09/11/2021
Shugaban Ƙasa Buhari Ya Isa Birnin Paris Domin Halatar Taron Zaman Lafiya
Daga Abdul Dan Arewa
A ranar Talata ne shugaban kasa Muhammadu Buhari ya sauka a birnin Paris na kasar Faransa domin halartar taron zaman lafiya na kwanaki uku na birnin Paris wanda zai gudana daga ranar 11-13 ga watan Nuwamban 2021.
Mai ba shugaban kasa shawara na musamman Femi Adesina ne ya sanar da hakan a wata sanarwa mai taken ‘Shugaba Buhari Ya Isa birnin Paris Domin Ziyarar Aiki, Dandalin Zaman Lafiya’.
A cewar sanarwar, Buhari zai kasance bako ga shugaban kasar Faransa, Emmanuel Macron, a Palais de l’Élysée, gabanin taron zaman lafiya.
Jirgin Buhari ya sauka a filin jirgin saman Le Bourget da karfe 2:45 na rana, in ji Adesina.
Sanarwar ta ci gaba da cewa, “A yayin ziyarar aiki a ranar Laraba, shugaba Buhari zai gana da takwaransa na kasar Faransa, domin tattauna batutuwan da s**a shafi kasashen biyu, musamman kan karfafa huldar tattalin arziki, inganta hadin gwiwa a fannin tsaro, da yin aiki tare a fannin ilimi, kiwon lafiya. da kuma dakatar da barazanar COVID-19 ga tattalin arzikin duniya.
“Daga ranar Alhamis, Shugaba Buhari zai hadu da shugabannin duniya, shugabannin kungiyoyin kasa da kasa, shugabannin kungiyoyin farar hula, da kuma kamfanoni masu zaman kansu a Grande Halle de La Villette don tsara dabarun gudanar da ingantaccen shugabanci don duniyar zaman lafiya, tare da wakilai, manyan darajoji, da tarurrukan bita.
“An shirya shugaban kasa zai yi tsokaci a wajen taron domin bayyana irin kwarewar da Najeriya ta samu ga duniya, da kuma kokarin da aka yi na kawo zaman lafiya. Sauran wadanda s**a yi jawabi sun hada da shugaba Macron, mataimakin shugaban kasar Kamala Harris na Amurka, da Sheikh Hasina, firaministan kasar Bangladesh."