07/07/2026
KOKASAN MEYENE DAKILIN DAYA SA AL'UMMAR JAHAR GOMBE KE KAUNAR DR. BALA BELLO TINKA??
Dr. Bala Bello Tinka de haifeffen jahar Gombe ne Kuma anan fadar jahar Gombe, a Kuma unguwar Dawaki. Mahai fiyarsa Kuma yar cikin garin Dukul ne, sannan mahaifinsa Kuma Dan Garin Shani ne dake Gundumar Dukul a karamar hukumar Kwami, anan jahar Gombe.
Allah ya sanyawa alummar jahar Gombe kaunar wannan bawan Allah ne, bisa wassu dalilai kamar haka, Dr. Bala Bello Tinka de mazauni garine ba Dan bariki ba, Wanda ake kwana tare atashi tare dashi, sannan adaura aururruka gamida rade raden suna, kana agudanar da wa'azuzzuka da maulidai tare dashi, gabatar da janaizozi, da sauran wassu mu'amaloli daban daban.
Ya samu tarbiya Dede gorgodo, ya Kuma samu ilimin addini dana zamani, wannan abubuwan ne s**a nusantar dashi wajen kyautata mu'amalarsa ga alumma baki daya. Ya kasance yana mutunta mutane, yana girmama na sama dashi ( Sarakuna malamai da Dattawa ), yana Kuma mutunta na kasa dashi, ya kasance yanacin abinci tareda talakawansa harma da leburorinsa da s**a kasance ma'aikatane a maaikatarsa.
Wannan abun yakara bashi dama yasan damuwar Al'ummar jahar Gombe tunbeyi karfin da ze taimakawa bayin Allah ba, har izuwa lokacin da Allah ya h**e Masa arziki ba dukiya ba, ya kasance ya cire tuta a jahar nan ( Gombe ) wajen bada tallafi da gudumowa daban daban kamar haka:
* Yana bada gudumowa a bangaren Ilimi
* Yana bada gudumowa abangaren addini
* Yana bada gudumowa abangaren bunkasa tattalin arzikin jahar Gombe
* Yana bada gudumowa abangaren harkar Noma
* Yana bada gudumowa abangaren kiwon lafiya
* Yana bada gudumowa abangaren samawa matasa aikinyi.
* Yana bada gudumowa wajen taimakon marasa karfi.
Wannan duk bazai rasa nasaba ba, da irin tarbiyan daya samu da Kuma karatun addini dayayi ba ko yake kanyi, wannan shine dalilin dayasanya Allah ya Sanya kauna da soyayyar sa ga zukatan alummar jahar Gombe a yau. Kuma duk abinda na lissafo yakeyin nan, da kudin aljihunsa yakeyi ba kudin talakawa da aka bashi amana ta hanyar zabarsa awata kujerar siyasa ba, ko wata mukami da ze wakilci alumma ba.
Allah Ina rokonka ka karawa rayuwar wannan bawan Allah naka albark, ka karawa dukiyar sa yalwa, ka kareshi daga sharrin masu sharri, ka haskaka rayuwar tanan duniya da lahira.
Director BBT Media And Publicity Crew
βοΈ Abdullahi Muhammad Lalas