AREWA TALK TV

AREWA TALK TV AREWA TALK TV Tashar Al,ummah
Tasha ta gaskiya da sahihanci cikin harshen Hausa.

Muna kawo muku labaran duniya, siyasa, tsaro, tattalin arziki, kimiyya, fasaha, da manyan abubuwan da ke faruwa a kowane lokaci — ba tare da son rai ko ɓoye gaskiya ba.

An gudanar da sallar idul Al-fitir a Birnin Tehran na kasar Iran a Yau asabar..
21/03/2026

An gudanar da sallar idul Al-fitir a Birnin Tehran na kasar Iran a Yau asabar..

YANZU-YANZU: Matatar Man Fetur Ta Dangote Ta Kara Farashin Man Fetur Zuwa 1,245 Kan Kowace LitaDaga Muhammad Kwairi Wazi...
20/03/2026

YANZU-YANZU: Matatar Man Fetur Ta Dangote Ta Kara Farashin Man Fetur Zuwa 1,245 Kan Kowace Lita

Daga Muhammad Kwairi Waziri

20/03/2026

Yadda Al’ummar Musulmi S**a Gudanar da Bukukuwan Sallah Cikin Farin Ciki a Jahar Gombe Dake Arewa Maso Gabas.

Rahoton Umar Muhammad Gadam

❤️

20/03/2026Eid-el-Fitr: Gwamna Inuwa Yahaya Ya Taya Al'ummar Musulmi Murnar Sallah; Ya Buƙaci a Ci Gaba da Addu'o'i da Ja...
20/03/2026

20/03/2026

Eid-el-Fitr: Gwamna Inuwa Yahaya Ya Taya Al'ummar Musulmi Murnar Sallah; Ya Buƙaci a Ci Gaba da Addu'o'i da Jajircewa Don Ganin Bayan Manyan Ƙalubalen Rayuwa

Gwamnan Jihar Gombe Muhammadu Inuwa Yahaya, CON, ya yi ƙira ga Al'ummar Musulmi da sauran 'yan ƙasa su ci gaba da jajircewa ga ibada, sadaukarwa da addu'o'i da aka saba a watan Ramadan, yayin da ake murna da bukukuwan sallar azumi (Eid-el-Fitr) na bana.

A saƙonsa na barka da sallah da ya fitar don murnar kammala azumin watan na Ramadan cikin nasara, Gwamnan ya jaddada cewa Eid-el-Fitr ba kawai lokaci ne na murna ba, lokaci ne ma na yin tunani da nazari mai zurfi, yana mai ƙira ga masu imani su ci gaba da ɗabbaƙa darussan da s**a koya a watan mai tsarki a harkokinsu na yau da kullum.

"Yayin da muke bikin Eid-el-Fitr, ina mana tuni cewa mu ci gaba da ɗabbaƙa kyawawan darussan watan Ramadan waɗanda s**a shafi ibada, biyayya da jajircewa. Dole ne mu yi riƙo da ƙa'idodin Musulunci waɗanda ke haɓaka zaman lafiya, haƙuri, tsantsaini da ƙauna," in ji Gwamnan.

Gwamna Inuwa Yahaya ya jaddada muhimmancin ci gaba da addu'o'in zaman lafiya, haɗin kai da wadata, musamman a wannan lokaci da ƙasar nan ke fuskantar ƙalubalen zamantakewa dana tattalin arziƙi.

Ya yi ƙira ga al'umma da cewa kar su yanke ƙauna, su ci gaba da dagewa kan imani da haɗin kai, yana mai bayyana ƙwarin gwiwar cewa Najeriya za ta yi nasara da samun ƙarin haɗin kai.

Ya kuma yi ƙira ga al'ummar Jihar Gombe su ci gaba da girmamawa da kare zaman lafiya da kwanciyar hankalin dake ci gaba da wanzuwa a jihar, yana mai bayyana zaman lafiya a matsayin ginshiƙin ci gaba mai ma'ana.

Gwamnan ya sake jaddada cewa gwamnatinsa ba za ta lamunci duk wani abu da zai iya kawo cikas ga zaman lafiyan jama'a ba, yana mai alƙawarin ci gaba da mai da hankali kan samar da romon demokraɗiyya ga jama'a.

Gwamna Inuwa Yahaya, wanda kuma shine Shugaban Ƙungiyar Gwamnonin Jihohin Arewa, ya bayyana muhimmancin wannan lokaci, musamman ganin yadda harkokin siyasa ke ƙara kankama a faɗin ƙasar nan, yayin da babban zaɓen 2027 ke gabatowa, yana mai roƙon a ci gaba da addu'o'i don samun zaɓe mai inganci cikin kwanciyar hankali da lumana.

