Ruhin Jarumtaka littafin yaki

Ruhin Jarumtaka littafin yaki Gawurtattun littatafan Hausa novel masu dogon zango daga Umar Muhammad da Zahra A. Adamu
(3)

RAMIN MUGUNTA!*  MUGUWAR GASA!*Babi na 81: *Kogon Ƙarƙashin Ƙasa**  *Wannan littafin sadaukarwa ne ga Fatima Umar Muhamm...
05/07/2025

RAMIN MUGUNTA!

*

MUGUWAR GASA!

*

Babi na 81: *Kogon Ƙarƙashin Ƙasa*

*

*Wannan littafin sadaukarwa ne ga Fatima Umar Muhammad*

*

Marubucin ✍️RUHIN JARUMTAKA ✍️
*

✍️✍️✍️ Marubucin littafin: Muhammad Umar Sangaru ✍️✍️✍️
*
*

~Birnin sarauni Milisa.
~Daular Ubbaniya.

*

“Ka kashe ma'aboci Otakí, ka samu kyautar sinadari har guda ashirin da biyar.” saƙon da ya shiga cikin allon ruhin Arshan kenan.

A wannan lokaci ya buɗe idanunsa, bayan yayi doguwar ajiyar numfashi da mamakin abubuwan da s**a faru sai ya miƙe zaune.

Arshan yayi arba da sarauniya Milisa durƙushe akan gwiwowinta tana ta haki. A gefe guda kuwa, Zonar ce a kwance cikin mawuyacin hali. Leɓɓan bakinta gaba ɗaya sun bushe saboda tsabagen ƙishirwa.

A guje Arshan ya laluɓo battar ruwansa ya ruga ya bata a baki tasha. Bayan ta kurɓa k**ar sau huɗu sai ta buɗe idanunta.

Koda taga Arshan a raye kuma cikin koshin lafiya sai ta cika da tsananin farin ciki.

Arshan na ganin gimbiya Zonar ta farfaɗo ya ruga da gudu zuwa wajen da masoyiyarsa gimbiya Dani ke kwance.

Yana zuwa ya tarar da ita cikin mummunan hali. Numfashinta na fita da ɗai-ɗai. Ranta yana da daf da fita.

A ɗimauce Arshan ya fiddo wani maganin barci mai ƙarfin gaske ya bata tasha. Tana shan wannan magani, barci mai nauyi yayi awun gaba da ita.

Arshan ya sa hannunsa ya zare wannan wuƙa dake cake a kafaɗarta. Koda yaga zurfin raunin da wannan wuƙa tayi mata sai hankalinsa yayi mummunan tashi.

Cikin gaggawa Arshan ya sake fiddo kayan aiki ya gyara mata wannan rauni.

A wannan lokaci sarauniya Milisa ta miƙe tsaye daga wannan waje da take durƙushe. Idanunta cike sharkaf da hawaye saboda tsananin tausayin mutanen ta da ta rasa sak**akon wannan hari.

Ba tare da ɓata lokacin komai ba, Arshan ya goya Dani a gadon bayan sa. Gimbiya Zonar ta taso tazo gaban sa tana dudduba gimbiya Dani.

Kasancewar tana cikin halin barci, k**anninta basa sauyawa. Kamannin gimbiya Dani, Zonar take gani a wannan lokaci.

To, amma tana jin ƙamshin wani babban sihiri yana tashi a jikin ta. Alhali ita kuwa gimbiya Dani bata kasance matsafiya ko mai ƙarfin sihiri ba.

“Wai har yanzu kwakwanto k**e akan ba ainihin masoyiyata bace?” Arshan ya yiwa gimbiya Zonar wannan tambaya.

Cikin gaggawa Zonar ta girgiza kanta, “Ko kaɗan!”

A zahiri ta nuna masa ta gamsu gimbiya Dani ce amma a zuciyarta ta ƙudurce zatayi gagarumin bincike akan wannan matsafiya kuma zata ɗauki matakin da ya dace akanta.

A wannan lokaci sarauniya Milisa ta ƙaraso gaban su. Fuskarta cike da jimami da alhini.

Tuni a wannan lokaci dakarun ƙasarta sun zo sun fara tono gawarwakin da wannan gini da ya rushe ya kashe.

Wani ƙasaitaccen keken doki yazo gabansu ya tsaya. Milisa ta sakarwa Arshan murmushin ƙarfin hali ta ce, “Mu tafi gida!”

Ba tare da gardamar komai ba, Arshan da gimbiya Zonar s**a shiga cikin wannan keken doki sa'annan s**a ci gaba da tafiya.

Saboda ganin wannan hali da sarauniya Milisa ta shiga yasa Arshan da gimbiya Zonar s**a ja bakinsu s**a yi shuru basu sake cewa komai ba.

Bayan dogon lokaci wannan keken doki ya ƙaraso cikin gidan sarautar sarauniya Milisa.

Sarauniya Milisa tana sauƙa daga cikin wannan keken doki ta bayar da umarnin akai Arshan da gimbiya Zonar masauƙinsu kuma a kirawo babban likita wanda zaizo ya sake duba lafiyar su.

Matuƙin keken dokin ya risina cikin biyayya sa'annan ya wuce tare da su Arshan.

