Ruhin Jarumtaka littafin yaki

Ruhin Jarumtaka littafin yaki Gawurtattun littatafan Hausa novel masu dogon zango daga Umar Muhammad da Zahra A. Adamu
(3)

19/10/2025

Karatun littafin RAMIN MUGUNTA.

Assalamu Alaikum muna so mu sanar da ku cewa, ku bibiye mu ta YouTube channel namu domin samun littafin RAMIN MUGUNTA a matsayin audio:

https://youtube.com/?si=fbGIKX8s27o16WWg

Kada dai ku manta, ku danna mana subscribe kana ku danna alamar ƙararrawa 🔔 domin a ringa sanar daku a kullum idan mun ɗaura sabon karatu.

SAI KUN ZO!

NB: YouTube channel zata iya zama hanya mafi sauki da zaku ringa samun ci gaban littafin musamman 'yan facebook da aka yiwa nisa.

RAMIN MUGUNTA!*  MUGUWAR GASA!*Babi na 123: *Isiniym**  *Wannan littafin sadaukarwa ne ga Fatima Umar Muhammad**  Marubu...
19/10/2025

RAMIN MUGUNTA!

*

MUGUWAR GASA!

*

Babi na 123: *Isiniym*

*

*Wannan littafin sadaukarwa ne ga Fatima Umar Muhammad*

*

Marubucin ✍️RUHIN JARUMTAKA ✍️
*

✍️✍️✍️ Marubucin littafi - Muhammad Umar Sangaru✍️✍️✍️

*
*
*

~20 ga watan Mayu.

***

Wannan rana ita ce ranar da za'a zartarwa Dani hukunci.

A wani ɓangare na wannan birni, wata ƙaramar runduna ce ta waɗasu dakaru suke ta tafiya bisa sawayen su.

Yanayin tufafin waɗannan dakaru da mak**an yaƙin dake hannun su, sun sha bamban da na rukunan dakarun dake cikin wannan birni.

Lamarin da yasa a cikin ƙanƙanin lokaci s**a ja hankalin dakarun dake baiwa birnin tsaro kenan.

Tun ana kallon-kallo a tsakanin su har sai da ta fara kaisu ga yaƙar juna.

Lokacin da yaƙi ya rincaɓe a tsakanin rukunan dakarun dake baiwa wannan birni tsaro da kuma wannan baƙuwar runduna.

Kururuwar mazaje da ƙarar karafkiyar ƙarafa ta yawaita. Jini ya rinƙa fallatsi gami da kwarara zuwa ƙasa.

Dakaru daga sassa daban-daban na wannan birni s**a riƙa rugowa da gudu zuwa wannan waje wanda ake fafatawa a cikin sa.

Kafun kace me wannan wajen ya fara cika da tarin gawarwaki. Jini yana ta gudu akan ƙasa gami da ambaliya. Sassan bil'adama suna ta shawagi gami da zubowa ƙasa k**ar takardu.

A wani babban sansani na dakarun dake baiwa wannan birni tsaro kuwa, wani mahayi ne ya shigo cikin sansanin a guje.

Wasu manyan kwamandu s**a tare shi, suna tambayar sa abinda yake faruwa.

"Wata baƙuwar runduna ce ta wasu mutane s**a kawo mana farmaki. Ba sa mutuwa da wuri kuma suna yi mana gagarumar ɓarna."

Koda waɗannan kwamandu s**a ji abinda wannan mahayi ya ce sai s**a cika da tsananin mamaki.

Yadda s**a ƙarfafa tsaro a birnin nan, ba sa tunanin akwai mutumin da ya shigo cikin wannan birni, ba tare da sanin su ba.

Saboda wannan dalili s**a hau dawakan su cikin gaggawa, wannan mahayi ya shige gaba yana nuna musu hanya.

Sai da aka shafe kusan sa'a biyar cir ana fafatawa tsakanin rukunan dakarun wannan ƙasa da wannan baƙuwar runduna da ta kawo hari.

Har zuwa wannan lokaci babu wanda ya san su wane ne wannan runduna ballantana asan dalilin da ya kawo su.

Duk da cewa anyi musu gagarumar ɓarna amma sun baiwa rukunan dakarun dake cikin birnin ciwon-kai.

Bayan sa'a biyar ne, wajen da s**a fafata yaƙin ya zamo babu kyan gani.

Gawarwaki da sassan jikin bil'adama da jinin su s**a cika wannan waje.

Rayukan dakaru da kwamandu masu yawan gaske sun salwanta, lamarin da yasa labari yaje kunnen sarki Ra'alin kenan.

To, amma kafun ya ɗauki wani mataki an nemi wannan baƙuwar runduna sama da ƙasa an rasa wajen da tayi.

Koda masana daga cikin jama'arsa s**a yi duba izuwa siffofin waɗannan dakaru sai s**aa gano cewa, wasu mutane ne daga cikin mutanen dake bautar wani ɓoyayyen addini a doron ƙasa ta bakwai.

Sarki Ra'alin na ganin wannan abu yana da alaƙa da doron ƙasa ta bakwai sai ya cije baki cikin takaici, ya koma cikin kasuwar Yewuri.

A wannan lokaci wannan kasuwa ta cika maƙil da tarin jama'a.

Bayan gama-garin mutanen da s**a zo kallon yadda za'a zartarwa Dani hukunci, akwai sauran sarakunan Ambaha wadanda s**a sa-hannu a kashe Dani.

Wani dogon gini aka gina wanda aka ƙarshensa aka kafa wani dogon itace mai gwafa.

A jikin wannan itace mai gwafa anan aka ɗaura murtuƙeƙiyar igiya wadda za'a rataye wuyan gimbiya Dani da ita.

Gaba ɗaya wannan dogon gini yana saman wani tudu ne wanda zai baiwa 'yan kallo damar ganin dukkan abinda ke faruwa.

Kewaye da wannan dogon gini, kujerun da sarakunan Ambaha zasu zauna akan su ne.

Kowanne sarkin Ambaha ya taho tare da 'yar ƙaramar tawagar sa waɗanda s**a kasance a cikin shirin to kwana.

Sarki Ra'alin yazo ya zauna akan wata karagar mulki wadda take tsakiyar kujerun sarakunan Ambaha.

A hannun daman sa, sarki Ladsin ne daga doron ƙasa ta biyar da kuma sarki Zir'indas daga doron ƙasa ta shida.

A hannun hagun sa kuwa, sarki Ai'yan daga doron ƙasa ta uku ne.

A bayan waɗannan sarakuna guda huɗu, rukunan dakaru ne irin dabam-dabam.

Ko tsuntsu bai isa ya gilma ta saman kansu, ba tare da an harbo shi ƙasa ba.

Wani irin ƙarfin iko wanda yake ɓoye a cikin iskar wannan waje yana ta kaɗawa a hankali a hankali.

Ƙamshin mulki da buwayar dake tasowa daga cikin wannan ƙarfin iko tana kashewa duk wanda yake adawa da abinda ke shirin faruwa a wannan waje gwiwa.

Mutane kaɗan ne s**a taɓa arba da mai wannan ƙarfin iko amma kusan duk wanda yake wannan waje yasan ƙarfin ikon wane ne.

***

A daidai wannan lokaci da kowa ya gama daidaita ana jiran a zartarwa gimbiya Dani hukunci, wasu dakaru guda biyu ne s**a buɗe ƙofar wata tsohuwar kurkuku.

Hasken rana ya dallare idanun wadda ke kulle a cikin wannan ɗaki.

Dakarun s**a danna kai cikin wannan ɗaki s**a ɗauko ta.

Ba ta iya tafiya da sawayenta sosai sai sun tallafa mata saboda wahalar da tasha a cikin wannan ɗaki.

