Progress Radio Tv Gombe

Progress Radio Tv Gombe MEDIA PRODUCTION

Rundunar sojin Isra'ila ta ce dakarunta huɗu sun mutu, yayin da wasu uku s**a jikkata bayan motarsu ta taka wani abin fa...
18/09/2025

Rundunar sojin Isra'ila ta ce dakarunta huɗu sun mutu, yayin da wasu uku s**a jikkata bayan motarsu ta taka wani abin fashewa a Rafah da ke kudancin Gaza.

A wani labarin kuma rundunar sojin ƙasar ta ce wani mutum ɗan ƙasar Jordan da ke tuƙa motar ɗaukar kayan agaji ya kashe sojojinta biyu a mashigar sarki Hussein da ke kan iyaka.

Jami'an tsaro sun ce mutumin ya soma ne da harbin sojojin kafin ya caccaka musu wuƙa.

Sun ce daga bisani wani mai gadi ya harɓe direban.

Hukumomi a Jordan sun ce an kulle mashigar, wadda ake kira mashigar Allenby a Isra'ila, saboda cunkoson ababen hawa.

Shirye-shiryen Zangon Farko tare da Bilkisu Musa Muhammad.
18/09/2025

Shirye-shiryen Zangon Farko tare da Bilkisu Musa Muhammad.

Gwamnatin Najeriya ta sake mayar da darasin tarihi a matsayin darussan dole da ɗalibai za su dinga yi makarantun firamar...
18/09/2025

Gwamnatin Najeriya ta sake mayar da darasin tarihi a matsayin darussan dole da ɗalibai za su dinga yi makarantun firamare da sakandare na ƙasar.

Wata sanarwa da ma'aikatar ilimi ta fitar a yau Laraba ta ce an ɗauki matakin ne domin "ƙarfafa kishi, da haɗin kai tsakanin 'yan ƙasa".

"A karon farko ɗaliban Najeriya za su fara yin darasin tarihi tun daga aji 1 na firamare zuwa aji 3 na ƙaramar sakandare [JSS3], yayin da 'yan aji 1 zuwa 3 [SS1 zuwa SS3] za su dinga yin darasin ilimin rayuwa da tsatso [Civic and Heritage Studies]," in ji sanarwar da ta wallafa a shafukan zumunta.

"'Yan aji 1 zuwa 6 na firamare za su san asalin Najeriya, da gwanayenta, da shugabanni, da al'adu, da siyasa, da addini, da mulkin mallaka, da kuma mulki bayan samun 'yancin kai.

"Ɗaliban JSS1-3 za su nazarci al'ummomi, da masarautu, da kasuwanci, da zuwan Turawa, da dunƙulewar Najeriya, da 'yancin kai, da dimokuraɗiyya, da kuma ɗabi'un mutum."

A shekarar 2007 ne gwamnatin Najeriya ta ƙaddamar da sabuwar manhajar karatu, inda a ciki ta cire darasin tarihi daga firamare da sakandare.

Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya sanar da kawo ƙarshen dokar-ta-ɓaci da ya ƙaƙaba a Jihar Rivers daga daren yau Laraba...
17/09/2025

Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya sanar da kawo ƙarshen dokar-ta-ɓaci da ya ƙaƙaba a Jihar Rivers daga daren yau Laraba, 17 ga Satumba, 2025.

A wata sanarwar da kakakin shugaban, Bayo Onanuga ya fitar, Tinubu ya umarci Gwamna Fubara, mataimakiyar sa Ngozi Nma Odu da kakakin majalisar Martins Amaewhule tare da sauran ƴan majalisa da su koma bakin aiki daga Laraba, 18 ga Satumba, 2025.

Tinubu ya bayyana cewa ya ayyana dokar ta-ɓaci a ranar 18 ga Maris, 2025 ne bayan rikicin siyasa tsakanin Gwamna Siminalayi Fubara da majalisar dokokin jihar ya haifar da durƙushewar ayyukan gwamnati.

Ya ce dokar-ta-ɓacin ta zama dole ne domin hana jihar faɗawa cikin tarzoma, inda aka dakatar da gwamna, mataimakiyar gwamna da ƴan majalisa na tsawon watanni shida.

Ya yi ƙira ga shugabannin siyasa a duk faɗin ƙasar da su tabbatar da zaman lafiya da kyakkyawar alaƙa tsakanin ɓangarorin gwamnati domin bai wa jama'a damar amfana da dimokuraɗiyya.

"Mai Hankali," a ƙarasa mana wannan karin magana, Progress Radio ke muku barka da safiyar Laraba.
17/09/2025

"Mai Hankali," a ƙarasa mana wannan karin magana, Progress Radio ke muku barka da safiyar Laraba.