Kai-tsaye sarauniya Milisa ta wuce zuwa fadarta. Tana zuwa ta zauna akan karagar mulki sannan ta tura aka kirawo dukkan sarakunan dake ƙarƙashin mulkin ta.

Bayan k**ar sa'a biyu, sarakunan s**a gama hallara.

Bayan sun gama yiwa sarauniya jalje bisa wannan mummunan abu da ya faru sai sarauniya Milisa ta dube su ta ce.

“Zan shigar da ƙorafi akan wannan abu da ya faru. Zan so sarauniya Jazwirà ta tsananta bincike kuma ta ɗauki tsatstsauran mataki akan waɗanda keda alhakin wannan hari.

“Shin a cikin ku akwai wanda ya ga farkon abin ko kuma yaji labari daga waje mai ƙarfi?”

A cikin wannan tattaunawa ce, sarakunan dake ƙarƙashin mulkin sarauniya Milisa s**a bata labarin shigowar mutane guda biyu daga sama.

Guda daga cikinsu shi ne, Jeziy'Kaubar guda kuwa basu san inda yai ba.

Sarauniya Milisa sai ta yiwa wannan al'amari wawan fahimta. A ganinta Jeziy'Kaubar ya biyo masoyiyar Arshan ce tunda sun tarar dashi ya caka mata wuƙa (a ganinta).

Saboda haka sarauniya Milisa ta ɗauki alhakin wannan hari gaba ɗaya ta ɗaura shi akan Jeziy'Kaubar kuma ta rubuta wasiƙa tare sa-hannu ta aikawa haɗaɗɗiyar daular ƙarƙashin ƙasa ta sarauniya Jazwirà.

Sarauniya Milisa ta buƙaci a bi mata haƙƙin mutanenta waɗanda rayukansu s**a salwanta a cikin wannan hari.

A ɓangaren Arshan, Kotegà da gimbiya Zonar kuwa. Tuni an sauƙe su a cikin wannan ƙasaitaccen gida nasu.

Arshan ya shiga cikin wannan gida da sauri kuma ya kwantar da masoyiyarsa akan gado.

Bayan ɗan lokaci, wani babban likita ya shigo cikin wannan ɗaki. Take ya tambayi Arshan dukkan abinda ya faru. Arshan ya kwashe labarin komai ya zayyane masa.

Likitan yai amfani da iliminsa na likitanci ya duba wannan rauni dake kan kafaɗar gimbiya Dani. Take ya dubi Arshan ya ce, “Wannan rauni ba ainihin raunin makami bane.”

Gimbiya Zonar wadda ke kwance akan wani gado dake gefe guda ta ɗan zaro idanu cikin mamaki.

Shi kuwa Arshan haɗe gira yayi, shi da kansa ya zare wannan wuƙa dake cake a kafaɗar Dani.

Ta ya ya za'a ce masa ba ainihin raunin makami bane?

“Idan ba raunin makami bane, to, raunin mene ne, likita?” Arshan ya tambaya.

Likitan ya ɗago kansa ya dubi Arshan cikin nutsuwa sa'annan ya fara yi masa bayani.

“Idan ka lura raunin yayi zurfi da yawa. Inda ace na ainihin wuƙa ce da tuni ya iso ƙashin kafaɗarta...”

Duk wannan maganganu s**a shiga kunnen wannan Kotegà daki-daki. Tuni a wannan lokaci hankalinta ya fara tashi saboda wannan likita yana ƙoƙarin tona mata asiri a wajen Arshan.

Cikin gaggawa ta fara tunanin hanyar da zatai amfani da ita wajen dakatar da wannan likita daga ci gaba da magana.

Sai dai a lokacin Arshan yayi magana. “Kaga likita, ba kiran aka yi domin kayi mini bayanin mene ne ya haddasa wannan rauni ba. An kira ka ne domin ka duba raunin kuma kayi masa aikin da ya dace.

“Saboda haka kayi abinda aka umarce ka kawai. Bincike ko ainihin wannan rauni duk ba naka bane!”

Likitan yana jin wannan batu ya ɗan risina cikin biyayya. Ba tare da gardamar komai ba, ya yiwa Dani aikin da ya dace.

A zuciyar Kotegà ta cika da tsananin farin ciki bisa ganin wannan abu da ya faru.

Likitan yana gama gyara raunin Dani ya koma kan gimbiya Zonar itama ya gyara raunikan dake wuyanta.

Bayan ya kammala ya fiddo kwalaben magunguna ya baiwa Arshan sa'annan s**a yi sallama da juna ya tafi.

Itama gimbiya Zonar gado aka bata, saboda an saka waɗansu itatuwa an gyara raunin dake wuyanta.

Arshan ya ci gaba da kula da waɗannan 'yan mata guda biyu har tsahon kwanaki uku.

A wannan lokaci raunin dake kafaɗar gimbiya Dani ya warke sumul tamkar bata taɓa jin rauni a wajen ba.

Al'amarin da ya baiwa Arshan mamaki kenan, kwanaki uku sun yi kaɗan wajen warkewar raunin.

Lamarin da yasa ya zauna ya ƙurawa gimbiya Dani idanu kenan, yana ta tunani.