Sanye take cikin tufafin fursunoni waɗanda aka yankewa hukuncin kisa.

Riga da wando ruwan ƙasa masu ratsi-ratsin baƙi.

Duk an rage yawan gashin kanta kuma fuskarta na ɗauke da firgici da tashin hankali wanda yake samo asali daga tsoron mutuwa, hakan bai hana kyakkyawar fuskar ta bayyana ba.

Ba wata bace wannan fursuna sai Dani 'yar sarki Mazurus ta doron ƙasa na huɗu.

Dani ta ci gaba da tafiya akan sawayenta tamkar zata faɗi ƙasa saboda tsananin galabaita.

Bayan doguwar tafiya s**a fito ta cikin wata siririyar ƙofa.

Suna fitowa Dani ta tsinci kanta a saman wannan tudu wanda miliyoyin jama'a s**a kewaye.

Waɗannan dakaru waɗanda s**a ɗauko ta daga cikin wannan ɗaki s**a dafa kafaɗunta s**a ƙarasa da ita gaban wannan gini.

Wani garjejen ƙaton sadauki wanda ya rufe fuskarsa ya karɓi gimbiya Dani daga hannun su.

Garjejen sadaukin ya saka ta a gaba s**a ƙarasa ƙarshen wannan gini wanda aka ɗaura wannan igiya wadda za'a rataye ta da ita.

Koda gimbiya Dani tayi arba da wannan igiya kuma ta fuskanci abinda ake shirin aikata mata sai ta yanki jiki zata faɗi ƙasa.

Wannan garjejen sadaukin yasa hannunsa guda ya riƙota, yayi amfani da ɗayan hannunsa wajen saka mata wata baƙar hula wacce ake sakawa duk wanda za'a rataye.

Gimbiya Dani tana faman sumewa sadaukin ya ƙarasa da ita ƙarshen wannan gini, ya kamo wannan igiya da hannunsa guda, ya zira kan gimbiya Dani a cikin sa.

Abinda kawai ya rage a wannan lokaci shi ne, ya ture sawayen Dani daga kan wata karamar kujera da take tsaye a kanta.

Sai dai a daidai lokacin ne, sarki Ra'alin ya miƙe tsaye ya fara yiwa jama'a bayanin laifin da gimbiya Dani ta aikata.

Gimbiya Dani bata cikin hayyacinta sosai ballantana tasan abinda yake cewa, bayan ɗan lokaci yana ta magana saiya dubi wannan sadauki ya ce, ya tambayi gimbiya Dani ko tana da wata wasiyya?

"Arshadan!" inji Dani cikin murya mai nuna karayar zuciya da bankwana da duniya.

SarkiRa'alin yayi dariya ya ɗaga hannunsa guda sama, niyyar sa ita ce yana sauƙar da hannun, za'a ture wannan kujera wadda Dani take tsaye akanta.

Da zarar an ture wannan kujera kuwa, wuyanta zai karye ta mutu.

Ba zato ba tsammani! Wani gagarumin baƙin hayaƙi ya turnuƙe sararin samaniya.

Da samuwar wannan baƙin hayaƙi a sararin samaniya gwara samuwar baƙin hadari saboda zai fiyewa halittu sauƙi.

Wata irin koriyar wuta ta fara feshi daga cikin wannan baƙin hadari tana sauƙowa ƙasa tana babbake mutane suna ƙonewa ƙurmus.

Kafun sarki Ra'alin da sauran Ambaha su fuskanci abinda yake faruwa a wannan waje, tuni wajen ya hargitse.

Jama'a sun fara ihu da guje-guje.

Sai dai wannan sauyin yanayi bai hana wannan sadauki dake tsaye a gaban gimbiya Dani ture kujerar da take tsaye a kanta ba.

Sawayen gimbiya Dani s**a fara wutsil-wutsil, wuyan ta yana faman karyewa.

A daidai lokacin sararin samaniya ta sake cika da tsawa da walƙiya.

Cikin ƙiftawar ido wata zabgegiyar takobi ta sauƙo daga cikin wannan baƙon yanayi. Kafun kace me wannan ma'abocin wannan takobi ya kai sara da ita.

Wani faifan walƙiya a cikin gudun haske yaje ya tsinke igiyar da ta ɗaure wuyan gimbiya Dani.

Gimbiya Dani ta faɗo ƙasa daga kan wannan gini.

A wannan lokaci tuni wannan waje ya hargitse, im banda guje-guje da iface-iface babu abinda ake.

Tuni gagarumin duhu ya mamaye wannan waje, kai kace dare ya kusanto alhali kuwa tsakiyar rana ce.

Inda ace abun ya tsaya iya duhu, da da sauƙi. To, amma a lokaci guda wasu dunƙulen walƙiya ne suke ta sukuwa tsakanin sama da ƙasa.

Wannan sadauki wanda zai zartarwa Dani hukunci, ya daka tsalle daga inda yake tsaye ya dira a gaban gimbiya Dani.

Sadaukin ya zaro wani ƙatoton sungumi na duka daga gadon bayansa.

Saboda girman wannan sungumi yafi kan gimbiya Dani girma kuma yana ta cako-cakon ƙaho.

Duk tsautsayin da yasa ya dokawa Dani wannan sungumi aka, sai kanta ya taarwatse ƙwaƙwalwarta ta baje.

Sadaukin ya ɗaga wannan sungumi sama zai dokawa gimbiya Dani aka, domin ya ƙarasa aikin da sarkinsa ya saka shi.

Kafun ya ƙarasa mugun nufinsa akanta, tuni wani haske ruwan-ƙasa ya taho cikin matsanancin gudu ya buge shi.

Kusan duk wanda yake hayyacinsa a wannan lokaci saida ya juyo domin ganin abinda ke faruwa da wannan sadauki.

Sadaukin ya buɗe bakinsa zai kwarara uban ihu, amma kafun ihun ya gama fitowa tuni jikinsa yayi wani irin haske. Ƙwarangwal ɗin jikinsa ya bayyana na tsahon daƙiƙu biyu kacal.

A daƙiƙa ta gaba kawai gani akayi wannan sadauki ya sulale ƙasa matacce, ko shurawa bai yi ba.

Al'amarin da ya baiwa duk wanda ke wannan waje mamaki kenan. Saboda ba'aa taɓa ganin fasaha mai saurin kashe mutum k**ar wannan ba.

Gimbiya Dani ta sake faɗuwa ƙasa saboda tsananin firgici kuma har a wannan lokaci fuskarta a rufe take sa'annan kuma hannayenta a ɗaure suke ta baya.

Wannan baƙin hayaƙi wanda ya cika sararin samaniya ya fara dunƙulewa a waje guda.

Sarki Ra'alin da sauran Ambaha a wannan lokaci tuni sun miƙe tsaye suna ƙoƙarin zaro mak**an yaƙin su.

Sauran dakarun dake basu tsaro kuwa tuni sun fara guje-guje suna tunkarar wajen da wannan baƙin hayaƙi yake taruwa.

A daidai wannan lokaci ne, siffofin wani kyakkyawan saurayi s**a fara samuwa daga dunƙulen walƙiya wadda tayi ragowa daga hare-haren ɗazu.

Lamarin da yasa hankalin waɗannan dakaru ya rabu gida biyu kenan, kaso guda s**a tunkari inda wannan baƙin hayaƙi yake samuwa, kaso guda s**a tunkari wannan kyakkyawan saurayi.

Sai dai zaka iya cewa sunyi gaggawa, idan ka fuskanci abinda ya sake faruwa a gaba.

Waɗansu mahaya guda goma ne sanye cikin baƙaƙen tufafi s**a bayyana, s**a taho a guje cikin azababben gudu, s**a fara karkashe waɗannan dakaru.

