
05/07/2025
RAMIN MUGUNTA!
*
MUGUWAR GASA!
*
Babi na 81: *Kogon Ƙarƙashin Ƙasa*
*
*Wannan littafin sadaukarwa ne ga Fatima Umar Muhammad*
*
Marubucin ✍️RUHIN JARUMTAKA ✍️
*
✍️✍️✍️ Marubucin littafin: Muhammad Umar Sangaru ✍️✍️✍️
*
*
~Birnin sarauni Milisa.
~Daular Ubbaniya.
*
“Ka kashe ma'aboci Otakí, ka samu kyautar sinadari har guda ashirin da biyar.” saƙon da ya shiga cikin allon ruhin Arshan kenan.
A wannan lokaci ya buɗe idanunsa, bayan yayi doguwar ajiyar numfashi da mamakin abubuwan da s**a faru sai ya miƙe zaune.
Arshan yayi arba da sarauniya Milisa durƙushe akan gwiwowinta tana ta haki. A gefe guda kuwa, Zonar ce a kwance cikin mawuyacin hali. Leɓɓan bakinta gaba ɗaya sun bushe saboda tsabagen ƙishirwa.
A guje Arshan ya laluɓo battar ruwansa ya ruga ya bata a baki tasha. Bayan ta kurɓa k**ar sau huɗu sai ta buɗe idanunta.
Koda taga Arshan a raye kuma cikin koshin lafiya sai ta cika da tsananin farin ciki.
Arshan na ganin gimbiya Zonar ta farfaɗo ya ruga da gudu zuwa wajen da masoyiyarsa gimbiya Dani ke kwance.
Yana zuwa ya tarar da ita cikin mummunan hali. Numfashinta na fita da ɗai-ɗai. Ranta yana da daf da fita.
A ɗimauce Arshan ya fiddo wani maganin barci mai ƙarfin gaske ya bata tasha. Tana shan wannan magani, barci mai nauyi yayi awun gaba da ita.
Arshan ya sa hannunsa ya zare wannan wuƙa dake cake a kafaɗarta. Koda yaga zurfin raunin da wannan wuƙa tayi mata sai hankalinsa yayi mummunan tashi.
Cikin gaggawa Arshan ya sake fiddo kayan aiki ya gyara mata wannan rauni.
A wannan lokaci sarauniya Milisa ta miƙe tsaye daga wannan waje da take durƙushe. Idanunta cike sharkaf da hawaye saboda tsananin tausayin mutanen ta da ta rasa sak**akon wannan hari.
Ba tare da ɓata lokacin komai ba, Arshan ya goya Dani a gadon bayan sa. Gimbiya Zonar ta taso tazo gaban sa tana dudduba gimbiya Dani.
Kasancewar tana cikin halin barci, k**anninta basa sauyawa. Kamannin gimbiya Dani, Zonar take gani a wannan lokaci.
To, amma tana jin ƙamshin wani babban sihiri yana tashi a jikin ta. Alhali ita kuwa gimbiya Dani bata kasance matsafiya ko mai ƙarfin sihiri ba.
“Wai har yanzu kwakwanto k**e akan ba ainihin masoyiyata bace?” Arshan ya yiwa gimbiya Zonar wannan tambaya.
Cikin gaggawa Zonar ta girgiza kanta, “Ko kaɗan!”
A zahiri ta nuna masa ta gamsu gimbiya Dani ce amma a zuciyarta ta ƙudurce zatayi gagarumin bincike akan wannan matsafiya kuma zata ɗauki matakin da ya dace akanta.
A wannan lokaci sarauniya Milisa ta ƙaraso gaban su. Fuskarta cike da jimami da alhini.
Tuni a wannan lokaci dakarun ƙasarta sun zo sun fara tono gawarwakin da wannan gini da ya rushe ya kashe.
Wani ƙasaitaccen keken doki yazo gabansu ya tsaya. Milisa ta sakarwa Arshan murmushin ƙarfin hali ta ce, “Mu tafi gida!”
