
05/07/2025
An gudanarda Zikirin Juma'a da Addu'o'in neman zaman lafiya ga ƙasa a Zawuyyar Jajjaye Kaura Namoda jahar Zamfara.
Daga Yahaya Mahi Na Malam Babba.
Da yammacin yau juma'a ne Zawuyyar Unguwar Jajjaye dake cikin karamar hukumar mulkin kaura Namoda jahar Zamfara ta Gudanarda taronta da ta sabayi duk shekara domin Gudanarda Zikirin juma'a tare da yiwa kasa Addu'a Akan matsalolinda s**a addabi Al'umma na tsadar rayuwa da Kuma neman zaman lafiya a yankin da kuma ƙasa baki ɗaya.
Kamar yanda s**a saba duk shekara suna haduwa a juma'ar farkon kowace shekarar Musulunci domin gabatarda wannan ibada.
A nasu jawabai bayan kammala Zikirin Khalifa Malam Abubakar Atiku Maisuna na Malam Babba, Sheikh Malam Muhammad na Malam Rabi'u gangaren Makaranta, Khalifa Malam Nasiru Sheikh Ibrahim ƙara, Khalifa Malam Kabiru Usman da Sharif Sidi Abba Sunyi Kira ga Samarin Tijjanawa da Ƙadirawa da su kasance Masu ladabi da biyayya da Kuma jin maganganun Maganata aduk inda s**a samu kawunansu, sannan su saka neman ilmin Addini dana zamani a gaba domin sai da ilimi ake samun Kowane kalar ci gaban rayuwa.
Taron dai ya samu halartar Dukkanin Khalifofi, mukaddimai, muridai da zakirai 'yan Darikar Tijjaniyya na garin kaura da kewaye da Kuma wasu daga cikin Malaman Darikar kadiriyya na kaura inda kowannensu yayi Addu'o'in Samun Dawwamammen Zaman lafiya a kaura Namoda jahar Zamfara da Najeriya Baki daya.
Da suke jawabin Godia ga Dukkanin Mahalarta taron Alhaji Tijjani Umar Mai kabit, Kumandan agajin Fitiyanul Islam Malam Balan Bala, Alh Abbas kilomiya, Kabiru na A'i. Sunyi godiya ga dukkanin mahalarta da fatan Allah ya maida kowa gidansa lafiya, sun ƙara da cewar wannan shine Karo na (16) ana Gudanarda wannan Zikiri aduk shekara.
Haka Kuma Dattibai da Samarin unguwar ke daukar dawainiyar taron duk shekara .