Cikin ƙanƙanin lokaci waɗannan dakaru s**a shiga cikin gagarumin masifa.

Waɗannan mahaya guda goma sun kasance asalin ƙwararrun mahaya kuma jarumai masu baƙin zafin nama.

A cikin daƙiƙa goma suna iya karkashe dakarun dake wannan waje masu ɗumbin yawan gaske.

Kafun kace me wannan, sun tashi hankalin dakarun dake wannan fili.

A daidai wannan lokaci ne, wannan baƙin hayaƙi ya gama dunƙulewa a waje ya ringa tsiri yana tokarewa da sararin samaniya.

Kamar tasowar inuwa daga cikin ƙarƙashin ƙasa, haka wannan mutumi ya miƙe tsaye.

Tsahon wannan mutumi ya ninka na ainihin bil'Adama wajen sau huɗu.

Kaurin jikinsa tamkar bishiyar giginya.

Duk wannan bai ja hankalin Ambaha dake wannan waje ba, babban abinda ya ja hankalin su shi ne, wani kakkauran baƙin hayaƙi wanda yake fita daga cikin gashin wannan mutumi.

"Sarki Mazurus Asaryan?" inji sarki Ladsin wanda ga dukkan alamu ya riga kowa gano wane ne wannan mutumi.

Hakane, wannan baƙon mutumi ba kowa bane illa sarki Mazurus wanda ake kira Erengalos.

Babu takobi babu makamin komai a hannun sarki Mazurus. To, amma da abinda s**a gani a hannunsa gwara ace takobi s**a gani.

A tare gaba daya Ambaha guda huɗun s**a buɗe baki, s**a ce, "FASAHAR RUHI?"

Haba dole mana, su sun yi mamakin yadda aka yi wannan sadauki yayi mutuwa ta farat ɗaya kuma ƙwarangwal ɗin jikinsa s**a bayyana.

Tabbas fasahar Ruhi ce tayi ajalin sa.

Sarki Mazurus ya tsaya ya fuskanci wadannan sarakuna guda huɗu, shi ɗaya jal.

A wannan lokaci ya ɗan motsa hannunsa guda, take rundunar sa ta bayyana a bayansa.

Sarki Mazurus yana sanye da doguwar alkyabba ruwan toka wadda aka yiwa ado da dinare.

Akansa ya saka wani kambu na mulki baƙi ƙirim, sai ka lura sosai zaka fuskanci akwai wannan kambu.

Hakan ya samo asali ne sak**akon wani kakkauran baƙin hayaƙi dake tashi daga gashin kansa.

Idan ka lura da wannan baƙin hayaƙi wanda ya mamaye sararin samaniya a ɗazu. Zaka tabbatar da cewa, irin sa ne sak yake fita daga kan sarki Mazurus.

Lamarin da ya sake girgiza mutane kuma ya basu tsoro kenan, saboda sun fuskanci wannan baƙon yanayi da s**a yi tsinkaye dashi a ɗazu yana da alaƙa da sarki Mazurus.

A bayan sarki Mazurus zaratan dakaru ne, waɗanda duk da cewa basu da yawa amma ganin su kadai ya isa ya firgita karamin jarumi ya cika wandonsa da iska.

Ba komai ne ya janyo hakan ba, sai ganin cewa, gaba ɗaya cikin wannan runduna tasa babu wanda bai taka matsayin Otaki ba.

Kai akwai wasu mutum goma a bayansa, wadanda har sun samar da Otaki mai inuwa a saman kansu.

A daidai wannan lokaci, wadannan mahaya guda goma masu sanye da baƙaƙen tufafi suna ta sha'aninsu a tsakiyar waɗannan dakaru.

A wannan lokaci wannan saurayi wanda jikinsa yake samuwa daga wannan walƙiya ya gama haɗewa a waje guda.

Ba wani bane wannan saurayi sai Arshan.

Yana sanye da falmara ta fatar damisa a jikinsa, wandonsa baida tsaho sosai domin kuwa da kadan ya wuce gwiwar sa.

A hannunsa yana riƙe da takobin Sikai.

Arshan yayi juyi da takobinsa ya sari iska da ita.

Nan take ita kanta iskar ta k**a da walƙiya. Dakarun dake kewaye da Arshan s**a fara ƙonewa ƙurmus suna komawa toka.

Kafun kace me wannan Arshan ya karkashe su duka.

Arshan ya daka tsalle ya dira a gaban gimbiya Dani.

Jarumin yasa hannunsa guda ya fidda wannan baƙar hula da ta rufe mata fuska.

Idanun gimbiya Dani s**a yi arba da fuskar Arshan a wannan lokaci.

"Arshadan?!" inji Dani.

****

THANKS 4 READING

RAMIN MUGUNTA!*  MUGUWAR GASA!*Babi na 122: *Yaƙi yana nan tafe**  *Wannan littafin sadaukarwa ne ga Fatima Umar Muhamma...
10/10/2025

RAMIN MUGUNTA!

*

MUGUWAR GASA!

*

Babi na 122: *Yaƙi yana nan tafe*

*

*Wannan littafin sadaukarwa ne ga Fatima Umar Muhammad*

*

Marubucin ✍️RUHIN JARUMTAKA ✍️
*

✍️✍️✍️ Marubucin littafi - Muhammad Umar Sangaru✍️✍️✍️

*
*
*

~Kasuwar Yewuri.
~Doron ƙasa ta takwas.

***

An gina wani babban gini wanda daga can ƙarshen sa, aka rataya wata murtuƙeƙiyar igiya wadda za'a yi amfani da ita wajen rataye gimbiya Dani.

An ƙawata wannan waje da kujeru na alfarma waɗanda sarakunan Ambaha zasu zauna akan su suyi kallo, a yayin da za'a yankewa gimbiya Dani hukunci.

An baiwa wannan kasuwa gagarumin tsaro na musamman, ta yadda duk wani motsi dake faruwa a cikin wannan kasuwa akwai idanun dakaru suna kallo.

Birnin sarki Ra'alin kuwa, tsaron da aka baiwa wannan birni ba'a magana.

A wannan lokaci saura kwanaki arba'in kacal, ranar da za'a zartarwa gimbiya Dani hukunci ta zo.

Tuni sarki Ra'alin ya fitar da sanarwar gargaɗi ga duk wanda yake tunanin kawowa gimbiya Dani ɗauki.

Tsarin da sarki Ra'alin yayi amfani dashi wajen yankewa gimbiya Dani hukunci halastaccen tsari ne.

Duk wanda yayi fito na fito da wannan tsari tamkar yayi fito na fito da ƙabilar Jorash ne.

Wannan dalilin ne yasa sarki Ra'alin ya fitar da wannan gargadi.

Sarki Ra'alin ya san cewa, mahaifin gimbiya Dani ba zaiyi shuru ba. Wannan ma na daga cikin dalilan da s**a sa ya fitar da wannan sanarwa.

Kusan kowacce rana sai sarki Ra'alin ya kaiwa gimbiya Dani ziyara a ɗakin da aka kulleta na kurkuku.

Duk da cewa gimbiya Dani a wulaƙance take kuma a kulle, amma hakan bai sa kyawunta ya ragu ba.

Lamarin da yake matuƙar baiwa sarki Ra'alin mamaki kenan.

Sarki Ra'alin ya san wace ce GIMBIYA ZONAR, amma ba don haka ba da tuni ya daɗe da kamuwa da soyayyar gimbiya Dani.

Sarkin ya ƙudurce a ransa, da zarar ya zartarwa gimbiya Dani hukunci zai kaiwa sarki Amuru mai makaranta ziyara, daga nan sai ya faɗa masa buƙatar sa.

Idan zaka tuna sa'adda Dorhos ya kawowa sarki Ra'alin gimbiya Dani ya bar mutuminsa guda ɗaya wanda sarki Ra'alin zai na sanar dashi abubuwan da ke faruwa.