Ba tare da gardamar komai ba, Arshan da gimbiya Zonar s**a shiga cikin wannan keken doki sa'annan s**a ci gaba da tafiya.
Saboda ganin wannan hali da sarauniya Milisa ta shiga yasa Arshan da gimbiya Zonar s**a ja bakinsu s**a yi shuru basu sake cewa komai ba.
Bayan dogon lokaci wannan keken doki ya ƙaraso cikin gidan sarautar sarauniya Milisa.
Sarauniya Milisa tana sauƙa daga cikin wannan keken doki ta bayar da umarnin akai Arshan da gimbiya Zonar masauƙinsu kuma a kirawo babban likita wanda zaizo ya sake duba lafiyar su.
Matuƙin keken dokin ya risina cikin biyayya sa'annan ya wuce tare da su Arshan.
Kai-tsaye sarauniya Milisa ta wuce zuwa fadarta. Tana zuwa ta zauna akan karagar mulki sannan ta tura aka kirawo dukkan sarakunan dake ƙarƙashin mulkin ta.
Bayan k**ar sa'a biyu, sarakunan s**a gama hallara.
Bayan sun gama yiwa sarauniya jalje bisa wannan mummunan abu da ya faru sai sarauniya Milisa ta dube su ta ce.
“Zan shigar da ƙorafi akan wannan abu da ya faru. Zan so sarauniya Jazwirà ta tsananta bincike kuma ta ɗauki tsatstsauran mataki akan waɗanda keda alhakin wannan hari.
“Shin a cikin ku akwai wanda ya ga farkon abin ko kuma yaji labari daga waje mai ƙarfi?”
A cikin wannan tattaunawa ce, sarakunan dake ƙarƙashin mulkin sarauniya Milisa s**a bata labarin shigowar mutane guda biyu daga sama.
Guda daga cikinsu shi ne, Jeziy'Kaubar guda kuwa basu san inda yai ba.
Sarauniya Milisa sai ta yiwa wannan al'amari wawan fahimta. A ganinta Jeziy'Kaubar ya biyo masoyiyar Arshan ce tunda sun tarar dashi ya caka mata wuƙa (a ganinta).
Saboda haka sarauniya Milisa ta ɗauki alhakin wannan hari gaba ɗaya ta ɗaura shi akan Jeziy'Kaubar kuma ta rubuta wasiƙa tare sa-hannu ta aikawa haɗaɗɗiyar daular ƙarƙashin ƙasa ta sarauniya Jazwirà.
Sarauniya Milisa ta buƙaci a bi mata haƙƙin mutanenta waɗanda rayukansu s**a salwanta a cikin wannan hari.
A ɓangaren Arshan, Kotegà da gimbiya Zonar kuwa. Tuni an sauƙe su a cikin wannan ƙasaitaccen gida nasu.
Arshan ya shiga cikin wannan gida da sauri kuma ya kwantar da masoyiyarsa akan gado.
Bayan ɗan lokaci, wani babban likita ya shigo cikin wannan ɗaki. Take ya tambayi Arshan dukkan abinda ya faru. Arshan ya kwashe labarin komai ya zayyane masa.
Likitan yai amfani da iliminsa na likitanci ya duba wannan rauni dake kan kafaɗar gimbiya Dani. Take ya dubi Arshan ya ce, “Wannan rauni ba ainihin raunin makami bane.”
Gimbiya Zonar wadda ke kwance akan wani gado dake gefe guda ta ɗan zaro idanu cikin mamaki.
Shi kuwa Arshan haɗe gira yayi, shi da kansa ya zare wannan wuƙa dake cake a kafaɗar Dani.
Ta ya ya za'a ce masa ba ainihin raunin makami bane?
“Idan ba raunin makami bane, to, raunin mene ne, likita?” Arshan ya tambaya.
Likitan ya ɗago kansa ya dubi Arshan cikin nutsuwa sa'annan ya fara yi masa bayani.
“Idan ka lura raunin yayi zurfi da yawa. Inda ace na ainihin wuƙa ce da tuni ya iso ƙashin kafaɗarta...”
