Abdulmumini Media

Abdulmumini Media Polite Manner and Good Behavior

Muna gayyatar duk wanda yasamu daman halarta, wad'anda kuma bazasu samu dama ba muna buqatan Addu'oi da fatan alkhairi.A...
12/06/2026

Muna gayyatar duk wanda yasamu daman halarta, wad'anda kuma bazasu samu dama ba muna buqatan Addu'oi da fatan alkhairi.

Allah ka albakaci abinda muka d'an samu, ya kuma sa ya amfani Al'umma, Alfarmar Manzan Allah sallalllahu alaihi wa'alihi wasallam.

WANI LOKACIN SHIRU SHINE MAFI KARFIN AMSA Ba kowani lokaci ne ake buƙatar magana ba. Wasu lokutan, shiru shi ne mafi ƙar...
11/06/2026

WANI LOKACIN SHIRU SHINE MAFI KARFIN AMSA

Ba kowani lokaci ne ake buƙatar magana ba. Wasu lokutan, shiru shi ne mafi ƙarfin martani.

Shuru nada tasirinsa a cikin Al-Ummah:

1. Shiru yana nuna hikima: Ba kowanne lokaci ne magana zata magance matsala ba.
Wasu lokuta shiru yafi jan hankali.

2. Yana hana rikici: Lokacin da motsin zuciya ke tashi, shiru na taimakawa a guje wa maganganu masu zafi.

3. Yana sa mutane suyi tunani: Idan ka tsaya shiru, wasu zasu fara tambayar kansu ko fahimtar halin da ake ciki.

4. Yana nuna iko da kai: Shiru yana nuni da cewa kai ne ke sarrafa yanayinka, ba yanayi yana sarrafa ka ba.

5. Yana gina daraja: A cikin al’umma, wanda yasan lokacin shiru yakan samu girmamawa da daraja daga mutane.

Ka tunani, wani lokacin magana na iya kara rikici, amma shiru yana warkar da zuciya da zaman lafiya a cikin al’umma.

Allah kayi mana tsari daga mummunar furuci🤲

Alhamdulillahi...Muna miqa sakon taya murnanmu ga Dr. Muhammad Mujtaba Abdulkadir Sheikh Musa Jahun (Radiyallahu anhu).K...
10/06/2026

Alhamdulillahi...

Muna miqa sakon taya murnanmu ga Dr. Muhammad Mujtaba Abdulkadir Sheikh Musa Jahun (Radiyallahu anhu).

Kalmomin mu sun gaza wurin fad'an alkhairan sa, kuma hidimar sa ga Al'umma da janibin sayyidina Rasulallahi Sallalllahu alaihi wa'alihi wasallam, ya chanchanci sama da haka, bamu da abinda zamuce sama da Alhamdulillah.

Maulana Dr. Muna qara mika saqon taya murnanmu gareka, Allah kuma ya maka jagoranci, Alfarmar Manzan Allah sallalllahu alaihi wa'alihi wasallam.

Congratulations again Sir, in Advanced.
10-06-2026.

You're all invited...
08/06/2026

You're all invited...

Don Allah Mu Sanya Sheikh Nuru Khālid A Addu'a 😢Allah Ya Bashi Lafiya Albarkar Annabi ﷺ 🤲
06/06/2026

Don Allah Mu Sanya Sheikh Nuru Khālid A Addu'a 😢

Allah Ya Bashi Lafiya Albarkar Annabi ﷺ 🤲

04/06/2026

Alhamdulillahi for my first semester 400 Level result. ✔️✔️✔️💯

* Sirrin Shehu Tijjani RTA, Sheikh Ahmad tijjani bn Maulana sheikh dahiru Usman bauchi RTA 'yaya Malam.Sirrin Shehu Ibra...
03/06/2026

* Sirrin Shehu Tijjani RTA, Sheikh Ahmad tijjani bn Maulana sheikh dahiru Usman bauchi RTA 'yaya Malam.