Shi kuma zai na sanar da shugabansa Dorhos.

A wannan lokaci Dorhos ya samu labarin dukkanin abinda yake faruwa.

Kuma zaka iya cewa, shima a nasa ɓangaren yana can, yana ta shirye-shirye.

To, a daidai wannan lokaci idan kayi duba izuwa ƙofar shiga cikin birnin sarki Ra'alin zaka yi arba da wani mutum tsaye a gaban dakaru suna ta yi masa tambayoyi.

A bayan wannan mutumi tarin kekunan dawakai ne waɗanda suke ɗauke da madarar shanu a cikin manya-manyan tukwane.

Wannan mutumi ba baƙo bane, hasalima haifaffen wannan birni ne amma saboda halin da ake ciki, ba'a barshi ya shiga cikin wannan birni kai tsaye ba.

Bayan ya gama amsa tambayoyin da ake yi masa, sai wasu daga cikin waɗannan dakaru s**a zo s**a fara caje wannan madarar shanu da ya ɗebo.

Tsahon ɗan lokaci suna ta bincika waɗannan tukwane, sa'annan s**a gama duba rabin su.

A wannan lokaci shugaban su ya basu umarnin dakatawa.

"Ku barshi ya wuce," inji shugaban nasu.

Wannan mutumi ya ɗan risina a gabansu cikin girmamawa kafun ya sakarwa dokinsa linzami ya wuce.

Sauran kekunan dawakan s**a take masa baya da gudu.

Bai sake fuskantar matsalar komai ba, ya ci gaba da danna kai a cikin wannan birni.

Bayan tafiyar sa'a goma cir ya iso unguwar da yake.

Ganin ya kawo madarar shanu unguwar ya baiwa mutanen unguwar mamaki. Kamata yayi ace kasuwa ya kaita k**ar kullum amma a wannan karon ya kawo ta gidan sa.

Mutumin ya sauƙa daga kan dokinsa, ya kawo keken doki guda huɗu ya shige dasu cikin gidansa.

Sai da ya tabbatar ya gama nutsewa a cikin wannan gida, sannan ya tsayar da kekunan dawakan.

A hankali ya rinƙa buɗe murafan waɗannan tukwane. Take mutane s**a fara tasowa daga cikin tukwanan suna bayyana.

A ƙalla mutanen zasu kai goma sha.

Kana kallon waɗannan mutane zaka cika da tsananin mamaki.

Koda yake idan ka kalli na gaban su sai kafi kowanne lokaci cika da tsananin mamaki.

Kyakkyawan saurayi ne wanda duk macen da tayi masa kallon farko sai ta yaba.

Saurayin ya rufe goshin sa da idanunsa na dama da wani baƙin ƙyalle.

Sai dai hakan ba zai hana ka gano wane ne ba.

Ba wani ba illa Arshan, idan har ka san wane ne Arshan.

Shin mene ne abinda ya kawo Arshan wannan waje?

Zaka iya cewa, Arshan ya shigo cikin doron ƙasa ta takwas ne ta ɓarauniyar hanya.

Hakan ya samo asali ne sak**akon hana shige da fice da sarki Ra'alin yayi a cikin wannan doron ƙasa.

Mu dawo kan wannan tambaya ta farko. Mene ne abinda ya kawo Arshan wannan waje?

Amsar wannan tambaya zaka iya cewa, an yankewa gimbiya Dani hukuncin kisa a cikin wannan doron ƙasa.

Sarki Ra'alin yasan zartarwa Dani hukunci ba zai taɓa yiwuwa ba, har sai ya ƙarfafa tsaro a doron ƙasar sa.

Gimbiya Dani tana da mahaifi kuma tana da magoya baya da tarin masoya waɗanda ba zasu taɓa bari a hallaka ta abanza ba.

Waje na ƙarshe da muka yi arba da Arshan shi ne, cikin doron ƙasa ta bakwai a babban ɗakin karatu na Amuru mai makaranta tare da gimbiya Zonar.

Ta ya ya aka yi muka ga Arshan a wannan waje maimakon doron ƙasa ta bakwai?

Zaka samu amsar wannan tambaya, idan kayi duba izuwa abinda ya faru wasu kwanaki kafun wannan rana.

****

~Doron ƙasa ta bakwai.

****

Arshan da gimbiya Zonar s**a dawo fadar sarki Amuru daga wannan babban ɗakin karatu.

A cikin wannan ɗakin karatu dai, an baiwa Arshan littafin Al'ajabi kuma ya karanta babuka guda uku daga cikin wannan littafi.

Babukan dake magana akan taurarin dake ɗamfare a jikin miyurar sa.

A cikin wannan fada s**a ci gaba da tattaunawa akan wannan yaƙi da ke tunkaro su da kuma yadda zasu tafiyar da komai.

Sarki Amuru mai makaranta ya ja dogon numfashi ya dubi Arshan ya ce.

"Babu ƙuri'ata a wannan hukunci da aka yankewa gimbiya Dani saboda haka wannan yaƙi bai shafe ni.

"Saboda idan na shiga wannan yaƙi zan iya jawowa kaina tuhuma daga manya.

"Na yanke shawarar komawa gefe a lokacin da ake fafata wannan yaƙi.

"Duk da cewa ba zan saka hannuna a wannan yaƙi ba, amma ta bayan fage zan taimaka wajen ganin ba'a cutar da gimbiya Dani ba."

Lokacin da sarki Amuru msi makaranta yazo nan a maganganunsa sai Arshan yaji sarkin yayi matuƙar burge shi.

Zaka iya cewa, sarki Amuru tarar aradu yayi da ka da ya zamo na farko daga cikin Ambaha wanda ya ƙi amincewa da buƙatar sarki Ra'alin.

Ganin rashin amincewar sa ce tasa sarki Jaha-Jana shima ya ƙi amincewa.

Koda ace iya wannan abun sarki Amuru mai makaranta yayi sai ya burge Arshan ballantana kuma yana maganar taimakawa wajen ganin ba'a hallaka gimbiya Dani masoyiyar Arshan ba.

Abun tambayar a wannan lokaci ita ce, ta ya ya sarki Amuru zai taimaka wajen ganin ba'a kashe gimbiya Dani ba?

Bayan nan mene ne dalilin sa na yin hakan?

Saboda ya ƙi amincewa da buƙatar sarki Ra'alin, ba abun mamaki bane. Akan samu sauyin ra'ayi ko rashin daidato a tsakanin sarakunan Ambaha.

Sanin wannan dalili yana daga cikin abubuwan da Arshan yake son sani.

Musamman idan ka tuno da cewa, wannan mutumi wanda Arshan yake ɗauka a matsayin mara asali, ya bashi labarin wata mata wadda ya alaƙanta ta da gimbiya Dani.

Wannan mata ba wata bace illa Isiniym.

Awarsu wanda ya baiwa Arshan labarin Isiniym ya gagara gamsar da Arshan yadda aka yi Dani ta zamo Isiniym.

Hakan ne yasa kwakwanton labaran da wannan mutumi yake baiwa Arshan yasa kwakwanto ya shiga ran Arshan.

"Baka tunanin taimakawa gimbiya Dani ta bayan fage zai sa ka fuskanci matsala, idan aka gano ka?" Arshan ya ce.

Sarki Amuru yayi guntun murmushi wanda ya dace da ƙarfin ikon sa ya ce, "Idan na ga damar aiwatar da abu ta bayan fage, hatta Yarima ba zai taɓa gano ni ba.

"Saboda haka ka kwantar da hankalinka babu wanda zai san shirina ballantana su gano ni!"

Arshan yana jin wannan batu yayi shuru yana tunani.

