Barewa Radio

Barewa Radio Welcome to Official page of Barewa Radio for News,Programs& Entertainment

Gwamna Muhammad Inuwa Yahaya na jihar Gombe, ya ce yankin arewacin Nijeriya za ta mara wa shugaba Bola Tinubu a fafukars...
29/07/2025

Gwamna Muhammad Inuwa Yahaya na jihar Gombe, ya ce yankin arewacin Nijeriya za ta mara wa shugaba Bola Tinubu a fafukarsa ta neman tsayawa zaɓe a 2027.

Gwamnan ya bayyana haka ne a yau Talata a wani taron kwanaki biyu na shugabannin arewa da ake gudanarwa a jihar Kaduna domin duba irin ƙoƙarin da gwamnatin Tinubu ta yi, musamman kan abin da ya shafi walwalar ƴan yankin.

Ya ce goyon baya da aka bai wa Tinubu a zaɓen 2023 ya fara haifar da ɗa mai ido a ɓangarorin ayyukan more rayuwa da tsaro da noma da kuma mak**ashi.

Taron wanda gidauniyar Sir Ahmadu Bello ta shirya, ta samu halartar gwamnan jihar Kaduna Uba Sani, gwamnan Gombe Inuwa Yahaya, sakataren gwamnatin tarayya, Sanata George Akume, mai bai wa shugaban ƙasa shawara kan harkar tsaro Nuhu Ribadu, tsoffin gwamnoni, ministoci, hafsoshin tsaro da kuma sauran ƴansiyasa daga yankin arewa.

Injiniya Aliyu Mohammed (Kombat), ɗan takarar gwamna kuma babban jigo a jam’iyyar All Progressives Congress (APC) a Jiha...
29/07/2025

Injiniya Aliyu Mohammed (Kombat), ɗan takarar gwamna kuma babban jigo a jam’iyyar All Progressives Congress (APC) a Jihar Gombe, ya sanar da janyewarsa daga tsayawa takara a kowanne matsayi na zaɓe a zaɓen 2027.

Wannan mataki ya fito ne a cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Litinin, inda ya bayyana cewa ya yanke wannan shawara ne bayan zurfin tunani da kuma tattaunawa da iyalansa, masu ba shi shawara, dattawa, da abokan siyasa.

Kombat ya bayyana cewa yana fahimtar yadda wannan mataki zai iya bata ran magoya bayansa, amma ya jaddada cewa ya yanke shi ne da niyyar alheri da kuma la’akari da muhimman abubuwan da ke gabansa a halin yanzu. Ya ce, “Ba zan tsaya takara ba a zaɓen 2027. Wannan shawara ba ta zo da sauƙi ba, ina neman fahimtar ku da addu’o’inku.

28/07/2025

Kanun labaran yau Litinin 28/7/2025.

HUKUMAR HISBAH A GARIN AZARE SUNKAMA MATA DASUKE ZUWA HOTEL HOTEL A FEDERAL LOW COST!Ayaune Hukumar Hisbah Shiyar Katagu...
27/07/2025

HUKUMAR HISBAH A GARIN AZARE SUNKAMA MATA DASUKE ZUWA HOTEL HOTEL A FEDERAL LOW COST!

Ayaune Hukumar Hisbah Shiyar Katagum S**a Kai Sumame Tareda Chafke Wayannan Gungun Yan Matan
Dake Zuwa Hotel Hotel A Federal Low Cost.

Wanda Kuma Zakuji Daga Bakin Shugaban Hukumar Ta Hisbah Malam Rilwanu Kairan Yabada Jawabi Yanda Abun Ya Kasance.

Kuma Zamu sake Vedion don Kuji yanda Takaya

📸Serbia Boy

Da dumi'dumi: Gwamna Abba Ya Bada Umarnin Bincike Kan Kwamishanan Sufuri Da Ake Zargi da karɓar belin dilan muggan kwayo...
26/07/2025

Da dumi'dumi: Gwamna Abba Ya Bada Umarnin Bincike Kan Kwamishanan Sufuri Da Ake Zargi da karɓar belin dilan muggan kwayoyi

Gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya bayar da umarnin gudanar da cikakken bincike kan zargin saka hannun kwamishinan sufuri na jihar, Alhaji Ibrahim Namadi, kan badakalar belin wani da ake zargi da sayar da miyagun kwayoyi, Sulaiman Aminu Dan Wawu.