"A wannan mawuyacin lokaci da za a gudanar da harkokin siyasa da zaɓe nan ba da jimawa ba a ƙasarmu, ina roƙon mu duka, mu ci gaba da yin addu'o'in samun zaman lafiya, musamman ga shugabanninmu a matakai daban-daban, akan Allah Ya ba su hikima kuma Ya daafa mu su wajen sauƙe nauyin dake kansu," in ji shi.

Gwamnan ya buƙaci shugabannin addinai, sarakuna da al'umma baki ɗaya su ƙara himma wajen inganta haɗin kai, haƙuri, da kuma zaman lafiya a tsakanin al'umma daban-daban, yana mai cewa irin waɗannan ɗabi'u suna da matuƙar muhimmanci ga ci gaba da ɗorewar zaman lafiya da kwanciyar hankali.

Ya bayyana matuƙar godiya ga al'ummar Jihar Gombe saboda goyon baya da haɗin kan da suke baiwa gwamnatinsa, yana mai ƙira garesu, su sabunta jajircewarsu ga ci gaban jihar baki ɗaya.

Gwamna Inuwa Yahaya ya tabbatarwa al'ummar jihar ci gaba da jajircewar gwamnatinsa na hamzarta samar da ci gaba a fannoni masu mahimmanci, yana mai alƙawarin ƙarfafa ribar da ake samu da kuma samar da wadata mai ɗorewa ga kowa.

Ya yi wa al'ummar Musulmi fatan alheri da gudanar da bukukuwan sallah cikin zaman lafiya da kwanciyar hankali.

Ismaila Uba Misilli
Babban Daraktan Yaɗa Labarun Gwamnan Jihar Gombe

20/03/2026

Hira na musamman tare da Professor Babayo Sule.
Akan lamarin siyasar mu ayau.

EID MUBARAK
20/03/2026

EID MUBARAK

Jadawalin tsaretsaren Hidiman bukukuwan sallah a jahar Gombe daga fadar maimartaba Sarkin Gombe (GIWA)
19/03/2026

Jadawalin tsaretsaren Hidiman bukukuwan sallah a jahar Gombe daga fadar maimartaba Sarkin Gombe (GIWA)

JAKADAN TUNISIYA YA KAI ZIYARAR BAN GIRMA GA JAMI’AR JIHAR GOMBE, YA NEMI ƘARFAFA HAƊIN KAI NA ILIMI DA AL’ADU19 ga Mari...
19/03/2026

JAKADAN TUNISIYA YA KAI ZIYARAR BAN GIRMA GA JAMI’AR JIHAR GOMBE, YA NEMI ƘARFAFA HAƊIN KAI NA ILIMI DA AL’ADU

19 ga Maris, 2026

Jakadan Jamhuriyar Tunisiya a Najeriya, wanda kuma shi ne jakada ga ƙasashen Ghana, Benin da Saliyo tare da zama a Najeriya, kuma wakilin Jamhuriyar Tunisiya a ECOWAS, Mai Girma Mohsen Antit, ya kai ziyarar ban girma ga Jami’ar Jihar Gombe, abin da ke nuna sabon yunƙuri na ƙarfafa haɗin gwiwar bangarorin biyu.

Ziyarar ta gudana ne tare da rakiyar Alhaji Ahmed Shaibu Gara da kuma Kwamishinan Kasuwanci, Masana’antu da Yawon Buɗe Ido, Hon. Nasiru Mohammed Aliyu.

Alhaji Gara ya gabatar da Jakadan ga shugabannin jami’ar, inda ya bayyana cewa manufar ziyarar ita ce gano hanyoyin haɗin gwiwa da za a iya aiwatarwa.

Jakadan ya bayyana farin cikinsa na kai ziyara Jami’ar Jihar Gombe tare da jaddada wasu muhimman fannoni na haɗin kai. A cewarsa, fannoni irin su ilimi, bunƙasa aikin gona, ci gaban bincike, da shirye-shiryen musayar al’adu na daga cikin abubuwan da ake sa ran za su ƙarfafa fahimtar juna da bunƙasa cibiyoyin.

Tawagar ta samu tarba daga Mataimakin Shugaban Jami’a (Vice Chancellor), Farfesa Sani Ahmed Yauta, tare da Rajistar Jami’a, Dr. Abubakar Aliyu Bafeto, Bursar, Alhaji Shehu Hassan, da sauran manyan ma’aikata.