Sarki Amuru yafi shi sanin abinda zai faru, idan asirinsa ya tonu. Saboda haka ba zai taɓa yin ganganci da rayuwar sa da muƙamin sa ba.

"Ta ya ya zaka taimakawa Dani ta bayan fage?"

Sarki Amuru ya ce, "Akwai wani rukuni na musamman daga cikin dakaruna da nake kira da suna, Ashura.

"Da taimakon waɗannan dakaru guda goma zan iya baiwa mahukuntan doron ƙasa ta takwas gagarumin koma baya a ƙoƙarin su na zartarwa Dani hukunci."

Arshan yana jin wannan batu yaji ya samu gagarumar dama wacce zai yi amfani da ita wajen shiga doron ƙasa ta takwas.

Duk da Arshan zai iya amfani da fasahar Kabancan wajen shiga doron ƙasa ta takwas (tun da ya taɓa zuwa) amma shigar sa tare da dakarun Amuru wadanda yake kira [rukunin] Ashura zai fi.

Abu na farko saboda yadda Amuru yake ta ruruta su.

"Rukunin Ashura, wani rukuni na zaɓaɓɓun dakaru guda goma daga cikin dakarun ƙasa ta.

"Horon da aka baiwa wannan rukuni na musamman ne. Na yarda da su kuma na yarda da cewa, babu wajen da ba zasu shiga a duniya suyi yaƙi ba.

"Yau saura kwana arba'in da uku a zartarwa Dani hukunci. Daga yau zan tura su birnin sarki Ra'alin, zasu mayar da hankali wajen karantar wannan birni da yadda zasu samu nasarar daƙile hukuncin da ake son zartarwa Dani."

Arshan yana jin wannan batu yayi farin ciki. Shima wannan shi ne, shirinsa yana son shiga doron ƙasa ta takwas da wuri domin fahimtar birnin da kuma lissafin yadda zai daƙile hukuncin da aka yanke mata.

Saboda wannan dalili Arshan ya sake yanke shawara a zuciyar sa da waɗannan dakaru zai yi wannan tafiya.

Abinda kawai ya tsayawa Arshan a ransa a wannan lokaci shi ne, mene ne dalilin da zai sa Amuru mai makaranta zai kuɓutar da gimbiya Dani?

Koda ya yiwa Amuru mai makaranta wannan tambaya sai sarkin yai murmushi ya dube shi yace.

"Saboda gimbiya Dani ita ce Isiniym wadda gaba ɗaya halittun duniyoyi suke nema!"

Maganar sarki Amuru tayi kunnen doki da maganar Awarsu a wannan waje.

Idan Arshan zai tuna Awarsu ya faɗa masa cewa, kusan duk mutumin da yake neman duwatsun daraja guda uku, tofa yana buƙatar Isiniym.

Arshan ya yamutse fuska ya ce, "Ta ya ya aka yi gimbiya Dani ta zamo Isiniym?"

Zuwa yanzu zaka iya cewa, Arshan ya samu gamsuwa a ransa Dani ita ce Isiniym.

Wannan ƙaramar yarinya wadda aka haifa a tsakiyar dokar daji. Jaririya ta farko da tazo da siffar mutane maimakon irin wannan siffa mai ban tsoro.

Abinda kawai Arshan yake son ji a wannan lokaci shi ne, tabbatarwa.

"Ba zaka taɓa samun amsar wannan tambaya taka ba, har sai ka karanta Ɓoyayyen Labarin Ka.

"Tabbas a cikin wannan labari ne, zaka san wace ce Isiniym da dalilin da yasa gaba ɗaya halittun duniyoyi suke nemanta."

Lokacin da sarki Amuru yazo nan a zancensa sai Arshan ya cije haƙora cikin tsananin takaici, yana tuno yadda wannan littafi ya salwanta a hannunsa.

Gimbiya Zonar a gefe guda kuwa, wani kallo ta yiwa Arshan mai cike da tsokana da zolaya, ba tare da ya sani ba.

Wannan shi ne abinda ya faru a doron ƙasa ta bakwai, bayan Arshan ya yanke shawarar shigowa cikin doron ƙasa ta bakwai tare dakarun Amuru waɗanda yake kira Ashura.

Kuma wannan shi ne yadda aka yi muka kalli Arshan tare da waɗannan dakaru a cikin doron ƙasa ta takwas, bayan sun shigo cikinta ta ɓarauniyar hanya.

Shin ta ya ya su Arshan zasu daƙile wannan hukunci da za'a zartarwa gimbiya Dani?

Daga wannan rana Arshan tare rukunin waɗannan dakaru s**a ci gaba da bincike da lissafi akan yadda zasu ɓullowa wannan al'amari.

Kwanaki s**a ci gaba da tafiya har tsahon kwanaki talatin da tara.

A wannan rana saura kwana guda jal ranar da sarki Ra'alin ya ayyana tazo.

An kammala shirya komai yadda za'a rataye gimbiya Dani.

Sarki Ra'alin ya tabbatar da cewa, kowanne lungu da saƙo na birnin sa akwai zaratan dakaru wadanda ke sa ido.

Hakan yasa ya samu gamsuwa ɗari bisa ɗari a ransa, babu wanda ya isa ya dakatar dashi daga abinda yake shirin yi.

A daidai wannan lokaci a wannan rana, a wani daji maras nisa da birnin sarki Ra'alin, wani baƙin hayaƙi ne ya turnuƙe sararin samaniya.

Kai kace gagarumar wuta abar ruruwa aka hura daga ƙasa, idan kaga yadda wannan baƙin hayaƙi yake ta ambaliya yana ruri.

Lamarin da yasa namun dawan dake cikin wannan daji guduwa da neman maɓoya kenan.

Sai dai hakan zai iya zuwa da sauƙi, idan ka kwatanta shi da abinda ya faru na gaba.

Wata irin baƙar wuta ta rinƙa feshi daga cikin wannan hayaƙi.

Take bishiyoyin dake cikin wannan daji s**a fara babbakewa. Namun dawan dake kusa kuwa s**a fara soyewa.

A hankali wannan baƙin hayaƙi ya fara yiwo ƙasa-ƙasa, har ya iso saman bishiyoyin dake ci da wuta.

A daidai wannan lokaci ne, wani irin masifaffen ƙarfin iko ya cika wannan daji gaba ɗaya.

Inda ace ruhin halitta yana kusa da wannan ƙarfin iko da ya kasance ma'abocin ƙololuwar biyayya ga wannan ƙarfin iko.

Duk da cewa idanu basuyi arba da wannan ƙarfin iko ba, amma tuni sun tsorata da abinda zai iya faruwa.

A hankali wannan baƙin hayaƙi ya rinƙa dunƙulewa, yana curewa a waje guda.

Kamar an tsaga ƙasa, haka wani shirgegen mutumi ya miƙe tsaye daga ƙarƙashin ƙasa.

Kallon farko ruhin halitta zai yiwa wannan mutumi, wani irin ƙarfin iko ya daki ruhin sa.

Yana sanye da doguwar alkyabba ruwan toka mai ado da dinare.

Hannunsa na hagu ya kasance mai cike da gashi-gashi.

Daga ƙarshen wannan hannu, ɗaya daga cikin duwatsun daraja Anishiyos ne yake ta haske da tartsatsi yana ɗaukar idanu da bayar da tsoro.

Idan ka san sarki Mazurus mahaifin gimbiya Dani zaka tarar shi ne a wannan waje, ba wani ba.

Erengalos mai fasahar ERENUR.

Shin ina sauran dakarun Erengalos wadanda ya taho da su?

Mene ne dalilin da yasa muka kalle shi, iya shi ɗaya?

Rukunin dakarun sarki Ra'alin waɗanda ke kula da dazuzzuka tuni sun rugo zuwa wannan daji domin abinda ke faruwa.

