Abdulmumini Media

Abdulmumini Media Polite Manner and Good Behavior

Wannan shi ne masallacin Quba da aka fara ginawa a tarihin Musulinci, ba da tubali da kasa kawai ba, an kwabashi cike da...
25/05/2025

Wannan shi ne masallacin Quba da aka fara ginawa a tarihin Musulinci, ba da tubali da kasa kawai ba, an kwabashi cike da tsoron Allah tsantsarsa.

لَمَسْجِدٌ أُسِّسَ عَلَى التَّقْوَى مِنْ أَوَّلِ يَوْمٍ أَحَقُّ أَنْ تَقُومَ فِيهِ

A nan aka assasa wanzuwar hijira.. aka tabbatar da sallah.. kuma daga nan aka fara tabbatar da ambaton Allah a ban kasa.

A nan ne Manzon Allah (saw) ya yi alwala, nan ya yi sallah, sannan ya sanar da cewa Musulinci ya samu yancinsa bayan shekaru ana wahalar da shi.

A nan gurin ne Manzon Allah (saw) ya ce raka'a biyu karbabbiya dai-dai take da ladan aikin Umrah saboda kimarsa. Nan miliyoyi s**a yi addu'a aka amsa. Nan miliyoyi s**a yi sallah ta karbu.

Mutane daruruwa na ta shiga. Wasu suna Sallah. Wasu na hoto. Wasu kuma suna fashewa da kuka.

Amma ni kuma...

Ina tsaye ina tunanin cewa masallacin nan ba tarihi kawai yake dauke da shi ba, yana cike da wata ma'ana mai nuni da cewa duk abin da ya zama babba to da dan karami ya fara.

Masallacin Quba yana gaya mana cewa kyallin da yake gabanka a yau, zai iya zama hasken rana matukar ka assasashi da kyakkyawar niyya.

17/05/2025

DON MANZAN ALLAH SALLALLAHU ALAIHI WASALLAM AKAYI DUNIYA DA LAHIRA.

Maulana Sheikh Dahiru Usman Bauchi R.T.A. Yana cewa :

Misalin da zai tabbatar maka da hakan shine: Idan wani Babban mutum kamar ace Sarkin yanka ya ziyarci wani Babban mutum dashi da tawagarsa, Bayan sun sauka a masauki sun huta an kawo Abinci Sarki yaci ya koshi, Iyalan Sarki suma sunci sun koshi, manyan Cabinate na Sarki ma sunci sun koshi, fadawan sarki sunci sun koshi, masu gadin Gidan suma sunci sun koshi, aka nemo Almajirai suma s**aci s**a koshi, Aka nemo masu cin Abinci suma s**aci s**a koshi, Abinci ya rage aka rasa masu ci, Aka diba aka zubar a juji (Bola), karnuka s**aci Agwagi s**aci kadangaru s**aci.

TAMBAYA: Shin duk mutanan da s**a amu s**aci Abincin nan shin don su Akayi? Amsa kaitsaye itace: A'a, Anyi ne don wannan Baban Bako guda daya.

To haka lamarin yake, Duk wanda kaga yasamu wani Abu a Duniya ya samu ne sanadin Annabi Muhammadu ne S.A.W., Domin Idan Kaji Namu to da mai-shi, mai abin nan kuma shine sayyiduna Rasulallahi sallallahu alaihi wasallam.

Allah yakara Mana son Manzon Allah S.A.W., alfarmar Manzan Allah sallallahu alaihi wasallam.

16/05/2025
15/05/2025
09/05/2025
SHEHU ALIYU HARAZIMI YANA CEWA.(RTA)Ka lazumci yin shiru Idan kaga ana zage zage ka tashi kabar wajen duk Wanda yayi Shi...
07/05/2025

SHEHU ALIYU HARAZIMI YANA CEWA.(RTA)

Ka lazumci yin shiru Idan kaga ana zage zage ka tashi kabar wajen duk Wanda yayi Shiru ya Tsira, Wallahi Akwai mutanen da in kazage su sai an Shekaru (40) a cikin 'ya'yan ka ba mutumin kirki ko Daya.

Kuma Allah bai rubuta Sunansu ba b***e kuma ace maka Gasu basu da wata Alama da za'a Gane su ubangiji (SWT) ya boye kayan shi Akwai Wadanda za,a rainasu Amma idan ka kuskura ka zage su to wallahi Gidanka shikenan ya mutu kenan har abada,
Allah ka kiyayemu,
'Yan uwa Wallahi mubar wannan muyi Abunda yake Gabanmu na karatu Ibada da Sana'a.
Duk abunda bai shafe muba mu barshi kawai

Allah ya kashemu da son bayin Allah, alfarmar Manzan Allah sallallahu alaihi wasallam.

07/05/2025

ALHAMDULILLAH, ALHAMDULILLAH, ALHAMDULILLAH.

Godiya ta tabbata ga Allah wanda yasanya result dina na first semester 300Level Federal University of Kashere yayi kyawun da ban taba samun sakamako mai kyau irinsa ba.

Ina mai amfani da wannan dama wurin godiya ga dukkanin yan uwa wadanda s**a tayamu Addu'a har nasarar ta tabbata, dafatan Allah tabaraka wa ta'ala ya cigaba da bamu nasara acikin dukkanin rayuwarmu, alfarmar Manzan Allah sallallahu alaihi wasallam.

Muhammad Abdulmumini Gombe.
07/05/2025.

02/05/2025

Address

Gombe

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Abdulmumini Media posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Abdulmumini Media:

Share