16/07/2025
YANZU YANZU: Ƙarya ne mijina bai sakeni ba tabbas mun ɗan samu saɓani da maigida na amma saɓani ne irin na mata da mijina, amma ƙarya ake min wlh bai sakeni ba—Aisha Buhari
Uwar gidan marigayi tsohon shugaban Najeriya Muhammad Buhari, Aisha ta bayyana cewar rahotanni da aka shafe yinin yau ana yaɗawa a kafafen sada zumunta na cewa ita bazawa ce mijinta ya daɗe da sakinta ƙarya ne Aisha tace.
"Maƙiya na ne ke yaɗa wannan labarin kuma ƙarya suke kawai dai mun ɗan samu saɓani ne irin na mata da miji kuma tuni muka fahimci juna, saboda haka ni matarsa ce har Allah ya karɓi rayuwar sa, kuma don Allah ina kira ga mutane su barmu muji da abinda ke damun mu na rashin da muka yi" In ji ta kamar yadda ta bayyana a wani taron manema labaran data kira a daren nan.
A yinin yau ne dai wasu rahotanni s**a bayyana cewar Buhari ya sake ta kafin ya rasu kamar yadda fitaccen marubucin nan.
Farfesa Farooq Kperogi, ya bayyana cewa mutane suna yaɗa labaran cewa Buhari ya ba wa matarsa, A’isha wasiyya cewa idan ya mutu ta roƙa masa afuwar ƴan Najeriya a madadinsa, "amma dai, a abin da na sani, babu aure a tsakanin Buhari da A’isha. Sun rabu tun kafin ya rasu, kuma ta koma amfani da asalin sunanta na A’isha Halilu". Cewar Farook, kamar yadda DK-TV ta ruwaito.
Farfesa Kperogi, kuma ya ƙara da cewa duk da cewa bai san inda wancan labari na wasiyya ya samo asali ba, amma in jama’a sun kula ko a lokacin da Buhari ya koma Daura bayan ya bar mulki ba da A’isha ya koma ba. Sannan kuma shi kaɗai ya koma Kaduna daga Daura.
"Magana ta gaskiya, ko lokacin da ya kwanta rashin lafiya a Ingila an nemi ta je ta kula da shi amma ba ta amince ba saboda a lokacin ita ba matarsa ba ce. Duk da haka, ta je ƴan kwanaki kaɗan kafin ya mutu bayan an takura ta". In ji shi.
Faefesa Farook, ya kuma ƙara da cewa, ko a yanzu da ake cikin jimamin mutuwarsa, "za a fahimci ba ta taka wata rawa a matsayin matarsa ba". In ji shi.
APA Hausa ✍️