A wannan lokaci tuni sun ƙaraso gaban Erengalos a guje.

Kafun su yi wani abu, tuni Erengalos ya yamutse fuska kuma ya nuna su da fasahar Erenur.

Nan take waɗannan dakaru gaba ɗayan su s**a ƙame na tsahon daƙiƙu biyu kacal. Zanen ƙwarangwal ɗin jikinsu ya bayyana a jikin fatar su.

A daƙiƙa ta gaba ɗaya waɗannan dakaru s**a zube ƙasa matattu.

Erengalos ya motsa hannun sa guda, take mutanen sa s**a fara bayyana k**ar waɗanda ke tsago iska suna fitowa.

Cikin ƙanƙanin lokaci gagarumar runduna ta sadaukai ƙarƙashin jagorancin Sarki Mazurus s**a gama bayyana.

******

Yauwa.

RAMIN MUGUNTA!*  MUGUWAR GASA!*Babi na 121: *Za mu ci gaba**  *Wannan littafin sadaukarwa ne ga Fatima Umar Muhammad**  ...
05/10/2025

RAMIN MUGUNTA!

*

MUGUWAR GASA!

*

Babi na 121: *Za mu ci gaba*

*

*Wannan littafin sadaukarwa ne ga Fatima Umar Muhammad*

*

Marubucin ✍️RUHIN JARUMTAKA ✍️
*

✍️✍️✍️ Marubucin littafi - Muhammad Umar Sangaru✍️✍️✍️

*
*

Sarki Bar Hu Wanjam yayi murmushi ya dubi Majanun ya ce.

“Mutumin da hatimin fasahar Lokaci kaso mafi rinjaye yake ɗamfare akan goshinsa shi ne, Jatraes!

“Sarki Jatraes ya mutu kimanin shekaru dubu ɗari da arba'in baya. Gaba ɗaya mutanen da s**a rayu s**a san zamanin sarki Jatraes sun ƙare daga duniya.

“Binciken kimiyya da fasaha ya gano zanen wani tsohon hatimi da aka zana a jikin wani dogon tsauni dake ƙarƙashin wata babbar teku a duniyar X.

“Masana tarihi da binciken fasahohi sun tabbatar mini da cewa, wannan zane shi ne wanda yake jikin miyurar sarki Jatraes.

“Idan kayi la'akari da haka, kaga mun gano inda zanen wannan hatimi yake. Hatimin fasahar Lokaci wanda zamuyi amfani dashi wajen saka fasahar Lokaci a cikin jikin ka.”

Maganganun Bar Hu Wanjam a wannan lokaci basa buƙatar ƙarin bayani ko tambaya saboda haka Majanun kasa kunne kawai yayi ya ci gaba da saurare.

Sarki Bar Hu Wanjam ya ci gaba da cewa, “Su kuwa waɗannan mutane guda uku da na baka labari. Salsa kenan. Na riga naji yanayin su a kusa da kai sa'adda kake cikin duniyar doron ƙasashe tara.

“Bari na nuna maka su ɗaya bayan ɗaya domin ka fuskanci zancen.”

Sarki Bar Hu Wanjam yana zuwa nan a zancensa ya nuna wannan allon gilashi da hannunsa guda.

Idanun Majanun, T'chai da Kilarà da Sairana s**a koma kan wannan allo dake gefe guda.

Allon yayi haske ya nuna k**annin wata jaruma wadda Majanun yayi mata farin sani.

A daƙiƙa ta gaba Majanun ya haɗe gira cikin mamaki.

“Sinarà Jani?!” inji Majanun. “Wannan ai ta daɗe da mutuwa. Ta mutu sa'adda naje ɗauko kwari da bakan Munàr E. Zogò!!” ya ƙarasa maganar sa yana kallon Bar Hu Wanjam.

Murmushi sarki Bar Hu Wanjam ya sake yi.

“Saurara ka ji. Idan baka manta ba, nace maka jini baya ƙarya.

“Wannan budurwa 'yar wata ƙabila ce da ake kira Zarjard k**ar yadda ta faɗa maka. To, amma abinda bata sani ba shi ne, ita ba 'yar ƙabilar Zarjard bane.

“Ita 'yar wata ƙabila ce da ake kira da suna, Sinarà.

“Mutanen wannan ƙabila suna da tsananin ilimi da sanin tarihin doron ƙasashe tara.

“Eh na yarda ta mutu amma akwai wata budurwa 'yar wannan ƙabila mai irin siffofin ta, zubinta da tsarin ruhin ta.”

Sarki Bar Hu Wanjam yana zuwa nan a zancensa ya nuna wannan allon gilashi da hannunsa guda. Take hoton Sinarà Jani ya ɓace, hoton wata kyakkyawar budurwa ya maye gurbin ta.

Inda ace Arshan da gimbiya Zonar suna wannan waje da sai sun riga kowa gano wannan budurwa.

Ba wata bace wannan budurwa sai Gimbiya Siyara Shauwat 'yar sarki Takuruku na birnin Mahajó dake doron ƙasa ta biyu.

Karo na farko da mai saurare yai arba da wannan budurwa yayi kwakwanto akan anya babu alaƙa tsakanin ta da Sinarà Jani wadda yarima Ra'alin ya kashe?

A yau, zaka iya cewa an amsa wannan tambaya.

To, amma shi Majanun bai san wannan budurwa ba. Bai taɓa kallonta ba, sai a wannan rana.

“Wace ce wannan budurwa wadda take tsananin k**a da Sinarà Jani?”

Sarki Bar Hu Wanjam ya ce, “Wannan budurwa ana kiranta da suna Siyara Shauwat.

“Ta kasance 'ya kuma gimbiya a wajen sarki Takuruku na birnin Mahajó dake doron ƙasa ta biyu.”

Sarki Bar Hu Wanjam ya ɗan yi shuru sa'adda yazo nan a zancensa.

Majanun ya ce, “Idan zata maye gurbin Sinarà Jani, meye amfanin nuna min Sinarà Jani wadda ta riga ta mutu?”

“Saboda na nuna maka kuskuren da ka aikata!” inji Bar Hu Wanjam a taƙaice. “Makamin Munàr E. Zogò dole ne ya kasance a kusa da kai, a kowanne lokaci.

“Saboda makami ne wanda ɗaya daga cikin salsanka zai na sarrafawa!”

Majanun yayi shuru yana tunani. Kuskure? Shin wanne kuskure ya aikata?

A tunaninsa wajen ɓatar Munàr E. Zogò ko kaɗan babu laifin sa.

“Bani da hannu wajen ɓatar Munàr E. Zogò, meye kuskuren da na aikata?”

Karo na farko sarki Bar Hu Wanjam ya haɗe gira, “Rashin bincike! Meyasa baka yi bincike akan wanda ya kashe Sinarà Jani ba?

“Ka riga ka san cewa, wannan kwari da baka ba zai tafi da ƙafafunsa ba. Dole wani ne yazo ya ɗauke shi kuma ya sare kan Sinarà Jani.”

Majanun yana jin haka ya fara tuno lokacin da wannan abu ya faru. A wancan lokacin sun je sun samu gawar Sinarà Jani; shi da Asnaki Jayà.

Majanun yayi tunanin mutanen ƙabilar H'ƙamru ne s**a kashe ta, hakan yasa ya tuhume su.

To, amma daga baya sun yi masa rantsuwa akan ba su bane. Majanun yasan zai yi wahala suyi masa rantsuwa akan ƙarya.

Ba zato ba tsammani! Yanayin wannan mutumi wanda Majanun yaji a kusa da su sa'adda s**a dauko Munàr E. Zogò a cikin kogon Zogoros ya faɗo ransa.