Duk wannan maganganu s**a shiga kunnen wannan Kotegà daki-daki. Tuni a wannan lokaci hankalinta ya fara tashi saboda wannan likita yana ƙoƙarin tona mata asiri a wajen Arshan.
Cikin gaggawa ta fara tunanin hanyar da zatai amfani da ita wajen dakatar da wannan likita daga ci gaba da magana.
Sai dai a lokacin Arshan yayi magana. “Kaga likita, ba kiran aka yi domin kayi mini bayanin mene ne ya haddasa wannan rauni ba. An kira ka ne domin ka duba raunin kuma kayi masa aikin da ya dace.
“Saboda haka kayi abinda aka umarce ka kawai. Bincike ko ainihin wannan rauni duk ba naka bane!”
Likitan yana jin wannan batu ya ɗan risina cikin biyayya. Ba tare da gardamar komai ba, ya yiwa Dani aikin da ya dace.
A zuciyar Kotegà ta cika da tsananin farin ciki bisa ganin wannan abu da ya faru.
Likitan yana gama gyara raunin Dani ya koma kan gimbiya Zonar itama ya gyara raunikan dake wuyanta.
Bayan ya kammala ya fiddo kwalaben magunguna ya baiwa Arshan sa'annan s**a yi sallama da juna ya tafi.
Itama gimbiya Zonar gado aka bata, saboda an saka waɗansu itatuwa an gyara raunin dake wuyanta.
Arshan ya ci gaba da kula da waɗannan 'yan mata guda biyu har tsahon kwanaki uku.
A wannan lokaci raunin dake kafaɗar gimbiya Dani ya warke sumul tamkar bata taɓa jin rauni a wajen ba.
Al'amarin da ya baiwa Arshan mamaki kenan, kwanaki uku sun yi kaɗan wajen warkewar raunin.
Lamarin da yasa ya zauna ya ƙurawa gimbiya Dani idanu kenan, yana ta tunani.
Babu abinda yake faɗowa kansa a wannan lokaci sai irin k**annin da ya taɓa gani a jikin gimbiya Dani sa'adda ya shiga gidan sarautar sarki Mazurus ta cikin wannan tafkin wanka. Wato lokacin da Dani ta kira shi da matsoraci kuma har ta ƙalubalance shi akan yazo gaban mahaifinta yace yana sonta.
A wancan lokaci fatar jikin gimbiya Dani fara ce tas tamkar idan aka taɓa ta jini zai zubo. Gashin kanta ya kasance baƙi wuluƙ kuma ya zubo har gadon bayanta.
Waɗannan siffofi guda biyu su Arshan yafi tunowa. To, amma wannan wadda take kwance a gabansa, fatarta ta ɗan yi duhu. Kuma gashin kanta bai yi wani tsaho na azo a gani ba.
A wannan lokaci abubuwan da gimbiya Zonar ta faɗa masa s**a faɗo kansa. Zonar cewa take, ita matsafiya take gani ba Dani ba.
Arshan yayi bincike akan dalilin da yasa aka makantar da gimbiya Zonar a shekarun baya. Kuma ya gano cewa, idanun gimbiya Zonar na musamman ne shiyasa aka yi mata tuggu ta makance.
To, amma a wannan karon gimbiya Zonar bata ce komai ba akan Dani ba. Shin hakan yana nufin asalin Dani ce?
Arshan na cikin waɗannan tunane-tunane nasa, aka turo hadimi daga fadar sarauniya Milisa ana yi masa sallama.
Ajiyar zuciya kawai Arshan yayi ya miƙe tsaye yaje kan gimbiya Dani ya sumbaci goshinta.
Wani ƙarfin iko da ya taso daga jikinta ya doki hancinsa ne ya baiwa Arshan mamaki kuma ya ja da baya a tsorace.
A daidai wannan lokaci taurarin dake kewaye juna a jikin miyurarsa s**a tsaya cak!
Ɗaya daga cikin taurarin ya disashe daga jikin wannan miyura sannan ya bayyana a cikin idon Arshan na hagu.