Babbar Kotun Birnin Tarayya dake Abuja ta yi watsi da karar da aka shigar domin hana Hukumar Yaki da Cin Hanci da Rashaw...
16/09/2025

Babbar Kotun Birnin Tarayya dake Abuja ta yi watsi da karar da aka shigar domin hana Hukumar Yaki da Cin Hanci da Rashawa, wato ICPC, gudanar da bincike kan zargin almundahana a kudaden tallafin karatu na jihar Kano.

Karar ta fito ne daga sakataren dindindin na ma’aikatar ilimin gaba da sakandare ta Kano, Dokta Hadi Bala da wasu, inda s**a ce gayyatar da ICPC ta aikewa jami’an gwamnati ta karya musu hakki.

Mai shari’a Josephine Obanor ta yanke hukunci cewa gayyatar hukumar domin bincike ba ta karya hakkin mutum ba, tare da jaddada cewa masu karar sun kasa bayar da hujjar tauye musu hakki.

Saboda haka, kotun ta kori karar saboda rashin cancanta, tare da nanata cewa ba za a hana ICPC gudanar da aikinta na bincike bisa doka ba.

A wata sanarwa da kakakin hukumar, Demola Bakare, ya sanya hannu, ICPC ta ce hukuncin ya kara karfafa ikon hukumar wajen gudanar da bincike kan rashawa da almundahana a kasar.

Hukumar ta kuma jaddada aniyarta na ci gaba da aiki da gaskiya, gaskiya da bin doka domin tabbatar da gaskiya da rikon amana a bangaren gwamnati.

14/09/2025

Ra'ayoyin masu saurare kan rahotannin shirin Daga Wakilan Progress.

Mai Karantawa - Yusraa Ridwan.

Ku bayyana ra'ayoyin ku kan rahotannin shirin  Daga Wakilan Progress wanda da Yusraa Ridwan, zai gabatar da misalin karf...
13/09/2025

Ku bayyana ra'ayoyin ku kan rahotannin shirin Daga Wakilan Progress wanda da Yusraa Ridwan, zai gabatar da misalin karfe 10 na daren yau Asabar ga kadan daga rahotannin.

MDD : Babban Zauren Majalisar Dinkin Duniya ya kaɗa kuri'a don farfado da shirin samar da zaman lafiya, ta hanyar kafa kasashe biyu tsakanin Isra’ila da Falasdinu.

NAJERIYA : Hukumar ICPC, ta yi ƙira ga Majalisar Dokoki ta Ƙasa da ta gaggauta amincewa da dokar nan ta kwarmata bayanai (Whistle-Blower) domin ba ƴan ƙasa damar bayar da rahoton cin hanci ba tare da tsoro ko tsangwama ba.

ZAMFARA : Anbukaci Gwamnatin jahar Zamfara ta yi mai yuwuwa don samarda tsaro ga al'ummar jahar domin gudanarda harkokin yau da kullum a cikin natsuwa.

Gwamnatin Albania ta ɗauki sabon matakin ne musamman wajen yaƙi da cin hanci da rashawa ta hanyar naɗa wata na'ura ta ƙi...
12/09/2025

Gwamnatin Albania ta ɗauki sabon matakin ne musamman wajen yaƙi da cin hanci da rashawa ta hanyar naɗa wata na'ura ta ƙirƙirar basirar a matsayin minista.

Wannan na'ura, wacce aka raɗawa suna Diella, za ta kula da dukkan harkokin kwangilolin gwamnati da kuma yadda ake bayar da su, da manufar kawar da cin hanci da duk wata hanyar neman kusanci ko tsoratarwa a cikin tsarin.

Firaministan ƙasar, Edi Rama, ya bayyana cewa wannan shi ne karon farko da wata ƙasa a duniya ta ɗora na'ura ta basirar kwamfuta a matsayin mai riƙe da mukamin gwamnati.

A cewar sa, Diella ba za ta taɓa karkata ba ko ta yi son zuciya, domin ba ta da halayyar ɗan adam, abin da ke nufin tsarin zai kasance cikin gaskiya da tsabta.

Sai dai masana sun dasa ayar tambaya kan yadda za a tabbatar da gaskiya da adalci a tsarin, da kuma batun wanda zai ɗauki alhakin kura-kurai idan s**a faru.

Shin za ka iya jure raɗaɗin rabuwa da masoyiyarka kan Naira miliyan 100 kacal?
11/09/2025

Shin za ka iya jure raɗaɗin rabuwa da masoyiyarka kan Naira miliyan 100 kacal?

Rugugin sauƙar ruwa da iska mai ƙarfi ta mamaye sararin samaniya, yayin da ƙanƙara ke faɗowa daga sama.
11/09/2025

Rugugin sauƙar ruwa da iska mai ƙarfi ta mamaye sararin samaniya, yayin da ƙanƙara ke faɗowa daga sama.

11/09/2025

Sakonnin ku

Address

Gombe

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Progress Radio Tv Gombe posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share