Barewa Radio

Barewa Radio Welcome to Official page of Barewa Radio for News,Programs& Entertainment

Gwamnatin Jihar Kaduna Za Ta Fara Biyan Ma'aikata Mafi Karancin Albashi ₦72,000
19/09/2025

Gwamnatin Jihar Kaduna Za Ta Fara Biyan Ma'aikata Mafi Karancin Albashi ₦72,000

DA ƊUMI-ƊUMI: Kotun Sojan Najeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Ga Wani Soja Saboda Kisan Mai Adaidaita Sahu a BauchiBabbar Ko...
18/09/2025

DA ƊUMI-ƊUMI: Kotun Sojan Najeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Ga Wani Soja Saboda Kisan Mai Adaidaita Sahu a Bauchi

Babbar Kotun Sojin Najeriya da ke Barikin Maxwell Khobe Cantonment, Jos, ta yanke hukuncin kisa ta hanyar rataya ga Private Lukman Musa, bayan ya amsa laifin kashe wani mai adaidaita sahu, Malam Abdulrahman Isa, a garin Azere na Jihar Bauchi.

Rahotanni sun bayyana cewa, Lukman Musa ya aikata laifin ne kwanakin baya, kuma kotun ta tabbatar da cewa an karya dokar soji da kuma dokokin kasa.

Hukuncin ya biyo bayan amincewar wanda ake tuhuma da aikata kisan, lamarin da ya girgiza al’umma musamman a Bauchi da kewaye.

Hukumomi sun ce hukuncin na nuni da cewa rundunar sojin Najeriya ba za ta lamunci keta dokoki ko cin zarafin fararen hula ba.

Woooooooh, Fantastic finish, what a goal from Marcus Rashford!!!! 😱💥Newcastle 0-2 Barcelona Marcus Rashford ya zura ƙwal...
18/09/2025

Woooooooh, Fantastic finish, what a goal from Marcus Rashford!!!! 😱💥

Newcastle 0-2 Barcelona

Marcus Rashford ya zura ƙwallon sa ta farko a Barcelona, kuma ya ƙara ta biyu duka a rana ɗaya. 💥⚽⚽

70'

🏴󠁧󠁢󠁥󠁮󠁧󠁿 Manchester City 2-0 Napoli 🇮🇹
🏴󠁧󠁢󠁥󠁮󠁧󠁿 Newcastle United 0-2 Barcelona 🇪🇸
🇵🇹 Sporting Lisbon 4-0 Kairat Almaty 🇰🇿
🇩🇪 Eintracht Frankfurt 4-1 Galatasaray 🇹🇷

Kwallo nawa kuke hasashen Rashford zaici a wannan kakar?

14/09/2025

Yadda Atiku Abubakar ya Gwangwajen Buhari Sanusi Mahaddacin Alkur'anin da yazo na 3 a gasar da akayi a Saudiyya.

Rahotanni sun ce tukunyar da Hilda Baci ke girka shinkafar da ta fi kowacce yawa domin kafa tarihi ta karye a daren jiya...
13/09/2025

Rahotanni sun ce tukunyar da Hilda Baci ke girka shinkafar da ta fi kowacce yawa domin kafa tarihi ta karye a daren jiya a daidai lokacin da ake kokarin auna nauyin abincin.

Kasar Burkina Faso 🇧🇫 ta cire dukkanin shingayen visa ga 'yan kasashen Afirka.Yanzu dukkanin 'yan Afirka zuwa iya ziyart...
12/09/2025

Kasar Burkina Faso 🇧🇫 ta cire dukkanin shingayen visa ga 'yan kasashen Afirka.

Yanzu dukkanin 'yan Afirka zuwa iya ziyartar Kasar ta Burkina Faso kyauta.

Manya daga cikin shugabannin Hamas, ciki har da Osama Hamdan, sun halarci jana'izar wadanda s**a rasa rayukansu sanadiiy...
12/09/2025

Manya daga cikin shugabannin Hamas, ciki har da Osama Hamdan, sun halarci jana'izar wadanda s**a rasa rayukansu sanadiiyar harin da Isra'ila ta kai.

