01/03/2026
LABARAI | ABIN MAMAKI DAGA HABASHA
Wani dattijo mai suna Isaac Adamo, dan shekaru 78, ya bayyana tarihin rayuwarsa da ya dauki hankalin jama’a, inda ya auri mata 23 tare da haifar da ’ya’ya 70.
Isaac Adamo na zaune ne a garin Malabi, yankin Oromia a ƙasar Habasha (Ethiopia). Ya auri matarsa ta farko ne yana da shekara 23, kuma cikin tsawon shekaru 55 da s**a biyo baya, ya kara aure har ya kai mata 23.
A cewarsa, bai wuce shekara guda ba tun da ya auri amaryarsa ta ƙarshe, wadda ita ce ta 23 a jerin matansa. A halin yanzu, ƙaramin ɗansa ko ’yarsa na da watanni uku, yayin da babban ɗansa ya kai shekaru 53.
Isaac Adamo ya shahara wajen kiwon dabbobi, inda a wani lokaci ya mallaki dabbobi sama da 800. Ya bayyana cewa yalwar dukiya ce ta sa yake yawan aure.
> “Nakan yi aure duk lokacin da nake so, saboda ina da shanu da yawa, ina da dukiya da kadarori,” in ji shi.
“Dogarona a rayuwa shi ne kiwon dabbobi; ina da raƙuma, shanu da awaki masu yawa.”
Ya kuma ce yana yin aure ne a duk lokacin da ya rabu da ɗaya daga cikin matansa.
> “Idan na ga mace mai kyau, sai na saki ɗaya daga cikin waɗanda nake tare da su, na auro wata,” in ji Isaac.
Matarsa ta farko ta rasu, yayin da a yanzu yake tare da mata uku kacal, bayan ya rabu da mata 19. Ya ce wasu rabuwar ta faru ne sakamakon saɓani, wasu kuma ba tare da wani dalili na musamman ba.
Daga cikin ’ya’yansa 70, akwai maza 36 da mata 34. Isaac ya bayyana cewa a yanzu ba shi da niyyar ƙara aure.
A cewarsa, idan aka haɗa ’ya’yansa da jikokinsa, iyalinsa sun kai mutum 279. Sai dai ya amince cewa dukiyarsa ta ragu a yanzu idan aka kwatanta da baya.
Babban ɗansa na da suna Ibrahim, yayin da ƙarama kuma ake kiranta Dahab. Isaac ya ce mutane da dama kan tambaye shi yadda yake kula da tarbiyyar wannan adadi na ’ya’ya, amma a ganinsa hakan bai da wahala matuƙa, musamman idan akwai dukiya.
Yanzu haka, labarin rayuwar Isaac Adamo na ci gaba da janyo muhawara da mamaki a tsakanin jama’a.