Al'umma Tv

Al'umma Tv Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Al'umma Tv, Media/News Company, Gombe.

Kafar watsa labarai ta Al'umma Tv ta himmatu wajen baku damar faɗin albarkacin bakinku k**ar yadda taken mu shine "Labaran Ku, Gaskiyar Mu" zaku iya tuntubar mu a 07015067942.

An gudanarda Zikirin Juma'a da Addu'o'in neman zaman lafiya ga ƙasa a Zawuyyar Jajjaye Kaura Namoda jahar Zamfara.Daga Y...
05/07/2025

An gudanarda Zikirin Juma'a da Addu'o'in neman zaman lafiya ga ƙasa a Zawuyyar Jajjaye Kaura Namoda jahar Zamfara.

Daga Yahaya Mahi Na Malam Babba.

Da yammacin yau juma'a ne Zawuyyar Unguwar Jajjaye dake cikin karamar hukumar mulkin kaura Namoda jahar Zamfara ta Gudanarda taronta da ta sabayi duk shekara domin Gudanarda Zikirin juma'a tare da yiwa kasa Addu'a Akan matsalolinda s**a addabi Al'umma na tsadar rayuwa da Kuma neman zaman lafiya a yankin da kuma ƙasa baki ɗaya.

Kamar yanda s**a saba duk shekara suna haduwa a juma'ar farkon kowace shekarar Musulunci domin gabatarda wannan ibada.

A nasu jawabai bayan kammala Zikirin Khalifa Malam Abubakar Atiku Maisuna na Malam Babba, Sheikh Malam Muhammad na Malam Rabi'u gangaren Makaranta, Khalifa Malam Nasiru Sheikh Ibrahim ƙara, Khalifa Malam Kabiru Usman da Sharif Sidi Abba Sunyi Kira ga Samarin Tijjanawa da Ƙadirawa da su kasance Masu ladabi da biyayya da Kuma jin maganganun Maganata aduk inda s**a samu kawunansu, sannan su saka neman ilmin Addini dana zamani a gaba domin sai da ilimi ake samun Kowane kalar ci gaban rayuwa.

Taron dai ya samu halartar Dukkanin Khalifofi, mukaddimai, muridai da zakirai 'yan Darikar Tijjaniyya na garin kaura da kewaye da Kuma wasu daga cikin Malaman Darikar kadiriyya na kaura inda kowannensu yayi Addu'o'in Samun Dawwamammen Zaman lafiya a kaura Namoda jahar Zamfara da Najeriya Baki daya.

Da suke jawabin Godia ga Dukkanin Mahalarta taron Alhaji Tijjani Umar Mai kabit, Kumandan agajin Fitiyanul Islam Malam Balan Bala, Alh Abbas kilomiya, Kabiru na A'i. Sunyi godiya ga dukkanin mahalarta da fatan Allah ya maida kowa gidansa lafiya, sun ƙara da cewar wannan shine Karo na (16) ana Gudanarda wannan Zikiri aduk shekara.

Haka Kuma Dattibai da Samarin unguwar ke daukar dawainiyar taron duk shekara .

Mai-ɗakin shugaban ƙasa Olu Remi Tinubu ta bada tallafin Naira biliyan 1 ga waɗanda harin Plateau ya shafa kuma ta ce ku...
03/07/2025

Mai-ɗakin shugaban ƙasa Olu Remi Tinubu ta bada tallafin Naira biliyan 1 ga waɗanda harin Plateau ya shafa kuma ta ce kuɗin ta ne ba na gwamnati ba

Uwargidan shugaban kasa, Sanata Remi Tinubu, ta bayar da tallafin Naira biliyan ɗaya (₦1bn) ga waɗanda s**a tsira daga hare-haren baya-bayan nan da aka kai a wasu sassan Jihar Filato.

Uwargidan shugaban kasar ta bayyana wannan tallafi ne a lokacin ziyarar ta’aziyya da ta kai jihar a ranar Alhamis, inda ta bayyana cewa kudin da ta bayar ba na gwamnati ba ne, amma ta tattara shi da kanta domin taimakon jama’a.

“Yau na zo da tallafin Naira biliyan ɗaya ga shirin Renewed Hope Initiative. Ban mallaki dukiya mai yawa ba.

“Idan na ajiye kudi domin biyan buƙatar kaina, hakan zai zama don kwaɗayi kawai. Amma burina shi ne amfani da abin da nake da shi domin alheri, don cigaban wannan ƙasa, ba wai asarar shi ba.

“Don Allah ku fahimci cewa kudin wannan shirin ba kudin gwamnati ba ne. Kudin da na tara da kaina ne domin taimakon wasu. Yayin da nake ci gaba da yin tafiye-tafiye da kuma ganin tasirin aikinmu, ina neman addu’o’inku yayin da muke ƙoƙarin kawo sauyi mai dorewa.

