince shi a kasuwa. Abun ya ci gaba da tafiya zuwa sa'adda Arshan yake shekaru shida har yayi arba da waɗannan taurari guda uku dake sararin samaniya.

Zuwa sa'adda ya girma ya zamo cikakken saurayi kuma yayi arba da gimbiya Dani kuma ya kamu da tsananin ƙaunar ta.

Ya tuno cewa, akan gimbiya Dani yake shan duk wannan wahalar da yake sha yanzu. Har ma an samu wata matsafiya da ta yaudare shi da gimbiya Dani kuma ta cutar dashi.

Kuma idan zai tuna yana fafatawa da ita ne, ya kira fasahar sa ta Kabancan. Babu shiri fasahar tai jifa dashi uwa-duniya. Yanzu ya tsinci kansa a wannan waje.

Arshan bai samu damar kammala wannan tunani da yake ba. Takun sahun wani mutum s**a yi masa sallama.

Babu shiri Arshan ya kawar da wannan tunani daga cikin ransa sannan ya buɗe idanun sa.

A tsakiyar wannan daji ya tsinci kansa. Iyakacin hangensa sahara ce ta lulluɓe ko'ina.

Wannan duk bai dame shi ba. Babban abinda ya dame shi shi ne, wannan dajin ina ne?

Wataƙila Arshan zai iya samun amsar wannan tambaya musamman da ya tuno cewa, ai akwai wanda yake tunkaro shi.

Arshan yai maza-maza ya juya wajen da yake jiwo takun sahun mutumin. Take yayi arba da wata kyakkyawar budurwa ta gaban kwatance wadda idan ka cire gimbiya Dani Arshan zai iya rantsewa bai taɓa ganin kyakkyawa k**ar ta ba.

Wasu abubuwa guda uku da Arshan ya gani tattare da wannan budurwa su ne s**a kore masa dukkan wannan kyawu nata. Wani kwarjini, ƙarfin mulki da isa irinta sarakunan farko s**a maye gurbin sa.

Abu na farko da Arshan ya gani tattare da wannan budurwa kuma yayi masa kwarjini shi ne, dogwayen kunnuwanta. Kunnuwan budurwar a fiƙe suke k**ar na zomo kuma sun kalli sama. Arshan ya san kaɗai mutanen dake doron ƙasa ta farko da ta biyu ne suke da irin waɗannan kunnuwa.

Abu na biyu da Arshan ya girgiza shi kuma shi ne, ƙwayar idanun wannan budurwa sun kasance jajazur. Kai kace wuta ake hurawa a cikin kanta. Duk faɗin doron ƙasashe tara babu mai irin waɗannan idanu sai mutanen ƙabila guda. Arshan ya san hakan kuma duk wanda ke rayuwa a duniya yasan hakan. Ƙabilar Jorash kaɗai take da irin waɗannan idanu.

Abu na uku da Arshan ya gani a jikin wannan yarinya ya mafi na farkon da na biyun girgiza shi. Domin kuwa sai da Arshan ya goge idanunsa da kyau domin ya tabbatar da abinda yake gani gaskiya ne ba ƙarya ba.

A daƙiƙa ta gaba Arshan ya laluɓo jakar guzurinsa ya buɗeta. Cikin gaggawa jarumin ya zaro wata takarda daga cikin aljihunsa.

Arshan ya duba wannan takarda sa'annan ya ɗago kansa ya duba wuyan wannan budurwa.

Mamakin dake kan fuskar Arshan ya ninka kansa wajen sau dubu a cikin daƙiƙa guda.

To, idan kayi duba izuwa wuyan wannan budurwa zaka ga ba komai bane a jikin wuyan sai wata kyakkyawar sarƙa.

Sarƙar ta zagayo ta bayan wuyanta. A tsakiyar ƙirjin wannan budurwa anan kan wannan sarƙa yake.

Idan kayi arba da hoton dake hannun Arshan kuma ka sake duba izuwa wuyan wannan budurwa. Zaka cika da tsananin mamaki.

Babu batun suna k**a ko kuma wani dogon bayani. Hoton wannan sarƙa dake hannun Arshan, sarƙar ita ce a wuyan wannan budurwa. Babu dogon bayani ko kuma ja-in-ja.

