Progress Radio Tv Gombe

Progress Radio Tv Gombe MEDIA PRODUCTION

Ku kasance da Maryam Atiku a Zango Na Biyu na kafar yaɗa labarai ta Progress Radio Gombe Najeriya.
23/08/2025

Ku kasance da Maryam Atiku a Zango Na Biyu na kafar yaɗa labarai ta Progress Radio Gombe Najeriya.

"Inuwar giginya," a ƙarasa mana wannan karin maganar, Progress Radio ke muku barka da safiyar Asabar.
23/08/2025

"Inuwar giginya," a ƙarasa mana wannan karin maganar, Progress Radio ke muku barka da safiyar Asabar.

Gwamnatin Najeriya ta sanar da cewa ba za ta gajiya ba har sai ta farauto maharan da s**a kashe masallata a garin Malumf...
22/08/2025

Gwamnatin Najeriya ta sanar da cewa ba za ta gajiya ba har sai ta farauto maharan da s**a kashe masallata a garin Malumfashi da ke jihar Katsina, saboda a cewarta, maharan sun nuna rashin imani a harin.

Cikin wata sanarwa da ministarn yaɗa labaran ƙasar ya fitar, gwamnatin tarayya za ta tabbatar an maharan tare da gurfanar da su a gaban shari'a, k**ar yadda kafar yaɗa labarai ta BBC ta ruwaito.

Ministan ya ce tuni jami'an tsaro s**a fara bibiyar maharan, inda ya ƙara da cewa ba za su gajiya ba sai an k**a waɗannan s**a kai harin.

Ya ce Shugaba Tinubu na miƙa ta'aziyarsa ga iyalan waɗanda aka kashe, da mutanen Malumfashi da jihar Katsina da ma ƙasar baki ɗaya da ma iyalan waɗanda aka kashe.

Ya ce daga cikin ƙoƙarin da gwamnati ke yi na kawo ƙarshen lamarin akwai k**a fitattun ƴan ƙungiyar Ansaru da ake zargi da fasa gidan yarin Kuje da sauran nasarori.

Hukumar Hasashen Yanayi ta Najeriya (NiMet) ta sanar da yiwuwar samun ruwan sama da iska daga ranar Juma’a zuwa Lahadi a...
22/08/2025

Hukumar Hasashen Yanayi ta Najeriya (NiMet) ta sanar da yiwuwar samun ruwan sama da iska daga ranar Juma’a zuwa Lahadi a sassa daban-daban na ƙasar.

A cewar rahoton da ta fitar, jihohin Arewacin ƙasa k**ar Kano, Katsina, Sokoto, Kebbi, Zamfara, Kaduna, Jigawa, Borno, Yobe da Taraba za su fuskanci guguwar iska da ruwan sama matsakaici.

A tsakiyar ƙasa kuma, akwai yiwuwar samun ruwan sama kaɗan a Babban Birnin Tarayya Abuja, Nasarawa, Benue, Kogi, Kwara, Neja da Filato.

Haka zalika, a yankin Kudu anyi hasashen yanayi mai zafi da ruwan sama kaɗan a jihohi irin su Oyo, Osun, Ekiti, Ondo, Edo, Enugu, Imo, Abia, Anambra, Delta, Rivers, Bayelsa, Cross River da Akwa Ibom.

NiMet ta gargaɗi jama’a da su guji tuƙi a lokacin ruwan sama mai yawa, a cire na’urorin lantarki daga soket, a guji zama ƙarƙashin manyan itatuwa, sannan a ɗaure kayayyakin da ba su da ƙarfi.

Haka kuma ta shawarci manoma da su guji amfani da taki da maganin kwari kafin ruwan sama, yayin da ta bukaci kamfanonin jiragen sama da su riƙa samun rahoton yanayi na musamman domin tsara tashi yadda ya k**ata.

Babbar jam'iyyar adawa a Najeriya Peoples Democratic Party (PDP) ta ce a shiye ta ke ta mayar wa Ministan babban birnin ...
22/08/2025

Babbar jam'iyyar adawa a Najeriya Peoples Democratic Party (PDP) ta ce a shiye ta ke ta mayar wa Ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyesom Wike, martani akan duk wani mataki da zai ɗauka dangane da babban taronta na ƙasa

Gwamnatin jihar Kano ta bayyana wani shiri na yi wa tubabbun ƴandaba afuwa, ƙarƙashin wani shirinta na musamman domin ka...
21/08/2025

Gwamnatin jihar Kano ta bayyana wani shiri na yi wa tubabbun ƴandaba afuwa, ƙarƙashin wani shirinta na musamman domin kakkaɓe matsalar daba a fadin jihar.

Daba da ƙwacen waya su ne manyan matsalolin tsaro da ke addabar birnin Kano da wasu yankuna na jihar.