A nasa jawabin, Mataimakin Shugaban Jami’ar ya tarbi jakadan da tawagarsa hannu biyu-biyu, inda ya bayyana ziyarar a matsayin wani muhimmin mataki na ƙara buɗe jami’ar ga duniya da faɗaɗa harkokin ilimi. Ya kuma gabatar da taƙaitaccen tarihin jami’ar, yadda ta bunƙasa, da nasarorin da ta samu a fannin ilimi, yana mai jaddada cewa jami’ar na da ƙudurin gina haɗin gwiwa da ƙasashen waje domin inganta koyarwa, bincike da kirkire-kirkire.

Farfesa Yauta ya kuma nuna godiya ga Gwamnan Jihar Gombe, Alhaji Muhammadu Inuwa Yahaya (CON), bisa ƙoƙarin gwamnatinsa wajen bunƙasa jami’ar da kuma tabbatar da ci gabanta.

19/03/2026

ZIYARAR GIRMAMAWA ZUWA GA MAI MARTABA, SARKIN GOMBE

Mai Martaba Sarkin Gombe ya karɓi bakuncin Mai Girma, Jakadan Jamhuriyar Tunisia, Mohsen Antit, cikin karamci. Jakadan yana Gombe ne domin halartar bukukuwan Eid-El-Fitr bisa gayyatar Mai Girma Gwamnan Jihar Gombe, Alhaji Muhammadu Inuwa Yahaya (Dan Majen Gombe).

Ran Sarki Ya Dade

Daga Abubakar A. Bello

Gwamnan Jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, ya buƙaci Musulmi da duk ’yan Najeriya su ci gaba da yin addu’a da kuma riƙ...
19/03/2026

Gwamnan Jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, ya buƙaci Musulmi da duk ’yan Najeriya su ci gaba da yin addu’a da kuma riƙe darusan da s**a koya a watan Ramadan yayin bikin ƙaramar Sallah.

Daga Aminiya

SHUGABA Bola Ahmed Tinubu YA TAYA MUSULMI MURNAR EID-EL-FITR, YA KIRA DA SABUNTA ƘISHIN ƘASAYayin da Musulmai a faɗin du...
19/03/2026

SHUGABA Bola Ahmed Tinubu YA TAYA MUSULMI MURNAR EID-EL-FITR, YA KIRA DA SABUNTA ƘISHIN ƘASA

Yayin da Musulmai a faɗin duniya ke bikin Eid-el-Fitr, wanda ke nuna ƙarshen watan Ramadan, Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya taya al’ummar Musulmi a Najeriya murna, tare da kira da a sabunta jajircewa ga ƙasa da kuma ɗan Adam.

A cikin wata sanarwa da Mai Bai Wa Shugaban Ƙasa Shawara na Musamman, Bayo Onaunuga ya fitar, an buƙaci Musulman Najeriya da su sake jajircewa wajen bin kyawawan koyarwar watan mai alfarma, waɗanda s**a haɗa da tsoron Allah, tausayi, da haɗin kai tsakanin al’umma.

Shugaba Tinubu ya kuma roƙi dukkan Musulmai da su miƙa hannun taimako ga masu buƙata ba tare da la’akari da addini ba, domin ƙara nuna haɗin kai da zumunci.

Sanarwar ta ƙara jaddada kira ga shugabannin Musulmi da su yi amfani da wannan dama wajen yin addu’o’i domin samun zaman lafiya da wadata a ƙasar.

Jakadan ƙasar Tunushiya a Najeriya ya ziyarci ƙaramar hukumar Gombe, Inda aka sanya masa kaya na Al'ada domin halartar S...
19/03/2026

Jakadan ƙasar Tunushiya a Najeriya ya ziyarci ƙaramar hukumar Gombe, Inda aka sanya masa kaya na Al'ada domin halartar Sallar IDI.

Maigirma Shugaban majalisar shuwagabannin ƙananan hukumomin jihar Gombe, Barr. Sani Ahmad Haruna, ya karɓi baƙuncin jakadan ƙasar Tunushiya Amb. Muhsin tare da rakiyar Kwamishinan kasuwanci da masana'antu Hon. Nasiru Muhammad da kuma Tsohon mai bawa gwamna shawari akan harkokin wasanni Alh. Ahmed Shuaibu Gara.

Inda aka tattauna muhimman batutuwa da zasu kawowa ƙaramar hukumar Gombe cigaba.

Address

Along GRA Road Behind Gombe State Government House
Gombe
760211

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when AREWA TALK TV posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share