Majanun ya rintse idanu. A wancan lokaci Majanun ya so yayi bincike akan wannan mutumi amma sai Sinarà Jani ta hana shi.

Majanun ya sake tuno cewa, Kilarà ya ce masa zasuyi bincike akan wannan mutumi daga baya. Shi dai kawai ya riƙe yanayin jikin mutumin.

Majanun ya juya ya dubi Kilarà ya ce masa, “Wane ne wannan mutumi wanda kace na riƙe yanayin sa, zamuyi bincike akan sa daga baya?”

Kilarà yana jin wannan tambaya ya tako yazo gaban Majanun ya tsaya. Daga can ya dubi sarki Bar Hu Wanjam ya ce.

“Mun ɗauki babbar shaida wadda zamu gano makashin Sinarà Jani kuma ɓarawon Munàr E. Zogò da ita!”

Sarki Bar Hu Wanjam ya ɗan yi shuru yana kallon su, kafun ya dubi Kilarà ya ce, “Mece ce shaidar taku?”

Kilarà yayi taku uku gaban wannan sarki, ya tafa hannayensa sau uku. Take Majanun yaga wani akwatin haske ya bayyana akan iska.

Kilarà ya ɗan juyo da kansa ya dubi Majanun ya ce, “Ƙaraso nan!” Majanun ya ƙarasa.

Majanun yana zuwa ya baiwa Majanun umarnin ɗora hannunsa guda akan wannan akwatin haske.

Majanun ya ɗora hannunsa. Yanayin wannan mutumi wanda Majanun ya jiwo sa'adda s**a ɗauko Munàr E. Zogò ya fara fitowa daga cikin allon ruhin sa yana biyo jijiyoyin jikinsa.

A hankali ya ƙaraso cikin hannun Majanun sa'annan ya shige cikin wannan akwatin haske. Wata 'yar girgiza wannan akwati yayi, kafun ya tarwatse.

Siffar yarima Ra'alin ta bayyana a daidai wajen da akwatin ya tarwatse.

Wata babbar fasaha Kilarà yayi amfani da ita a yanzu wajen gano wannan mutumi. Fasahar ta juyar da yanayin wannan mutumi wanda Majanun ya ajiye a cikin allon ruhinsa izuwa siffofin ainihin mutumin.

Koda sarki Bar Hu Wanjam yaga wannan mutumi sai ya miƙe tsaye cikin tsananin mamaki.

“Luka?!” inji sarki Bar Hu Wanjam.

Al'amarin da ya baiwa su Majanun mamaki kenan. Wane ne kuma Luka?

Sarki Bar Hu Wanjam ya ƙaraso gaban mutum-mutumin ya ɗora hannun sa guda akansa.

Nan take mutum-mutumin ya juye daga hoto ya koma ainihin siffofin yarima Ra'alin. Kai kace ɗauko yarima Ra'alin aka yi, aka kawo shi wannan waje.

Majanun bai taɓa kallon yarima Ra'alin ba a rayuwar sa, saboda haka bai san wane ne shi ba.

“Wane ne wannan mutumi?” inji Majanun.

“Sunan sa Yarima Ra'alin ɗan uwan sarki Kam'alin na doron ƙasa ta takwas.” Bar Hu Wanjam ya amsa masa wannan tambaya a taƙaice.

“Ra'alin?” inji Majanun. “To, amma meyasa ka kira shi da suna Luka a ɗazu?”

Sarki Bar Hu Wanjam ya gyaɗa kai ya ce, “Shi Ra'alin ɗan wata ƙabila ce wacce ake kira Luka... Tana daga cikin ƙabilun da aka tsine musu tun a zamanin ɗan uwa Dahasàm.”

Nan take Bar Hu Wanjam ya kwashe labarin ƙabilar Luka k**ar yadda Tairiy ta karanta a ɗakin karatun sarki Amuru ya zayyane musu.

Al'amarin da ya baiwa su Majanun mamaki kenan saboda basu taɓa tsammanin hakan ba.

“Idan mutum yayi la'akari da abinda ya faru a shekarun baya. Tabbas makamin Munàr E. Zogò yana hannun Ra'alin. Saboda da makamin aka yi amfani wajen kashe ɗan uwansa.”

Majanun ya ce, “Saboda haka zamu ƙwato makamin a hannun sa kenan!”

Sarki Bar Hu Wanjam ya gyaɗa kai, “Eh amma sai bayan wani lokaci!”

“Na fahimta!” Majanun ya ce.

“Gimbiya Siyara Shauwat zata maye gurbin Sinarà Jani kuma ita ce, Salsa-3.”

Koda yake Majanun bai san gimbiya Siyara Shauwat ba, bai san mahaifinta ba. Amma ya san doron ƙasa ta biyu da hatsarin ta.

Hasalima doron ƙasa ta biyu da doron ƙasa ta farko ba'a kiransu doron ƙasashen ƙasa. Sai dai ace doron ƙasashen sama. Ba don komai ba sai domin ɗaukakar da mutanen dake rayuwa a cikinsu s**a samu.

Majanun ya ce, “Ta ya ya zan mayar da Siyara Shauwat salsa ɗina, ba tare da na fuskanci matsala daga wajen mahaifinta ba da al'ummar doron ƙasa ta biyu ba?”

Sarki Bar Hu Wanjam ya ce, “Saura sa'a guda kacal a fara gwabza wani azababben yaƙi.

“Wannan yaƙi zai shafi gaba ɗaya doron ƙasashe tara. Akwai yiwuwar al'ummar doron ƙasashen sama da kansu su saka hannu.

“Idan kuwa zasu saka hannu, sarki Takuruku mahaifin gimbiya Siyara Shauwat yana gaba-gaba. Saboda an ci mutuncin 'yar sa watannin baya.

“Za kuyi amfani da wannan dama wajen kutsawa birnin Mahajó. Idan dai, Siyara Shauwat tayi arba da Sabon Farin Watan dake kan goshinka. Zance ya ƙare. Dolenta zata yi maka biyayya saboda ruhinta ne zai yi hakan.”

Majanun yana jin wannan batu ya gyaɗa kai cikin fahimta. Matsala ta farko an shawo kanta.

Saura matsala ta biyu da ta uku.

Majanun ya ce, "Wane ne salsa na biyu kuwa?"

Sarki Bar Hu Wanjam yayi murmushi tamkar wanda yake jin daɗin yadda Majanun ya fahimci abinda yake nufi, ba tare da tambayoyi ba.

Sarki Bar Hu Wanjam ya sake nuna wannan allon gilashi da hannunsa guda. Nan take hoton gimbiya Siyara Shauwat dake jikin allon ya disashe.

Hoton wani ƙaramin yaro wanda ba zai wuce shekaru goma sha-shida ba ya maye gurbin sa.

Majanun ya zaro idanunsa ya ƙurawa wannan yaro idanu. Yana ta ƙoƙarin tuno inda ya san wannan yaro.

Bayan ɗan dogon lokaci yana ta tunani gami da nazari, sai fuskar wannan yaro ta faɗo masa.

Sai da Majanun ya sake bude idanunsa cikin mamaki. A waje guda ya taɓa kallon wannan yaro.

Wajen da s**a je ɗaukar makamin takobin Saif-al-Ƙamr, kogon Danishin na ƙabilar H'Ƙamru kenan.

Majanun ya ɗauke idanunsa daga kan wannan allon gilashi sannan ya dubi mahaifinsa ya ce.

"Wane ne wannan yaro?

"Ta ya ya alaƙa zata shiga tsakanina dashi, alhali ni ne wanda ya kashe masa mahaifinsa?

"Shin akwai wani abu na musamman a tattare da wannan yaro ne?"

Koda sarki Bar Hu Wanjam ya ji waɗannan tambayoyi sai yayi guntun murmushi.