Wato a wannan lokaci idanun Arshan gaba ɗaya sun koma na taurari kenan.
To, a ɓangaren Arshan kuwa, wani abu yake kallo cikin tsananin mamaki da al'ajabi. Waɗannan idanu nasa na musamman ne.
Wasu taurari guda bakwai Arshan ya gani suna kewaye kan gimbiya Dani. Tartsatsin da waɗannan taurari suke yi ne ya kashewa Arshan idanu.
Wani ilimi ya fara shiga kan Arshan. Ilimin karantar Taurari.
Ganin waɗannan taurari suna ta haske yana nufin akwai sa'a da nasara a tattare da gimbiya Dani kenan.
Arshan ya juya ya kalli gimbiya Zonar. Take yaga irin wadannan taurari guda shida suna ta kewaye kanta. Saɓanin na gimbiya Dani na gimbiya Zonar duhu ne dasu.
Arshan yana murnar ya samu babbar fasaha ta karantar Taurari amma a lokacin tauraron da ya bayyana a cikin idanunsa na hagun ya ɓace ɓat!
Tauraron ya koma cikin miyurarsa sa'annan s**a ci gaba da kewaye juna.
Arshan ya ja dogon numfashi sai a wannan lokaci ya tuno da cewa, ana fa jiransa a fada. Saboda haka cikin gaggawa ya fice daga cikin wannan ɗaki.
Fitar Arshan keda wuya, idanun gimbiya Dani s**a buɗe. Take ta miƙe tsaye ta tunkaro gimbiya Zonar wacce ke kwance tana ta barci sak**akon maganin da ta sha.
Kafun ta riski Zonar ta juye izuwa siffar Kotegà.
Tana zuwa kan gimbiya Zonar ta haɗe hannayenta biyu a waje ta saita daidai idanun gimbiya Zonar.
Wani baƙin haske ya fito daga cikin hannayenta kuma ya shige cikin idanun Zonar a guje Kotegà ta koma kan gadonta ta kwanta kuma ta sake juyewa zuwa k**annin gimbiya Dani.
***
Arshan na fuskanto fadar sarauniya Milisa ya hango wata gawurtacciyar sarauniya zaune akan karagar mulki ta musamman. Milisa tana zaune a gefenta cikin tsananin biyayya.
Arshan na ƙarasowa fadar, wannan sarauniya ta tashi da kanta ta tarɓe shi cikin girmamawa.
Lamarin da ya baiwa Milisa mamaki kenan.
Sai dai Arshan baya iya shaida k**annin wannan sarauniya. Saboda manyan tufafi ta saka waɗanda s**a rufe jikinta gaba ɗaya.
Ta rufe rabin fuskar ta da wani kyakkyawan ƙyalle wanda dukda cewa shara-shara ne amma baka ganin fuskar ta ta.
Ta saka wata hular Fulani akanta wadda ta sauƙo har kan goshinta.
“Suna na Sarauniya Jazwirà. Kada ka tambaye ni fuskata saboda babu wanda ya taɓa ganinta a duk faɗin duniya sai 'yan ƙalilan.
“Nazo ne domin na sanar da kai yadda zaka yi amfani da wannan taswira domin samun nasarar ɗauko Fursunan Littafi!”
Arshan yana jin muryar wannan sarauniya ya fara karkarwa. Ba don komai ba sai domin yadda muryar take k**a da muryar Lasirina Ajamen. To, amma bata kai muryar Lasirina Ajamen zurfi, izza da ƙarfin iko ba.
“Saboda wanne dalili k**e ɓoye fuskar ki a matsayin ki na sarauniya guda?” inji Arshan.
Arshan ya ga ta haɗe kyawawan girarta ta ce, “Nace maka bana so, ka tambaye ni fuskata amma sai da ka tambaya, ko?”
Arshan ya ɗan ja numfashi ya ƙura mata idanu kawai. Kai da gani ka san ya fara gajiya da yadda ake wasa da hankalinsa wajen ɓoye masa abubuwa.
“Muje mu zauna!” inji sarauniya Jazwirà.