An gudanar da Janaizar ne a makabartar Mesaimeer dake Qatar. Wadanda s**a rasa rayukansu sun hada da Humam, ɗan mai jagorantar sasanci Khalil Al-Hayya, wanda Isra'ila ta yi kokarin kashe shi a harin da ta kai ranar Talata.

DA DUMI-DUMI: Gwamnatin Najeriya ta rage 5% na farashin Data da katin kira. Tsohon farashin Data 1GB Naira 268 gwamnatin...
12/09/2025

DA DUMI-DUMI: Gwamnatin Najeriya ta rage 5% na farashin Data da katin kira. Tsohon farashin Data 1GB Naira 268 gwamnatin Najeriya ta basu dama s**a kara 200% sai 1GB ya koma 800.

A yanzu sunce sun rage 5% daga 800 zata dawo Naira 760 akan kowane 1GB.

12/09/2025

Mutane sun taru cikin yanayin alhini a babban birnin Qatar, Doha, don yin addu’a ga mutane shida da s**a rasa rayukansu a harin Isra’ila, ciki har da wani jami'in 'yan sanda mai shekara 22.

An bayyana wannan harin a matsayin wanda ba a taba ganin irinsa ba a yankin Gulf.

Amincewar da INEC ta yi na shugabancin Mark ya yi dai-dai da tsarin doka — Jigon ADCWani jigo a jam’iyyar African Democr...
11/09/2025

Amincewar da INEC ta yi na shugabancin Mark ya yi dai-dai da tsarin doka — Jigon ADC

Wani jigo a jam’iyyar African Democratic Congress (ADC), Chille Igbawua, ya bayyana amincewar Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC) ta yi na shugabancin David Mark a matsayin “abinda ya dace da doka.”

Ya bayyana haka ne a cikin wata hira da aka yi da shi a shirin The Morning Brief na Channels Television a ranar Alhamis.

“Wannan tabbaci ne ga doka, tabbaci ne ga mulkin doka. Hakika, INEC ta yi abin da doka ta tanada a yi.

Shin ko kun san waɗanda sabuwar dokar haraji za ta shafa?A wata hira da aka yi da Shugaban kwamitin gyaran haraji, Mr Ta...
10/09/2025

Shin ko kun san waɗanda sabuwar dokar haraji za ta shafa?

A wata hira da aka yi da Shugaban kwamitin gyaran haraji, Mr Taiwo Oyedele a tashar Channels ranar Talata, 8 ga watan Satumba, ya bayyana cewa sama da kashi 97 na yan Najeriya ba za su biya haraji ba kwata-kwata, Mr Taiwo ya bayyana jerin wadanda biyan sabon harajin ba zai shafe su ba kamar haka

1. Masu karɓan mafi ƙarancin Albashi na 70k zuwa ƙasa

2. Waɗanda kuɗin shigarsu bai zarce dubu 100 ba a wata

3. Ƴan kasuwa masu jarin ƙasa da Naira Milyan 2

4. Kamfanoni da a da ake karɓan haraji a hannunsu duk da kadararsu ba ta haura milyan 25 ba, yanzu sai kadararsu ta kai Naira Milyan 100 sannan za su biya haraji

6 Waɗanda ke biyan tarin haraje- haraje ma ba a barsu a baya ba, domin daga sabuwar shekarar 2026 za su fara biyan haraji ɗaya tal , kuma mafi ƙaranci.

Ko ta yaya mutum zai gane cewa bai cancanci biyan haraji ba? Mr Oyedele ya ce tuni s**a tanadi hatimi a manhajar QR kan shafin yanar gizo na tsarin harajin, inda duk mai bukatar sanin matsayinsa zai je ya dauki hoton hatimin QR din ya zura sunansa da bayanin kudaden shigarsa don sanin ya dace ya biya haraji ko aa

Address

Biu Bye Pass
Gombe

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Barewa Radio posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Barewa Radio:

Share

Category