Babu abinda yake faɗowa kansa a wannan lokaci sai irin k**annin da ya taɓa gani a jikin gimbiya Dani sa'adda ya shiga gidan sarautar sarki Mazurus ta cikin wannan tafkin wanka. Wato lokacin da Dani ta kira shi da matsoraci kuma har ta ƙalubalance shi akan yazo gaban mahaifinta yace yana sonta.

A wancan lokaci fatar jikin gimbiya Dani fara ce tas tamkar idan aka taɓa ta jini zai zubo. Gashin kanta ya kasance baƙi wuluƙ kuma ya zubo har gadon bayanta.

Waɗannan siffofi guda biyu su Arshan yafi tunowa. To, amma wannan wadda take kwance a gabansa, fatarta ta ɗan yi duhu. Kuma gashin kanta bai yi wani tsaho na azo a gani ba.

A wannan lokaci abubuwan da gimbiya Zonar ta faɗa masa s**a faɗo kansa. Zonar cewa take, ita matsafiya take gani ba Dani ba.

Arshan yayi bincike akan dalilin da yasa aka makantar da gimbiya Zonar a shekarun baya. Kuma ya gano cewa, idanun gimbiya Zonar na musamman ne shiyasa aka yi mata tuggu ta makance.

To, amma a wannan karon gimbiya Zonar bata ce komai ba akan Dani ba. Shin hakan yana nufin asalin Dani ce?

Arshan na cikin waɗannan tunane-tunane nasa, aka turo hadimi daga fadar sarauniya Milisa ana yi masa sallama.

Ajiyar zuciya kawai Arshan yayi ya miƙe tsaye yaje kan gimbiya Dani ya sumbaci goshinta.

Wani ƙarfin iko da ya taso daga jikinta ya doki hancinsa ne ya baiwa Arshan mamaki kuma ya ja da baya a tsorace.

A daidai wannan lokaci taurarin dake kewaye juna a jikin miyurarsa s**a tsaya cak!

Ɗaya daga cikin taurarin ya disashe daga jikin wannan miyura sannan ya bayyana a cikin idon Arshan na hagu.

Wato a wannan lokaci idanun Arshan gaba ɗaya sun koma na taurari kenan.

To, a ɓangaren Arshan kuwa, wani abu yake kallo cikin tsananin mamaki da al'ajabi. Waɗannan idanu nasa na musamman ne.

Wasu taurari guda bakwai Arshan ya gani suna kewaye kan gimbiya Dani. Tartsatsin da waɗannan taurari suke yi ne ya kashewa Arshan idanu.

Wani ilimi ya fara shiga kan Arshan. Ilimin karantar Taurari.

Ganin waɗannan taurari suna ta haske yana nufin akwai sa'a da nasara a tattare da gimbiya Dani kenan.

Arshan ya juya ya kalli gimbiya Zonar. Take yaga irin wadannan taurari guda shida suna ta kewaye kanta. Saɓanin na gimbiya Dani na gimbiya Zonar duhu ne dasu.

Arshan yana murnar ya samu babbar fasaha ta karantar Taurari amma a lokacin tauraron da ya bayyana a cikin idanunsa na hagun ya ɓace ɓat!

Tauraron ya koma cikin miyurarsa sa'annan s**a ci gaba da kewaye juna.

Arshan ya ja dogon numfashi sai a wannan lokaci ya tuno da cewa, ana fa jiransa a fada. Saboda haka cikin gaggawa ya fice daga cikin wannan ɗaki.

Fitar Arshan keda wuya, idanun gimbiya Dani s**a buɗe. Take ta miƙe tsaye ta tunkaro gimbiya Zonar wacce ke kwance tana ta barci sak**akon maganin da ta sha.

Kafun ta riski Zonar ta juye izuwa siffar Kotegà.

Tana zuwa kan gimbiya Zonar ta haɗe hannayenta biyu a waje ta saita daidai idanun gimbiya Zonar.

Wani baƙin haske ya fito daga cikin hannayenta kuma ya shige cikin idanun Zonar a guje Kotegà ta koma kan gadonta ta kwanta kuma ta sake juyewa zuwa k**annin gimbiya Dani.

***

Arshan na fuskanto fadar sarauniya Milisa ya hango wata gawurtacciyar sarauniya zaune akan karagar mulki ta musamman. Milisa tana zaune a gefenta cikin tsananin biyayya.

Arshan na ƙarasowa fadar, wannan sarauniya ta tashi da kanta ta tarɓe shi cikin girmamawa.

Lamarin da ya baiwa Milisa mamaki kenan.

Sai dai Arshan baya iya shaida k**annin wannan sarauniya. Saboda manyan tufafi ta saka waɗanda s**a rufe jikinta gaba ɗaya.

Ta rufe rabin fuskar ta da wani kyakkyawan ƙyalle wanda dukda cewa shara-shara ne amma baka ganin fuskar ta ta.

Ta saka wata hular Fulani akanta wadda ta sauƙo har kan goshinta.

“Suna na Sarauniya Jazwirà. Kada ka tambaye ni fuskata saboda babu wanda ya taɓa ganinta a duk faɗin duniya sai 'yan ƙalilan.

“Nazo ne domin na sanar da kai yadda zaka yi amfani da wannan taswira domin samun nasarar ɗauko Fursunan Littafi!”