“Na dade ina addu’a musamman ga wadanda ambaliyar ruwa ta shafa a wasu wurare. Na yi addu’ar cewa ruwan sama zai zamo albarka wajen fidda amfanin gona ba lalata shi ba. Allah ya riga ya amsa addu’o’inmu, kuma za mu kai ziyara wasu wuraren da ke bukatar tallafi k**ar Benue da Neja.

“A ƙarshe, ina roƙon shugabannin gargajiya a nan. Ku ne masu kula da wannan ƙasa. Mu masu rike muk**ai za mu zo mu wuce, amma ku za ku kasance. Don Allah ina roƙonku ku kawo zaman lafiya a wannan ƙasa. Allah zai taimake ku wajen kiyaye da kuma kula da wannan ƙasa. Ina addu’a Allah ya sanya Jihar Filato ta bunƙasa, Najeriya ta girma cikin zaman lafiya da haɗin kai.”

Wasu daga cikin fuskokin manyan jiga-jigai na sabuwar hadakar jam’iyyar ADC. Wanne fata za ku yi musu?
03/07/2025

Wasu daga cikin fuskokin manyan jiga-jigai na sabuwar hadakar jam’iyyar ADC.

Wanne fata za ku yi musu?

YANZU-YANZU: Mataimakin shugaban ƙasa, Kashim Shettima ya isa gidan marigayi Alhaji Aminu Alhassan Dantata da ke unguwar...
03/07/2025

YANZU-YANZU: Mataimakin shugaban ƙasa, Kashim Shettima ya isa gidan marigayi Alhaji Aminu Alhassan Dantata da ke unguwar Ƙoƙi a birnin Kano don ta'aziyyar rasuwar sa.

Gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf ne da wasu jagororin siyasar jihar Kano s**a tarbi Shettima a filin jirgin sama na Malam Aminu Kano, sannan ya raka shi zuwa gidan gaisuwar.

Gwamnatin Tarayya ta kaddamar da cibiyar Fasahar Sadarwa ta Zamani (Digital Industrial Park) a Jihar Kano, wacce aka ƙon...
03/07/2025

Gwamnatin Tarayya ta kaddamar da cibiyar Fasahar Sadarwa ta Zamani (Digital Industrial Park) a Jihar Kano, wacce aka ƙone ta yayin zanga-zangar matsin rayuwa a ranar 1 ga watan Agusta 2024.

Ministan Sadarwa da Fasaha, Dr. Bosun Tijani, wanda ya ƙaddamar da cibiyar a madadin shugaban kasa, ya yabawa kamfanin IHS Nigeria saboda gaggauta sake gina cibiyar ba tare da amfani da kudin gwamnati ba.

A cewar Tijani, an kafa cibiyar ne domin baiwa matasa damar koyon fasahar zamani don taimaka wa rayuwarsu.

Ministan ya ce lalata cibiyar, lokacin da ake da da buɗe ta a bara, abun takaici ne, inda ya ƙara da cewa "amma takaicin bai kashe mana gwiwa ba har sai da mu ka sake gina ta."

A nasa ɓangaren, Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf, ya ce cibiyar alama ce ta jajircewar jihar wajen tallafa wa matasa da bunkasa tattalin arzikin su.

Gwamnan wanda ya samu wakilcin mataimakinsa , Aminu Abdussalam Gwarzo ya ce tun shigowarsa Gwamnati a 2023, jihar ta mayar da hankali kan shirye-shiryen da zasu tallafawa matasa a fannin sadarwa.

Hukumar NCC, ta bakin shugaban ta na ƙasa, Dr Aminu Mai ta bayyana cewa an kafa irin wannan cibiyar a Borno, Ogun da Enugu domin samar da sabbin masu fasaha a Najeriya.

Maida ya ce irin waɗannan cibiyoyin za su yi amfani wajen bincike da bunkasa ilimin fasaha don bukatar tattalin arzikin ƙasa.

DA DUMI DUMINSA: Rundunar 'yan sandan jihar Gombe karkashin jagorancin CP Bello Yahaya psc(+) na tayi nasarar k**a wani ...
02/07/2025

DA DUMI DUMINSA: Rundunar 'yan sandan jihar Gombe karkashin jagorancin CP Bello Yahaya psc(+) na tayi nasarar k**a wani mutum bisa zargi na hada baki da kuma mallakar kudin jabu.

A ranar 28/06/2025, da misalin karfe 1404 na safe, jami’an ‘yan sanda da ke aiki da sashin filin jirgin saman Lawanti a lokacin da suke sa-ido s**a k**a wani mutum mai suna Usman Kawu “M” mai shekaru 35 a kauyen Kuji Kwadon, karamar hukumar Yamaltu-Deba, jihar Gombe.