Wannan hoto dai, sarki Mazurus mahaifin gimbiya Dani ce ya baiwa shi Arshan lokacin da ya kuɓutar da Arshan daga kurkuku ta ɓoyayyiyar hanya.

Sarki Mazurus ya buƙaci Arshan ya shiga duniya ya nemo masa wannan sarƙa. Idan Arshan ya samo wannan sarƙa kuma ya kawo masa ita.

Sarki Mazurus ya yi alkawarin aura masa 'yarsa gimbiya Dani.

Zaka iya cewa, nemo wannan sarƙa ita ce abinda ya shigo da Arshan duniya.

Bayan doguwar fafatawa da bincike da haɗuwa da mutane iri-iri. Yau ga Arshan a gaban wannan sarƙa.

Ganin wannan sarƙa a wuyan wannan budurwa ya saɓa da abinda su sarki Ladsin s**a ce da kuma abinda binciken Arshan ya bashi.

A ganin Arshan wannan sarƙa a wuyan yarinya Silmà take. Babu kwakwanto ko jan magana akan haka. Kusan kowa ya yarda da hakan.

Saboda idan mutum zai tuna a jikin hotunan yarinya Silmà waɗanda s**a cika lunguna da saƙo na doron ƙasashe tara akwai wannan sarƙa a wuyan ta.

Ya ya aka yi wannan sarƙa tazo wuyan wannan budurwa dake gaban Arshan?

Saboda idan Arshan ya tsaya kwakwanto akan ainihin sarƙar ko ba ainihinta bane, hikimar sa da basirarsa batai masa amfani ba. Wannan sarƙa dai ita yake nema kuma gata nan a wuyan wannan budurwa.

Wai shin ma wace ce wannan budurwa?

Sai dai duk wannan lokaci da Arshan ya ɗauka yana ta tunani gami da kai-komo a cikin zuciyarsa. Ita kuwa wannan budurwa ƙarasowa tayi gabansa. Tazarar taku goma kacal.

Budurwar ta ɗan ja numfashi. “Karo na farko da na kalli ƙasƙantaccen bawa a cikin 'yanci.

“Ya ya aka yi ka gudo daga kurkuku?!”

Muryar budurwar tana da daɗin saurare dukda cewa idan kayi la'akari da lafazinta dakawa Arshan tsawa tayi.

Wataƙila Arshan bai ji abinda wannan budurwa ta ce ba. Domin kuwa kwata-kwata amsar da ya bata, bata da alaƙa da tambayar da tayi masa.

“Wace ce ke?!” Arshan ya tambaye ta shima.

“Ya ya aka yi kika mallaki wannan...” kafun kalmomin su gama fitowa daga bakin Arshan tuni dunƙulen yashi ya daki kansa.

Arshan ya hantsila can baya. Ƙura ta turnuƙe daidai inda ya faɗo.

Wannan budurwa tana huci ta tunkaro Arshan. Ga dukkan alamu Arshan ya raina ta ne a ganin ta.

Saura taku goma ta iso inda Arshan yake kwance ta tashi sama a cikin iska tamkar tsuntsuwa.

A daidai lokacin da Arshan ya miƙe zaune, a daidai lokacin yaji muryar wannan budurwa ta cika wannan daji da amsa kuwwa. Kai kace wani ƙatoton bututun magana take amfani dashi.

“Ba zan ga laifin ka ba. Saboda ka nemi ka san sunan wadda zata tura ka lahira.

“Sau tari bayi suna zama a cikin baƙin ciki da takaici, idan s**a je lahira basu san waɗanda s**a tura su can ba.

“SUNA NA AIYINI 'YAR BABBAN SARKI DUR'HAMU!!!”

Kiran sunan wannan sarki sai da yasa gaba ɗaya gashin dake jikin Arshan mimmiƙewa.

Wata irin wutar ƙiyayya ta fara ruruwa a cikin zuciyar Arshan. Idanun sa s**a kaɗa s**a yi ja. Marmarin yaƙi da burin ɗaukar fansa ya fara kaɗawa ta cikin su.

Tauraron dake cikin idanun Arshan na dama ya fara haske. Lamarin da ya janyo hankalin Aiyini kenan.