Arshan yana jin muryar wannan sarauniya ya fara karkarwa. Ba don komai ba sai domin yadda muryar take k**a da muryar Lasirina Ajamen. To, amma bata kai muryar Lasirina Ajamen zurfi, izza da ƙarfin iko ba.

“Saboda wanne dalili k**e ɓoye fuskar ki a matsayin ki na sarauniya guda?” inji Arshan.

Arshan ya ga ta haɗe kyawawan girarta ta ce, “Nace maka bana so, ka tambaye ni fuskata amma sai da ka tambaya, ko?”

Arshan ya ɗan ja numfashi ya ƙura mata idanu kawai. Kai da gani ka san ya fara gajiya da yadda ake wasa da hankalinsa wajen ɓoye masa abubuwa.

“Muje mu zauna!” inji sarauniya Jazwirà.

Babu musu Arshan ya bi bayanta s**a zauna akan karagar mulkin nan. Milisa ta matso kusa gaban wani ƙaramin teburi dake gaban wannan karaga.

Arshan ya zaro wannan taswira ya shimfiɗa ta akan wannan ƙaramin teburi.

“Babban dalilin da yasa muka kawo wannan Littafi daular ki shi ne saboda kema za ki bayar da gudunmawar ki wajen ɗauko littafin.” sarauniya Jazwirà ta fara yi musu bayani.

“Wannan taswira zata fara aiki ne a cikin wani babban daji wanda ake kira da suna: Céns.

“Wata doguwar tafiya ce ta kusan kwana arba'in akan wata masifaffiyar hanya mai ɗauke da tarin hatsari. Ba abun mamaki bane ku rasa rayukan ku a cikin wannan tafiya, to, amma dole zakuyi ta.”

Sa'adda Jazwirà tazo nan a zancenta sai ta fara nunawa su Arshan abubuwan dake jikin wannan taswira. Abubuwa guda biyu ta nuna musu. Abu na farko, farkon dajin Céns. Abu na biyu, wannan doguwar hanya wadda aƙalla za'a shafe kwanaki arba'in akanta.

Hannun sarauniya Jazwirà yazo kan sashe na ƙarshe na wannan taswira. Akwai zane-zane da tsare-tsare da tarin bayanai a wannan sashe.

“Lokacin da kuka iso wannan waje, kun iso wajen da wannan littafi yake.” sarauniya Jazwirà ta dubi Arshan cikin nutsuwa. “Ka nutsu ka saurare ni da kyau da kunnuwan basira!”

Sarauniya Jazwirà ta nuna wani murfi tamkar murfin rijiya. To, amma anyi masa fasali da waɗansu zanen kibiyoyi guda uku waɗanda suke kallon gabas.

“Za ka juya murfin wannan rijiya sau uku ta ɓangaren gabas!
“Idan kayi haka ka buɗe ƙofar shiga wannan kogo kenan!
“Kayi sani cewa, a cikin wani ƙatoton kogo da aka gina a ƙarƙashin ƙasa zaku tsinci kan ku.”

Sarauniya Jazwirà tasa yatsan hannunta guda ta taɓa jikin wannan murfi. Take yayi haske kuma ya buɗe kansa.

Arshan da Milisa s**a ga wani ƙatoton kogo ya bayyana. Babu komai a cikin wannan kogo sai tarin mayaƙa sunyi shiga ta yaƙi.

A gabansu ne aka nuno wasu ƙofofi guda uku. Guda tana da launin shuɗi. Guda fari. Ta ƙarshen kuwa, baka ƙirim.

“Babu ruwanku da waɗannan mutum-mutumi. Arshan kai zaka ɗiga jininka a jikin wannan ƙofa mai launin baƙi. Da zarar kayi hakan zata buɗe. Tana buɗewa zaka tsinci kanka a cikin kurkukun litattafai.

“Idan kayi kuskuren ɗiga jini a ƙofar da ba wannan baƙa ba. Waɗannan mutum-mutumi zasu dawo rayayyu kuma su afka muku da azababben yaƙi.

“A cikin wannan kurkuku ta littatafa zaka sake ɗiga jininka akan akwati ta 110. Idan kayi kuskure a wannan waje ma. Fursunan Littafi dake cikin akwati ta 110 zai narke. Saboda haka ka kula sosai.

“Na rantse har da darajar Dahasàm. Jinin ka ne kaɗai zai buɗe waɗannan ƙofofi. Koda mutum ya samu nasarar shiga cikin wannan kogo ba zai iya zuwa inda wannan littafi yake ba. Dole sai da taimakon ka.”

Sarauniya Jazwirà tana zuwa nan a zancenta ta ɗago kanta ta dubi Arshan da sarauniya Milisa ta ce, “Ina yi muku fatan alheri da samun nasara!!”

****

Yau *05/07/2025*
Babi na gaba zai zo *07/07/2025* In Sha Allah.

RAMIN MUGUNTA!*  MUGUWAR GASA!*Babi na 80: *Erengalós**  *Wannan littafin sadaukarwa ne ga Fatima Umar Muhammad**  Marub...
30/06/2025

RAMIN MUGUNTA!

*

MUGUWAR GASA!

*

Babi na 80: *Erengalós*

*

*Wannan littafin sadaukarwa ne ga Fatima Umar Muhammad*

*

Marubucin ✍️RUHIN JARUMTAKA ✍️
*

✍️✍️✍️Dr. Umar Muhammad ✍️✍️✍️
*
*
***

~Yaren Dahamísh.