Sirrin Shehu Ibrahim inyãss (Professor Ibrahim Ahmad Maqary).

Sirri cikin sirrin 💯🤝
Alhamdulillah 🥰

Innalillahi wa inna ilaihi raji’un!Allah yayiwa malamin mu, shehinmu, kuma da shehin mu, wato Sheikh Alhafiz Muhammad Mu...
29/05/2026

Innalillahi wa inna ilaihi raji’un!

Allah yayiwa malamin mu, shehinmu, kuma da shehin mu, wato Sheikh Alhafiz Muhammad MustaphaSheikh Ahmadu Bolari Gombe rasuwa.

Muna roqon Allah tabaraka wa ta'ala yajikansa da rahama Alfarmar sayyiduna Rasulallahi S. A. W.

Amin...

Allah maka rahama Malam

ALLAHU AKBAR: Ku Karanta Hudubar Bankwana Mai Ratsa Zuciya Da Annabi SAW Ya Yi A Irin Wannan Rana Ta Yau (Arfa)A irin wa...
26/05/2026

ALLAHU AKBAR: Ku Karanta Hudubar Bankwana Mai Ratsa Zuciya Da Annabi SAW Ya Yi A Irin Wannan Rana Ta Yau (Arfa)

A irin wannan ranar ce 9 ga watan Zul-Hijjah, shekar ta goma bayan Hijira a Dutsen Arafat (ranar Arfa kenan) Annabi Muhammad S.A.W ya yi wata huduba mai ratsa zuciya.
Fiyayyen Halitta (S.A.W) Ya fara da cewa:
*Ya ku mutane ku ba ni hankalinku, domin mai yiwuwa ba zan sake kasancewa da ku bayan wannan shekarar ba, saboda haka ku saurari abinda nake gaya maku da kyau, kuma (ku isar da abinda zan gaya maku) ga wadanda ba su a wannan wuri a yau.

*Ya ku mutane kamar yadda ku ka ri'ki wannan
wata, (na Hajji) da wannan rana (ta Arfa) dakuma wannan gari (na Makka) da girma kuma abin tsarewa, to, haka kuma ku riki ran Musulmi da kuma dukiyoyinsu da girma abin kuma karewa, ku maida wa mutane kayan da s**a ba ku amana. Kar ku cuci kowa, saboda kar wasu su cuce ku.

*Ku tuna fa, hakika Allah zai yi sakayya akan ayukakanku. Allah (SWT) ya hana cin riba,(wato kudin ruwa) saboda haka, duk abin da aka kulla ta kudin ruwa sai an warware shi.
*Ku yi hattara da shaidan, domin kiyaye
addininku. Yanzu kan ya fidda ran batar da ku akan manyan abubuwa (na sabo) saboda haka ku guji binshi akan kanana.

*Ya ku jama'a hakika kuna da hakki bisa
matayenku, amma su ma suna da hakki bisa kanku, to hakkin su ne akan ku da kuciyar da su, kuma ku tufatar da su akan jin kai. ku bi da su kyakkyawan biyarwa. Ku kuma tausasa musu domin su majibintan al'amurran ku ne, kuma mataimakan ku, Hakki ne akan su da kar su yi abota da duk wanda ba ku so, kuma su nisanci
zina.

*Ya ku jama'a, ku yi kyakkyawar bauta ga Allah (SWT) ku tsaida salloli biyar (5) na farilla, ku azumci watan Ramadan, kuma ku bada zakka. Ku aikata aikin Hajji idan har kun samu damar yi.

*Ku sani fa, kowane musulmi dan uwan musulmi ne. Dukkan ku daidai ku ke. Ba wanda yake da fifiko saman wani sai wajen tsoron Allah da aikata kyawawan ayyukka.
*Ku tuna fa (ya ku jama'a) wata rana za ku tsaya gaban Ubangijinku, domin sakamako

Address

Gombe

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Abdulmumini Media posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Abdulmumini Media:

Share