Babu musu Arshan ya bi bayanta s**a zauna akan karagar mulkin nan. Milisa ta matso kusa gaban wani ƙaramin teburi dake gaban wannan karaga.
Arshan ya zaro wannan taswira ya shimfiɗa ta akan wannan ƙaramin teburi.
“Babban dalilin da yasa muka kawo wannan Littafi daular ki shi ne saboda kema za ki bayar da gudunmawar ki wajen ɗauko littafin.” sarauniya Jazwirà ta fara yi musu bayani.
“Wannan taswira zata fara aiki ne a cikin wani babban daji wanda ake kira da suna: Céns.
“Wata doguwar tafiya ce ta kusan kwana arba'in akan wata masifaffiyar hanya mai ɗauke da tarin hatsari. Ba abun mamaki bane ku rasa rayukan ku a cikin wannan tafiya, to, amma dole zakuyi ta.”
Sa'adda Jazwirà tazo nan a zancenta sai ta fara nunawa su Arshan abubuwan dake jikin wannan taswira. Abubuwa guda biyu ta nuna musu. Abu na farko, farkon dajin Céns. Abu na biyu, wannan doguwar hanya wadda aƙalla za'a shafe kwanaki arba'in akanta.
Hannun sarauniya Jazwirà yazo kan sashe na ƙarshe na wannan taswira. Akwai zane-zane da tsare-tsare da tarin bayanai a wannan sashe.
“Lokacin da kuka iso wannan waje, kun iso wajen da wannan littafi yake.” sarauniya Jazwirà ta dubi Arshan cikin nutsuwa. “Ka nutsu ka saurare ni da kyau da kunnuwan basira!”
Sarauniya Jazwirà ta nuna wani murfi tamkar murfin rijiya. To, amma anyi masa fasali da waɗansu zanen kibiyoyi guda uku waɗanda suke kallon gabas.
“Za ka juya murfin wannan rijiya sau uku ta ɓangaren gabas!
“Idan kayi haka ka buɗe ƙofar shiga wannan kogo kenan!
“Kayi sani cewa, a cikin wani ƙatoton kogo da aka gina a ƙarƙashin ƙasa zaku tsinci kan ku.”
Sarauniya Jazwirà tasa yatsan hannunta guda ta taɓa jikin wannan murfi. Take yayi haske kuma ya buɗe kansa.
Arshan da Milisa s**a ga wani ƙatoton kogo ya bayyana. Babu komai a cikin wannan kogo sai tarin mayaƙa sunyi shiga ta yaƙi.
A gabansu ne aka nuno wasu ƙofofi guda uku. Guda tana da launin shuɗi. Guda fari. Ta ƙarshen kuwa, baka ƙirim.
“Babu ruwanku da waɗannan mutum-mutumi. Arshan kai zaka ɗiga jininka a jikin wannan ƙofa mai launin baƙi. Da zarar kayi hakan zata buɗe. Tana buɗewa zaka tsinci kanka a cikin kurkukun litattafai.
“Idan kayi kuskuren ɗiga jini a ƙofar da ba wannan baƙa ba. Waɗannan mutum-mutumi zasu dawo rayayyu kuma su afka muku da azababben yaƙi.
“A cikin wannan kurkuku ta littatafa zaka sake ɗiga jininka akan akwati ta 110. Idan kayi kuskure a wannan waje ma. Fursunan Littafi dake cikin akwati ta 110 zai narke. Saboda haka ka kula sosai.
“Na rantse har da darajar Dahasàm. Jinin ka ne kaɗai zai buɗe waɗannan ƙofofi. Koda mutum ya samu nasarar shiga cikin wannan kogo ba zai iya zuwa inda wannan littafi yake ba. Dole sai da taimakon ka.”
Sarauniya Jazwirà tana zuwa nan a zancenta ta ɗago kanta ta dubi Arshan da sarauniya Milisa ta ce, “Ina yi muku fatan alheri da samun nasara!!”
****
Yau *05/07/2025*
Babi na gaba zai zo *07/07/2025* In Sha Allah.