**
Akwai wani tsohon yaren da ake amfani dashi a wancan zamani wanda ake magana da sadarwa dashi tun kafun Amjusàn. Ana kiran wannan yare da suna Dahamish.

Yaren Dahamish shi ne, babban yaren da al'umma suke amfani dashi kafun zuwa mutanen ƙabilar Jorash. Bayan zuwan ƙabilar Jorash s**a kawo sabon yare k**ar yadda s**a kawo sabon addini da tsarin mulki.

Ya zamana cewa, yaren Dahamísh yana ɓacewa a hankali a hankali. Kafun kace me wannan tuni an fara mantawa dashi. Amma dukda haka akwai sunaye, mak**an yaƙi da waɗansu kalmomi da suke da alaƙa da wannan yare waɗanda ake samu ɗaya biyu haka.

Misali k**ar Munàr, Zogó, Sikaí, Silmà, Egí, Siwin, Bozó da dai sauran waɗanda zasu iya bayyana a gaba.

Kalmar 'Erengalós' kalma ce wadda sai asalin tsohon mutum zai santa. Irin mutanen nan da s**a rayu kimanin shekaru ɗari biyar baya.

Kalmar tana ɗaukar ma'ana guda biyu. Suna da aiki.

Idan ka ɗauke ta a matsayin 'suna' kuma ka fassara ta zuwa yaren Jorash wanda al'umma suke amfani dashi. Sunan zai baka sunan wani mutum daga cikin wasu mutane waɗanda aka fi tsana a duniya. Erengalós Ijunú.

Sunan ƙabilar waɗannan mutane, Ijunú. Tuni an shafe ta daga doron ƙasashe tara kimanin shekaru ɗari huɗu baya. Saboda an tsane su fiye da yadda aka tsani mutuwa. A wancan lokaci a duk lokacin da aka kira kalmar 'Ijunú' zaka ji wani ya amsa da kalmar tsinuwa.

Idan ka fassara kalmar a matsayin 'aiki' kuwa, zata baka sadaukarwa. Wato k**ar sadaukarwar da wani abu ko kuma wani ruhi ko jini ko sassan jikin mutum. Erengalóssa - sadaukarwa da...

***
~Dajin Erénhul.
~Duniyar Júsaiƙ.
***

To, a cikin wani baƙin daji kuwa dake cikin wata duniya wadda ake kira Júsaiƙ, waɗansu mutane guda biyu ne keta tafiya.

Komai da komai dake cikin wannan duniya ya saɓa da abinda idanu s**a saba kallo.

Abu na farko sararin samaniyar wannan duniya da ƙasar da ake takawa duk iri ɗaya ne.

Koda yake akwai wani kakkauran hadari wanda ya maye gurbin ƙasar da ake takawa.

Waɗansu irin bishiyoyi ne manya-manya s**a cika wannan daji. Saboda tsabagen tsahon su sun kusa tokarewa da sararin samaniya. Ganyayyakin bishiyoyin sai rangaji suke k**ar zasu kaiwa mutun duka.

Waɗansu irin dabbobin daji baƙaƙe ƙirim sun cika wannan daji, sai kaiwa da komowa suke suna farautar abinda zasu ci.

Waɗannan mutane guda biyu kuwa, guda daga cikinsu yana kan gaba. Ya yin da guda kuwa yake baya.

Wanda yake tsaye a bayan ya kasance zabgegen ƙato kuma dogo na kwatance. Kasancewar ya rufe fuskar sa da baƙar hula yasa ba zaka gano wane ne ba.

Ita kuwa wadda take tsaye a gaban kallon farko zakai mata tunanin doron ƙasa ta uku ya faɗo maka. Gimbiya Caiyàn ce wadda sarki Mazurus Asaryan ya baiwa Kalmaru umarnin sato masa.

Tuni an gusar da hankalin gimbiya Caiyàn, tafiya kawai take a cikin wannan duniya cikin umarni ga wani babban ƙarfin iko.

Yayin da s**a shafe sa'a goma sha-uku suna tafiya a cikin wannan ƙatoton daji, sai s**a iso cikin wani ƙatoton fili gaban wani gabjejen mutum-mutumi.

Wani ɗan ƙaramin kogi ya kewaye wannan mutum-mutumi a tsakiya. Mutum-mutumin yayi tsayuwa ta musamman. Yana sanye da doguwar alkyabba wadda ta sauƙo har cikin ruwan wannan kogi. Akansa akwai kambu na mulki wanda yake ɗaukar idanu tun daga can nesa.

Gimbiya Caiyàn ta ƙarasa cikin wannan kogi tazo gaban wannan mutum-mutumi ta tsaya.

A hankali ta durƙusa akan gwiwowinta, sannan ta sunkuyar da kanta ƙasa.

Wannan mutumi wanda yake tsaye a bayanta yasa hannunsa ya fidda wannan baƙar hula da ta rufe masa fuska.

Nan take fuskar sa ta bayyana. Ba wani bane illa sarki Mazurus Asaryan mahaifin gimbiya Dani.

To, amma wannan sarki Mazurus ɗin yana da matuƙar bambanci da ainihin Mazurus wanda ake gani a cikin doron ƙasa ta huɗu.