Umurnin ya biyo bayan cece-ku-ce da jama’a s**a yi bayan da rahotanni s**a bayyana cewa sunan Kwamishinan ya bayyana a cikin takardun hukuma da ke taimaka wajen sakin wanda ake zargin.

An bayyana hakan ne a wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sanusi Bature Dawakin Tofa ya fitar ranar Asabar.

Domin shawo kan lamarin Gwamna Yusuf ya kafa kwamitin bincike na musamman karkashin jagorancin Barista Aminu Hussain, mai ba shi shawara na musamman kan harkokin shari’a da tsarin mulki.

An wajabta wa kwamitin da ya bayyana al'amuran da ke tattare da lamarin tare da ba da shawarar matakan da s**a dace da gaggawa.

Mambobin kwamitin sun hada da:

1. Barr. Aminu Hussaini, Chairman

2. Barr. Hamza Haladu, Member

3. Barr. Hamza Nuhu Dantani, Member

4. Alhaji Abdullahi Mahmoud Umar, Member

5. Maj. Gen. Sani Muhammad (Rtd.), Memba

6. Comrade Kabiru Said Dakata, Memba

7. Hajiya Bilkisu Maimota – Sakatariya

A lokacin da yake sanar da kafa kwamitin, Gwamna Yusuf ya nuna matukar damuwarsa kan rashin da’a da ake zarginsa da aikatawa, inda ya jaddada kudirin gwamnatinsa na yaki da shaye-shayen miyagun kwayoyi da duk wani nau’i na munanan ayyuka a jihar.

Labari cikin Hutuna: Yadda ake gudanar da taron jin ra’ayin jama’a game da shirin yi wa kundin tsarin mulki kwaskwarima ...
26/07/2025

Labari cikin Hutuna:

Yadda ake gudanar da taron jin ra’ayin jama’a game da shirin yi wa kundin tsarin mulki kwaskwarima na yankin Arewa maso Yamma wanda Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa Barau Jibrin ke jagoranta a Kano.

Yadda Dan Bello da Abba Hikima da Sharfaddeen Bature s**a kashe Miliyan 3 wajen gyara wani ajin sakandari a arewacin Naj...
26/07/2025

Yadda Dan Bello da Abba Hikima da Sharfaddeen Bature s**a kashe Miliyan 3 wajen gyara wani ajin sakandari a arewacin Najeriya.

📷Dan Bello

Bello Turji ya shiga gudun ɓuya bayan da sojoji s**a yi alƙawari sau takwas cewa za su kamo shi da ransa ko a mace, kuma...
26/07/2025

Bello Turji ya shiga gudun ɓuya bayan da sojoji s**a yi alƙawari sau takwas cewa za su kamo shi da ransa ko a mace, kuma s**a hallaka manyan jagororin ’yan bindiga.

26/07/2025

G-Fresh ya bayyana dalilin dayasa aka turashi gidan Yari 👇

Da dumi'dumi: Sa'o'i kadan bayan ganawa da tsohon gwamnan jihar Neja, Babangida Aliyu a gidansa da ke Abuja, Peter Obi y...
25/07/2025

Da dumi'dumi: Sa'o'i kadan bayan ganawa da tsohon gwamnan jihar Neja, Babangida Aliyu a gidansa da ke Abuja, Peter Obi ya sake ganawa da tsohon gwamnan jihar Kaduna kuma jigo a jam'iyyar SDP, Nasir El-Rufai a gidansa da ke Abuja.

A yau ne dai aka yi ta rade-radin cewa wasu jiga-jigan jam’iyyar PDP na kokarin dawo da Peter Obi jam’iyyar PDP domin ya zama dan takarar shugaban kasa a zaben 2027.

Yadda EFCC ta k**a G-Fresh da Laifin  wasa da Naira.Saidai mutane dayawa na korafin cewa k**ar ancire masa Filter 🤔Miye ...
25/07/2025

Yadda EFCC ta k**a G-Fresh da Laifin wasa da Naira.

Saidai mutane dayawa na korafin cewa k**ar ancire masa Filter 🤔

Miye ra'ayinku kusa ma a comment 👇

Gwamnan jihar Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf kenan yanzu haka a masallacin juma’a na Marigayi Alhaji Nasiru Ahli yayin hal...
25/07/2025

Gwamnan jihar Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf kenan yanzu haka a masallacin juma’a na Marigayi Alhaji Nasiru Ahli yayin halartar Daurin Auren Nadiya Ibrahim Fagge.

📸Salisu Mohammed kosawa

Address

Biu Bye Pass
Gombe

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Barewa Radio posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Barewa Radio:

Share

Category