Ba tare ya ce komai ba, ya sake nuna wannan allon gilashi da hannun sa guda.

Nan take hoton wannan yaro ya disashe. Wani faifan bidiyo ya fara gudana akan wannan allon gilashi.

Wannan yaro aka nuno a gaban ɗaruruwan jama'ar su yana yi musu wani jawabi.

Majanun, Kilara, Tchai da Sairana s**a nutsu suna sauraren abinda wannan yaro yake cewa.

"Ya bayyana," abinda kunnuwan su Majanun s**a fara jiyo musu kenan.

"Mutumin da ke ɗauke da miyurar abar bauta Rekaza, Luru da Zogosh ya bayyana.

"Koda zamu shekara arba'in muna yaƙi da wannan mutumi, ba zamu taɓa samun nasara akansa ba.

"Wannan shi ne dalilin da ya sa na dakatar da ku daga afka masa da yaƙi.

"Bari na taƙaice muku bayani, wannan mutumi shi ne Yarima Na Musamman.

"Magajin Duniya Ta Musamman - maɗaukakiyar duniya inda ababen bautar mu suke!"

Lokacin da wannan yaro yazo nan a zancen sa sai wani mutum daga cikin mutanensu ya dube shi ya ce.

"Ta ya ya aka yi ka gano waɗannan manyan sirruka waɗanda mahaifinka da kansa bai gano su ba, dukda cewa ya fafata yaƙi da wannan saurayi?"

Yaron yana jin wannan tambaya ya dubi mutumin cikin nutsuwa ya ce, "Mahaifina ya faɗa min cewa, a duk lokacin da takobin Saif-al-Ƙamr ta shiga hannun wanda ya dace. Miyurar Rekza, Luru da Zogosh zata bayyana a goshin sa."

Wannan mutumi yana jin wannan batu, jikinsa yayi sanyi ya samu gamsuwa a ransa bisa jin wannan amsa.

Kusan mutanen ƙabilar H'Ƙamru gaba ɗayan su sun kalli miyurar dake goshin Majanun sa'adda zai yaƙe su da takobin Saif-al-Ƙamr.

Abu na ƙarshe da su Majanun s**a gani a wannan faifan bidiyo shi ne, wannan yaron yana tabbatarwa mutanen sa cewa, zasu yiwa Majanun biyayya kuma zasu nemo shi a duk inda yake domin kuwa ya kasance Na Musamman daga wajen ababen bautar su.

Lokacin da wannan faifan bidiyo yazo wannan waje sai sarki Bar Hu Wanjam ya sake nuna wannan mudubin gilashi da hannunsa guda.

Faifan bidiyon na ɗaukewa, hankalin su Majanun ya koma kan Bar Hu Wanjam suna jiran ƙarin bayani akan abinda s**a gani a wannan faifan bidiyo.

Sarki Bar Hu Wanjam yayi ajiyar zuciya ya fara bayani.

"Sunan wannan yaro sunansa Selenos.

"Ya kasance na musamman kuma ɗan ƙabilar H'Ƙamru.

"Alaƙar dake tsakanin ka dashi ita ce, Sabon Farin Wata Wata.

"Kaine babban hadimi kuma mutum na musamman wanda Rekza, Luru da Zogosh s**a san da zamansa.

"Selenos da mutanensa ba su da abun bauta wanda ya wuce waɗannan sunaye guda uku da na amabata.

"Kaga dole zasu yiwa mutumin da yazo na musamman daga wajen ababen bautar su biyayya.

"Wannan shi ne alaƙar dake tsakanin ka da shi.

"Abu na musamman dake tattare da Selenos shi ne, shi ne kaɗai mahaluƙin da zai iya sarrafa makamin Azmir."

Lokacin da sarki Bar Hu Wanjam yazo nan a zancensa sai yayi shuru, ya baiwa Majanun damar yin tunani.

Daga cikin wannan abubuwa da s**a tattauna, Majanun ya tsinto tarin tambayoyi waɗanda yake buƙatar a amsa masa kuma idan da hali ayi masa ƙarin bayani.

Majanun ya dubi sarkin ya ce, "Mene ne Rekza, Luru da Zogosh? Ban taɓa jin waɗannan sunaye ba, sai fa yanzu da nazo wajenka.

"Ina son cikakken bayani akan waɗannan sunaye waɗanda kace na zamo hadimi kuma mutum na musamman daga wajen su.

"Abu na biyu, ina son sanin wanne makami ne Azmir wanda kace iya Selenos ne zai sarrafa shi?

"Abu na uku, ka faɗa min yadda zan mayar da Siyara Shauwat ɗaya daga cikin salsa ɗina.

"Amma baka faɗa min yadda zan mayar da Selenos ba."

Sarki Bar Hu Wanjam yana jin waɗannan tambayoyi, ya ja dogon numfashi,

"Amsar tambaya ta farko, amsa ce mai tsaho. Aƙalla zata iya ɗaukar mu tsahon sa'a uku kafun na gama amsa maka wannan tambaya.

"Bayani akan Rekza, Luru da Zogosh bayani mai tsaho.

"Idan nace zan yi maka bayaninsu hakan zai ɗauke mu dogon lokaci wanda zai iya janyo a kammala wannan yaƙi.

"Mu kuma muna so ana tsaka da fafata wannan yaƙi, kuje doron ƙasa ta biyu ku ɗauko Salsa ta uku.

"Saboda haka zan amsa maka wannan tambaya amma sai gaba. Ka tuna min idan na manta."

Majanun yana jin abinda sarkin ya gyaɗa kai cikin fahimta.

Saura sa'a guda jal a fara gwabza azababben yaƙi wanda zai shafi gaba ɗaya doron ƙasashe tara.

Su Majanun zasu yi amfani da wannan dama wajen zuwa doron ƙasa ta biyu, su ɗauko Siyara Shauwat.

Wannan ita ce kaɗai damar su, saboda indai ba wannan yaƙi ake gwabzawa ba. Shiga doron ƙasa ta biyu su ɗauko gimbiya guda, ba ƙaramin aiki bane.

"Shi kuwa makami Azmir," Bar Hu Wanjam ya ci gaba da bayani. "Wasu tagwayen takubba ne guda biyu. Guda ana ce masa Az, guda kuwa Mir. Idan ka haɗa su zasu baka Azmir.

"Az - Wata takobi ce mai bala'in kaifi, hasalima tun lokacin da aka ƙirƙiro ance babu abinda ya gagareta yankawa. Walau dutse, ƙarfe ko itace. Duk abinda aka sara da wannan takobi saiya tsarge gida biyu.

"Mir kuwa- Wata siririyar takobi ce mai bala'in tsini. Duk abinda aka cakawa wannan takobi sai ya ɓule koda kuwa menene.

"Idan Selenos ya mallaki waɗannan takubba guda biyu zai sarrafa su tamkar yadda zai sarrafa jikin sa."

Lokacin da Bar Hu Wanjam yazo nan a zancensa sai ya duba wani agogon gilashi dake hannun sa.

Yanayin fuskar sa ya sauya ya ɗago kansa ya dubi Kilara, Tchai da Sairana ya ce.

"Lokaci yana neman ƙurewa. Ku je birnin Mahajo ku ɗauko Shauwat."

Sarkin ya dubi Majanun ya ce, "Idan kuka dawo zamuci gaba da tattaunawa!"

Da wannan s**a tsayar da wannan tattaunawa ta musamman, akan yarjejeniyar idan s**a dawo tare da Siyara Shauwat 'yar sarki Takuruku zasu ci gaba da tattaunawa.

*****

THANKS 4 READING.

Address

Sangaru Street
Gombe

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Ruhin Jarumtaka littafin yaki posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Ruhin Jarumtaka littafin yaki:

Share

Category