Abu na farko da ya bambanta su, kwayar idanun sarki Mazurus ɗinnan sun kasance 'yan siraru k**ar na maciji. Akwai wani ƙarfin iko da tsohon buri dake tasowa daga cikin su.

Abu na biyu, akwai zanen Dauwamammiyar Miyura akan goshinsa. Kamar irin miyurar su Arshan da su Sauraban. Miyurar tana ɗauke da zanen irin wannan mutum-mutumi dake tsaye a gaban sa.

Bayan wannan, 'yan yatsun hannunsa guda shida-shida ne maimakon biyar-biyar k**ar na kowa.

Waɗannan abubuwa dake tattare da wannan Mazurus ɗin su ne s**a bambanta shi da wanda aka saba gani a cikin doron ƙasa ta huɗu.

To, amma idan kayi la'akari da yanayin fuskar sa, abinda yake ƙoƙarin aikatawa da kuma ganinsa tare da gimbiya Caiyàn zai tabbatar maka da cewa, lallai sarki Mazurus ɗin ne ba wani ba.

Sai dai kawai zaka iya cewa, shigowar sa cikin wannan duniya ce ta sauya masa k**anni ko kuma waɗannan su ne ainihin k**annin sa.

To, abin tambayar mece ce wannan duniya?

Wannan mutum-mutumi dake tsaye a gaban su, wane ne shi?

“Tú Erengalós lí (Ni Erengalós).

“Hó màs Erengalóssa hi ram sklí (Na sadaukar da) - Tihúr Jairab Caiyàn alanà (tsarkakken jinin iYàn) fú hasó raíj dakirin (da hauni na) Tur Jadadà ahassà bä! (domin na samar da fasahar Erénur)!”

Sarki Mazurus yayi magana a cikin wannan yare wanda ake kira Dahamísh. Yana gama faɗin haka wannan mutum-mutumi ya sunkuyo da kansa ƙasa.

Wani ruwa mai launin ɗorawa ya fara zubowa daga cikin bakin mutum-mutumin yana kwarara a gaban gimbiya Caiyàn.

Sarki Mazurus ya zaro wata wuƙa mai ɗauke da rubutun ɗalasimai ya tunkari gimbiya Caiyàn.

Yana zuwa gaban Caiyàn ya kwantar da ita ta fuskanci wannan mutum-mutumi. Mazurus ya ɗaura wannan wuƙa akan wuyanta sannan ya ɗaga kansa ya kalli idanun wannan mutum-mutumi. Nan take yayi karatun yanka a cikin wannan yare.

Sarki Mazurus ya yiwa gimbiya Caiyàn yankan rago. Jininta ya fara kwarara yana haɗewa da wannan ruwa mai launin ɗorawa dake zubowa daga bakin wannan mutum-mutumi.

Kafun cikar daƙiƙa goma tuni gimbiya Caiyàn ta mutu. To, amma inda ace zaka matso kusa kuma kaga abinda yake faruwa da zaka ga cewa, wannan ruwa mai launin ɗorawa dake zubowa daga cikin bakin wannan mutum-mutumi cikin jikin gimbiya Caiyàn yake ƙara komawa.

Rabin sa'a kacal ruwan ya ɗauka yana shiga cikin jikin gimbiya Caiyàn, idanuwanta s**a buɗe. Tuni sun juye sun koma ruwan ɗorawa. Gashin kan Caiyàn shima ya koma ruwan ɗorawa.

Kafun kace me wannan komai na jikin Caiyàn ya koma ruwan ɗorawa. Nan ta miƙe tsaye ta k**a hannun sarki Mazurus na hagu ta ciza.

Wani azababben zogi ya ratsa sarki Mazurus amma sai ya daure bai kwarara uban ihu ba.

Wani layi ruwan ɗorawa ya bayyana a damtsen hannun Mazurus inda kan kace me wannan ya guntule ya faɗi ƙasa.

Abun mamaki guntulewar wannan hannu bata haifar da zubowar jini ko rauni ba.

Gimbiya Caiyàn tayi nutso a ƙarƙashin wannan kogi wanda suke tsaye a cikinsa.

“Ham Erengalóssa habàskli (an karbi sadaukarwar ka)!” wata katuwar murya ta yiwa Mazurus magana.

A daidai wannan lokaci ne, hannun gimbiya Caiyàn ya taso daga ƙarƙashin wannan kogi. Hannun nata yana riƙe da wani hannu wanda aka samar daga sinadari na musamman.

Wannan hannu ya taho a hankali ya haɗe da dungulmin hannun sarki Mazurus na hagu wanda aka sare ɗazu.

Wani masifaffen raɗaɗi ya ratsa sarki Mazurus ya ɗaga kansa sama, ya kwarara uban ihu wanda ya cika dodon kunne.

Gaba ɗaya jijiyoyin jikin Mazurus s**a kawo haske na tsawon daƙiƙa goma kafun su ɓace ɓat!

Nan take ya fara ƙamshin wani masifaffen ƙarfin iko wanda ya wuce a misalta.

Wannan hannu ya maye gurbin hannun sarki Mazurus na ainihi. Hannun ya kasance baƙi ƙirim kuma waɗansu irin baƙaƙen gashi sun cika shi ta ko'ina.