Koda taga wannan tauraro sai ta ɗan zaro idanu cikin mamaki.

“Sairanàm?!” ta ɗan kira sunan tauraron.

Zuwa yanzu ta fara tabbatarwa kanta cewa, zai yi wahala fa idan wannan saurayin dake gabanta fursuna ne.

Saboda ta san cewa, gaba ɗaya fursunonin dake kulle a kurkuku babu wanda yake da ikon mallakar fasaha.

Sairanàm babbar fasaha ce. Asali ma fasaha ce dake da alaƙa da takobi. Takobi wacce take haɗe da ruhi.

Arshan ya miƙe tsaye, kansa yana kallon sama. Idanunsa suna kafe akan Aiyini.

Aiyini ta ɗaga hannunta guda sama ta murza 'yan yatsunta. Take ƙasar dake bayanta ta fara haɗewa a waje guda.

Cikin ƙanƙanin lokaci ƙasar ta juye ta samar da wani ƙatoton ƙwallo na ƙasa.

Ƙwallon ya taso yazo gaban Aiyini ya tsaya. Kai kace wani curin nakiya aka haɗe a waje guda.

Aiyini ta nuna Arshan da yatsar ta guda. Take wannan ƙatoton dunƙule na ƙasa yayi kan Arshan da gudu.

“Sikaí!” inji Arshan.

Tauraron dake cikin idanun sa ya fitar da wani haske. Hasken ya juye ya koma zabgegiyar takobi wadda tun daga farkonta har zuwa mariƙinta, walƙiya ce take ta feshi.

Wannan dunƙulen ƙasa yana isowa gaban Arshan, Arshan yayi masa wawan sara da takobin Sikaí.

Wata gagarumar ƙara ta tashi sama. Dajin gaba ɗayan sa yayi girgiza. Ƙura ta tashi sama ta turnuƙe sararin samaniya.

Aiyini ta ɗan haɗe gira bisa ganin an samu mahaluƙi na farko da ya tare harin ta.

Budurwar ta tafa hannayenta sau uku sannan ta sake nuna Arshan da tafukan hannayenta.

Ƙasar dake kewaye da Arshan ta fara murza kanta tana darewa. Arshan ya riƙe takobin Sikaí da kyau kuma ya zuba idanu.

Jim kaɗan ƙasar ta fara juyewa tana samar da mutum-mutumi. Ɗaiɗai har guda uku sai da s**a fito daga cikinta.

Ba wannan ne karo na farko da Arshan ya fafata da mutum-mutumi ba. Amma ƙamshin iko da gaskiyar da yake ji a jikin waɗannan mutum-mutumi ta dabam ce.

Ba don a gabansa aka samar dasu ba da zai yi wahala ya yarda mutum-mutumi ne.

Waɗannan mutum-mutumi guda uku suna sanye da dogwayen riguna. Gaba ɗayansu suna riƙe da wuƙaƙe. A duk lokacin da s**a buɗe bakunansu sai kaga yashi yana feshi daga ciki.

Arshan ya gyara tsayuwa kuma ya ci gaba da zuba musu idanu. A wannan lokaci tuni sun kewaye shi.

To, a ɓangaren Aiyini kuwa, motsa 'yan yatsun hannunta take tamkar wata mai wasa.

Wajen da budurwa take tsaye ya fara tsatstsagewa. Kai kace girgizar ƙasa ce take shirin afkuwa.

Tuni waɗannan mutum-mutumi guda uku sun afkawa Arshan da azababben yaƙi.

Babu yadda Arshan ya iya dolen sa ya tare su kuma a halin yanzu suna tsaka da fafatawa.

Waɗannan mutum-mutumi suna da baƙin zafin nama fiye da duk wani abu wanda Arshan ya sani.

Kusan ta kowanne ɓangare suna iya kawowa Arshan sara ko s**a da waɗannan wuƙaƙe dake hannun su.

Kai ba don Arshan yana da baƙin zafin nama ba da babu yadda ya iya da waɗannan mutum-mutumi guda uku.

Kai kace wani iko ne na musamman yake sarrafa waɗannan mutum-mutumi. Idan ɗayan su ya kawowa Arshan s**a ta kai, ɗayan zai kai masa a ƙirji, na ƙarshen kuwa sai ya nemi tumbinsa. Sai Arshan yayi da gaske yake iya kauce musu.