Matsalar ta haifar da asarar rayuka da dama, inda har gwamnati ta kafa wani kwamitin yaƙi da matsalar, sai dai duk da haka lamarin ya zamo mai wahala.

A lokuta da dama mahukunta sun zargi al'umma da rashin haɗin kai ta hanyar gaza fallasa ƴan daba da ke tsakaninsu, yayin da a ɓangare ɗaya kuma al'ummar ke zargin hukumomi da gaza ɗaukar ƙwararan matakan yaƙi da matsalar.

A wani rahoto da Babban Bankin Ƙasa, CBN, ya fitar a ranar 19 ga watan Agusta, asusun na ƙasar wajen ya ƙaru zuwa Dalar ...
21/08/2025

A wani rahoto da Babban Bankin Ƙasa, CBN, ya fitar a ranar 19 ga watan Agusta, asusun na ƙasar wajen ya ƙaru zuwa Dalar Amurka Biliyan 41.

A cewar CBN, rabon da asusun ya ƙaru irin haka, tun ranar 3 ga watan Disamba, 2021.

Mai magana da yawun shugaban ƙasar, Bayo Onanuga ne ya wallafa sanarwa ta Babban Bankin ƙasar CBN, na ci gaban da aka samu ya zuwa ranar 19 ga watan Agusta, a shafinsa na Facebook.

Jagoran Ɗarikar Katolika na duniya Fafaroma Leo na 14, ya yi ƙira da a tashi da azumi ranar Juma'a, don neman agajin mah...
21/08/2025

Jagoran Ɗarikar Katolika na duniya Fafaroma Leo na 14, ya yi ƙira da a tashi da azumi ranar Juma'a, don neman agajin mahalicci wajen samun wanzuwar zaman lafiya a yankin Gabas ta Tsakiya da kuma Ukraine, k**ar yadda kafar yaɗa labarai ta DW Hausa ta ruwaito.

Tsohon Ministan Ma'aikatar Sadarwa da Tattalin Arziƙi na zamani a Najeriya, Farfesa Isa Ali Ibrahim Pantami, ya yi Allah...
21/08/2025

Tsohon Ministan Ma'aikatar Sadarwa da Tattalin Arziƙi na zamani a Najeriya, Farfesa Isa Ali Ibrahim Pantami, ya yi Allah-wadai da kisan masallata da ƴan bindiga s**a yi a wani masallaci da ke ƙaramar hukumar Malumfashi, a jihar Katsina.

A ranar Talata da ta gabata ne, gwamnatin jihar ta tabbatar da cewa, maharan sun kashe mutum 13 a lokacin sallar Asuba a Unguwar Mantau, inda kuma adadin waɗanda s**a mutu ya ƙaru zuwa 30 daga baya.

Lamarin ya faru ne bayan ƴan ta’adda sun kai hari a matsayin ramuwar gayya ga al’ummar yankin, biyo bayan kwanton ɓauna da jama'ar unguwar s**a yi musu tare da kashe da dama daga cikin su.

Gwamnatin Amurka ta ce sabon mafi ƙarancin albashin Najeriya na N70,000 ba zai iya fitar da ma'aikata daga talauci ba sa...
21/08/2025

Gwamnatin Amurka ta ce sabon mafi ƙarancin albashin Najeriya na N70,000 ba zai iya fitar da ma'aikata daga talauci ba saboda tsananin matsin tattalin arziƙi da kuma faɗuwar darajar Naira.

A cikin rahoton haƙƙokin ɗan adam na 2024 da aka fitar a ranar 12 ga watan Agusta 2025, Ma'aikatar Harkokin Wajen Amurka ta nuna cewa albashin wanda darajarsa ta kai kusan dala $47.90 a wata, ya ragu ƙwarai saboda raguwar Naira fiye da N1,500 a kan kowace dala.

Rahoton ya kuma ce duk da an ninka albashin daga na baya, jihohi da dama ba sa aiwatar da shi saboda ƙarancin kuɗi, yayin da yawancin kamfanoni ƙanana da ke da ƙasa da ma'aikata 25 ba su cikin kariyar dokar.

Har ila yau, an bayyana cewa kashi 70–80% na ma'aikatan Najeriya suna cikin kasuwar da ba ta hukuma ba, inda dokokin albashi da aiki ba sa aiki yadda ya k**ata.

Rahoton ya yi gargaɗi cewa ƙarancin masu sa ido kan aiki na barin miliyoyin ma'aikata cikin haɗarin cin zarafi da rashin samun albashi mai inganci.

21/08/2025

"Ko wane tsuntsu," a ƙarasa mana wannan karin maganar, Progress Radio ke muku barka da safiyar Alhamis.

Address

Gombe

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Progress Radio Tv Gombe posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share