A tsakiyar tafin wannan hannu, akwai waɗansu guraben ramuka guda uku. Dukkansu suna bayar da haske.

A hankali hannun Caiyàn ya sake nutsewa a cikin wannan kogi.

A wannan lokaci waɗansu sakonni s**a shigo allon ruhin Mazurus.

“Ka samu nasarar samar da fasahar Erénur: Maɗaukar duwatsun daraja guda uku.
“Dutsen B: (babu).
“Dutsen S: (babu).
“Dutsen X: (babu).
“Idan kana son morar fasahar Erénur ɗari bisa ɗari mallaki waɗannan duwatsu guda uku.”

Sarki Mazurus yana gama sauraron wannan saƙo ya cika da tsananin farin ciki. Ya samu nasarar abinda ya zo nema.

Sarki Mazurus ya sadaukar da rayuwar Caiyàn ga wannan kogi kuma ya sadaukar da hannunsa na hagu. Idan ka lura da gimbiya Caiyàn da hannunsa na hagu duk sun nitse a cikin wannan kogi.

Ita kuwa fasahar Erénur fasaha ce wadda ake maye gurbin hannun hagu da ita. Sarki Mazurus ya maye hannun hagunsa da wannan fasaha.

Kamar yadda mai saurare yaji kuma ya gani, a jikin Erénur akwai waɗansu guraben ramuka guda uku waɗanda aka yi su domin ɗaukar duwatsun daraja guda uku.

Wannan ita ce fasahar Erénur. Fasahar dake buƙatar tsarkakken jinin iYàn (ƙabilar su Romaiyan) da hannun hagun ɗan ƙabilar Ijunú.

“Tú Erengalós Ijunú lí! (Ni ne Erengalós Ijunú)!” inji sarki Mazurus Asaryan.

Yana gama faɗin haka ya zube a gaban wannan mutum-mutumi yayi gaisuwa sa'annan ya miƙe tsaye ya juya ya tafi.

***

A daidai wannan lokaci ne, wani saƙo ya shigo cikin allon ruhin sarauniya Zena O. Jemage.

Babu wanda yasan me saƙon yake tafe dashi amma sai gani kawai akayi ta haɗe gira kuma ta murtuƙe fuska.

Sarauniya Zena O. Jemage ta miƙe tsaye daga kan karagar mulkinta ta fara kaiwa da komowa.

Gaba ɗaya hadiman ta mutum goma sha-uku suna tsaitsaye a gefenta cikin tsananin nutsuwa.

Daga can sarauniya Zena O. Jemage ta koma kan karagar mulkinta ta zauna ta fiddo wani ƙaramin mudubi.

Mudubin yai haske, wata murya ta fara magana ba tare da an nuno mai yin maganar ba.

“An samar da kishiyar Baihindír!
“Abinda ya k**ata muyi a wannan lokaci shi ne, mallakar Baihindír. Daga nan sai mu nemo waɗannan duwatsun daraja guda uku!!
“Kije ki ɗauko takobin Jemage babban mataki!!!”

Muryar ta ɗauke a daidai wannan waje. Inda ace zaka lura da ka fuskanci cewa, gaba ɗaya mutanen Zena O. Jemage sun durƙusa kan gwiwowinsu suna biyayya ga wannan murya.

Sarauniya Zena O. Jemage ta ja dogon numfashi ta dubi ɗaya daga cikin waɗannan mutane tace, “Ka turo min ma'aboci fasahar Adawa dashi nake son yin wannan gagarumar tafiya!”

Mutumin ya gyaɗa kai cikin tsananin biyayya.

***

Al'amarin Haihan kuwa, tuni ya koma gida ya ci gaba da harkokinsa tamkar bashi ne shugaban ƙungiyar Miciji ba.

Wata rana da tsakiyar dare yana kwance yana barci, wani abu ya tokare zuciyar sa. Tsananin zogi da raɗaɗin da yake ji ne yasa ya farka a firgice.

Nan take yayi arba da Miciji tsaye a gabansa cikin mummunar siffa. Fuskar sa tana murtuƙe ya dakawa Haihan tsawa.

“Bawana! Ashe har ka samu damar dawo gida, ka huta?

“Ka manta aikin da yake gabanka na neman Ebalos da rigar Baihindír?

“To, bari na faɗa maka an samar da kishiyar Baihindír k**ar yadda zata ɗauki duwatsun daraja guda uku haka itama kishiyar zata ɗauka.

“Ya zamo dole a gare ka, ka shiga duniya ka nemo Ebalos kuma ka samo wannan riga. Saboda kada ka manta. Ebalos, duwatsun daraja guda uku da rigar Baihindír suna da alaƙa!”

Miciji yana gama faɗin haka ya ɓace daga wannan waje. Hankalin yarima Haihan a tashe ya bar wannan birni nasu, ba tare da wani shiri ba.

***

Dukkan waɗannan abubuwa dake faruwa a ƙungiyoyi daban-daban na matsafa da asiri suna faruwa sak**akon samar da fasahar Erénur da sarki Mazurus Asaryan yayi.

Idan ka saurari maganganun su zaka fuskanci kimar Erénur ta kai kimar rigar Baihindír. Saboda dukkansu amfanin su guda ne. Maɗaukar duwatsun daraja guda uku.

