17/05/2025
DON MANZAN ALLAH SALLALLAHU ALAIHI WASALLAM AKAYI DUNIYA DA LAHIRA.
Maulana Sheikh Dahiru Usman Bauchi R.T.A. Yana cewa :
Misalin da zai tabbatar maka da hakan shine: Idan wani Babban mutum kamar ace Sarkin yanka ya ziyarci wani Babban mutum dashi da tawagarsa, Bayan sun sauka a masauki sun huta an kawo Abinci Sarki yaci ya koshi, Iyalan Sarki suma sunci sun koshi, manyan Cabinate na Sarki ma sunci sun koshi, fadawan sarki sunci sun koshi, masu gadin Gidan suma sunci sun koshi, aka nemo Almajirai suma s**aci s**a koshi, Aka nemo masu cin Abinci suma s**aci s**a koshi, Abinci ya rage aka rasa masu ci, Aka diba aka zubar a juji (Bola), karnuka s**aci Agwagi s**aci kadangaru s**aci.
TAMBAYA: Shin duk mutanan da s**a amu s**aci Abincin nan shin don su Akayi? Amsa kaitsaye itace: A'a, Anyi ne don wannan Baban Bako guda daya.
To haka lamarin yake, Duk wanda kaga yasamu wani Abu a Duniya ya samu ne sanadin Annabi Muhammadu ne S.A.W., Domin Idan Kaji Namu to da mai-shi, mai abin nan kuma shine sayyiduna Rasulallahi sallallahu alaihi wasallam.
Allah yakara Mana son Manzon Allah S.A.W., alfarmar Manzan Allah sallallahu alaihi wasallam.