A duk lokacin da takobin Sikaí ta haɗu da wuƙaƙen waɗannan mutum-mutumi. Wata ƙara ce take tashi sama tamkar an buga bango.

Arshan ya ci gaba da fafatawa da waɗannan mutum-mutumi har tsahon ɗan lokaci.

Koda s**a ga basu sami nasarar komai akan Arshan ba. Sai guda daga cikin su ya kwanta a ƙasa take jikinsa ya rududduge ya shige cikin ƙasa.

Arshan yana murnar sun fara mutuwa, ba zato ba tsammani yaji an k**a ƙafafunsa daga ƙarƙashin ƙasa.

Arshan yana dubawa yaga hannayen wannan ɗayan ne wanda ya shige cikin ƙasar a ɗazu.

Ga dukkan alamu waɗannan mutum-mutumi dabara s**a yi masa. Kafin Arshan ya ƙwace sawayen sa daga damƙar da wannan mutum-mutumi yayi masa.

Tuni ɗaya daga cikin su ya kawo masa s**a a wuya, ɗaya ya kawo masa a ciki.

Arshan ya sunkuya wuƙar wanda ya kawo masa s**a ta caki iska. Amma a daidai lokacin wani mugun zogi ya ratsa shi.

Ba shiri Arshan ya taƙarƙare zai kwarara uban ihu amma sai ya fasa sak**akon tuno duk wannan fafatawa da yake da mutum-mutumi yake yin ta.

Idan ba zai iya samun nasara akan mutum-mutumi ba, ta ya ya zai fara tunkarar Aiyini?

Cikin baƙin zafin nama da fusata Arshan ya fizge sawayensa daga hannun wannan mutum-mutumi sannan ya daka wani irin tsalle, a saman yasa ƙafafunsa ya doki ƙirjin mutum-mutumin da ya caka masa wuƙa a ciki.

Saboda ƙarfin dukan sai da mutum-mutumin ya hantsila can nesa, yana faɗowa ƙasa ya fara rushewa.

A daidai lokacin ne ɗaya daga cikin mutum-mutumin ya sake kawo masa wawan s**a a wuya.

Arshan ya cilla takobin Sikaí sama, kafun takobin ta faɗo tuni ya kamo hannun wannan mutum-mutumi wanda yake riƙe da wuƙa ya fizge shi da ƙarfin tsiya.

Hannun ya tsinke daga ainihin gangar jikin. Arshan ya miƙa hannunsa ya cafo Sikaí.

Cikin ƙwarewa Arshan yayi juyi da takobin sai ga kafadar wannan mutum-mutumi ta zaftare shima take ya rushe a wannan waje.

Sai a wannan lokaci Arshan ya lura da abinda Aiyini take ƙoƙarin aikatawa.

Wani mugun zogi ya sake ziyartar Arshan a daidai wajen da aka masa wuƙa ɗazu.

Cikin gaggawa Arshan ya laluɓo magani daga cikin jakar tsafin sa. Arshan ya barbaɗawa wannan ciwo magani.

A daidai lokacin ne wannan daji ya cika da wani irin rugugi. Kai kace ƙasa ake ƙoƙarin juyawa ta koma sama.

A gaggauce Arshan ya ɗago kansa ya kalli Aiyini.

Nan take yai arba da ƙawanya-ƙawanya na yashi suna ta taruwa a gaban ta.

Cikin ƙiftawar ido ƙawanyar ta juye ta koma wata zabgegiyar takobi. Takobi ce doguwa kuma kakkaura. Tana da launin ruwan ƙasa k**ar ƙasar dake wannan daji.

Takobin ta dira akan hannun Aiyini.

Sarƙar dake wuyanta ta fara haske wanda ya ja hankalin Arshan ƙwarai da gaske.

Wata babbar inuwa mai k**a da inuwar Otakí tazo saman kan Aiyini ta tsaya.

***

THANKS FOR READING.

Address

Sangaru Street
Gombe

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Ruhin Jarumtaka littafin yaki posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Ruhin Jarumtaka littafin yaki:

Share

Category