Rigar da Manya s**a jagoranci wani farmaki sa'adda zasu ƙwato ta a hannun wani babban sarki.

***
~Ɓangaren Sauraban.
***

Tuni a wannan lokaci Sauraban ya juye ya koma abun tsoro. Hakan yana da alaƙa da shigar sa ƙungiyar Jemage.

Wani irin ƙarfin iko na musamman yana tashi daga jikin Sauraban. Lamarin da yasa yake baiwa dakarun dake tsaron wannan kurkuku wahala kenan kullum.

A kullum sai Sauraban ya tsere daga cikin wannan kurkuku amma kafun ya haura sama, sarauniya Jazwirà zata bayyana kuma ta k**a shi.

Al'amarin da yake fusata Sauraban kuma yake bashi tsoro kenan. Saboda ta daina amfani da fasahar Siwod-siwin akansa. Da zallar ƙarfin ikonta take k**a shi kuma ta ladabtar dashi.

Sai da Sauraban ya jarraba tserewa daga cikin kurkukun sau arba'in amma bai samu nasara ko sau ɗaya ba.

Lamarin da ya sake girgiza shi kenan, ya ajiye maganar guduwa daga cikin wannan kurkuku a gefe guda.

A wannan rana yana zaune a cikin wannan kurkuku yana ta tunanin hanyar da zaiyi amfani da ita ya tsere. Kusan duk hikimominsa da dabarunsa sun ƙare amma bai samu nasara ba.

Ba zato ba tsammani! Bangon ɗakin da yake ciki ya tsage, wannan 'yar budurwa wacce ta kira kanta da suna 'Yar Baiwa ta bayyana a gabansa.

Sauraban ya zabura zai rufe ta da duka amma sai wani ƙarfin iko kwatankwacin irin na sarauniya Jazwirà ya ziyarci wannan waje. Bisa dole Sauraban ya saduda kuma yayi ladabi.

“Nazo ne domin na baka labarin mutumin da aka fi tsana a duniya, Erengalós. Ka nutsu ka saurare ni!”

Sauraban yana jin haka ya ja dogon numfashi ya ƙurawa 'Yar Baiwa idanu. Zuciyarsa tana bashi umarnin ya nutsu ya saurare ta.

A wannan lokacin ma, faifan bidiyo ta sake samarwa wanda ya fara nuna wani al'amari da ya taɓa faruwa.

***
~Shekarar 401 kafun Amjusàn.
~Doron ƙasa ta tara.
***

Wata ƙaramar runduna ce ta waɗansu mutane keta tafiya a gefen wani ƙaramin ƙauye. Dukkansu suna sanye da baƙaƙen tufafi. Babu abinda yafi jan hankalin mutane a jikin waɗannan mutane k**ar gashin kansu.

Eh, gashin kansu k**ar na kowa ne. To, amma wani baƙin hayaƙi ne yake tashi daga cikinsa.

Kafun kace me wannan wajen da waɗannan mutane suke tsaitsaye ya fara yin duhu.

Babban cikinsu ya zaro wata zabgegiyar takobi ya kwarara uban ihu tamkar gurnanin zaki. Ya nuna wannan gari wanda suke tsaitsaye a gefensa.

Nan take s**a kwarara uban ihu s**a afka cikin wannan gari. Ba sa kashe mutane kuma basa cutar dasu. To, amma duk wanda s**a ciji wuyansa sai kaga ya koma irinsu.

Sara da s**a baya tasiri akansu. Wuta bata ƙona su. Kafun mutanen wannan gari su gano lagonsu tuni sun mayar da kowa irin su.

Tufafin gaba ɗaya mutanen ya koma baƙi ƙirim. Wani baƙin hayaƙi ya fara tashi daga gashin kansu.

Cikin ƙanƙanin lokaci wannan gari yayi duhu. Alamun sun samu nasarar mallake shi kenan.

Bayan dogon lokaci s**a sake motsawa zuwa gari na gaba. Bayan sun ƙwace wannan gari s**a sake shiga cikin wani. A haka har s**a mallaki wani babban yanki.

'Yar Baiwa ta sa hannunta ta ja wannan bidiyo can gaba kusan ƙarshe.

Wajen da aka nuno, wani babban sarki ya gama karkashe dukkan irin waɗannan mutane guda ɗaya ne kawai ya gagare shi.

Shi ɗin ma guduwa yayi inda kafun ka ce me wannan an neme shi an rasa.

“Waɗannan mutane 'yan ƙabilar Ijunú ne. Ƙabilar da sarki Dahasàm ya tsine mata tun a wancan lokaci.

“Wannan shi ne dalilin da yasa al'ummar doron ƙasashe tara s**a tsani 'yan ƙabilar kenan.

“Wannan wanda ya tsere ance sunansa: Erengalós Ijunú.”

***

Sauraban yana gama ganin wannan al'amari ya girgiza kai cikin fahimta.

Daga bisani ya ɗago kansa ya dubi 'Yar Baiwa ya ce.

“ERENGALÓS IJUNÚ!!!”

***

Yau *30/06/2025*
Babi na gaba zai zo *03/07/2025* In Sha Allah.

Address

Sangaru Street
Gombe

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Ruhin Jarumtaka littafin yaki posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Ruhin Jarumtaka littafin yaki:

Share

Category