An samu wanda ake zargin da laifin jabun kudaden dalar Amurka, wanda ya yi yunkurin yin amfani da su wajen yaudarar jama’ar da ba su ji ba gani. Binciken farko da aka gudanar ya nuna cewa yana rike da wasu kudade guda goma (10) na kudi dala dari daya da ake zargin na bogi ne. A cikin kudin gida kuwa, adadin ya kai ₦1,500,000 (Naira miliyan daya da dubu dari biyar). Ya kuma mallaki ₦10,000 (Naira Dubu Goma) a kudin Najeriya, duk an boye a cikin gajeren wandonsa na ciki, aka gano a matsayin baje koli.

A yayin hirar, wanda ake zargin ya amsa laifinsa amma ya yi zargin cewa an ba shi kudin jabun ne domin yin kasuwanci.

Kazalika, hukumar na ci gaba da kokarin ta waje damke wanda aka ce mai laifinne tare da yin wasu abubuwan baje koli. Ana ci gaba da gudanar da bincike.

Rundunar ‘yan sandan jihar Gombe na ci gaba da jajircewa wajen tabbatar da tsaron lafiyar al’ummar jihar Gombe. Za a sanar da ƙarin abubuwan ci gaba a lokacin da ya dace.

Dan gwagwarmayar kare hakkin dan Adam kuma dan takarar shugaban kasa karkashin jam’iyyar AAC a zaben 2023, Omoyele Sowor...
02/07/2025

Dan gwagwarmayar kare hakkin dan Adam kuma dan takarar shugaban kasa karkashin jam’iyyar AAC a zaben 2023, Omoyele Sowore, ya bayyana cewa ba zai taba shiga cikin hadakar ’yan adawan da ke neman kifar da jam’iyyar APC mai mulki a zaben 2027 ba.

A wata sanarwa da ya fitar a ranar Talata, Sowore ya ce ba zai iya hada kai da wasu fitattun ’yan siyasa da ya zarga da rusa Najeriya ta hanyar cin hanci da rashawa, cin amanar kasa da zalunci ba.

“Ban taba hada kai da Bola Ahmed Tinubu wajen rarraba hodar iblis a birnin Chicago ba,” in ji Sowore.

“Ban hada kai da Atiku Abubakar wajen wawure dukiyar Hukumar Kwastam ba. Ban taba shiga cikin barnar David Mark wanda ya saci kudaden da aka ware don gyara wayoyinmu sannan ya taimaka wajen murkushe burin dimokuradiyyarmu a ranar 12 ga Yuni ba.”

A cikin wannan s**a mai zafi ga tsarin siyasar Najeriya, Sowore ya jero wasu daga cikin manyan ’yan siyasa da ya ce sun taka rawa wajen lalata kasar, ciki har da tsofaffin gwamnoni, ministoci da ‘yan takarar shugaban kasa.

Sowore ya ki amincewa da kira da ake yi masa da ya sassauta tsayuwarsa kan akida saboda bukatar siyasa, yana mai cewa:
“Ban taba shiga cikin kungiyoyin ’yan fashi da makami ba. Ban taba rantsuwa da wata kungiya ko tsari na sirri — ko da kuwa suna da farin jini, iko ko ban sha’awa — ba.”

Daga Jarida: Daily Nigerian Hausa

Al'ummar unguwan Rimi Quarter Dake Kan Hanyar ratse Na Bypass sun koka Kan yadda Sabon hanyar Da Wanda ya tawo Daga Tsoh...
02/07/2025

Al'ummar unguwan Rimi Quarter Dake Kan Hanyar ratse Na Bypass sun koka Kan yadda Sabon hanyar Da Wanda ya tawo Daga Tsohon tashan Bauchi zuwa bypass

Sun koka Kan yadda aikin hannya Ake Neman Jaffa sa musu kwari a Unguwan Da din bin Al Umma Da Dama

Da muke zantawa Da wasu mazauna unguwan sun bayyana irin kukarin Mai Girma Gwamnan Jahar Gombe Alh Muhammad Inuwa inda suke Kira Da a kawo musu dauki Kan wannan kwari Dake cinye Gidaje Da Kuma yin barazana ga rayuwan Al Umma.

Umar Ahmad, Aliyu Haruna Da muhammad Mai medicated sunyi Kira Da mahukunta Da su gaggauta kawo musu dauki.

Wata Daga cikin Wanda gidanta ya rushe Saka makon wannan kwari Naomi' ta bayyana Yanda suke Zaman Dar Dar Sak**a Kon barazana Da Ruwan Ke musu

Tsohon Shugaban Kasa Muhammadu Buhari na fama da rashin lafiya, kuma rahotanni sun ce kwanan nan aka sallame shi daga da...
02/07/2025

Tsohon Shugaban Kasa Muhammadu Buhari na fama da rashin lafiya, kuma rahotanni sun ce kwanan nan aka sallame shi daga dakin kula da masu matsananciyar rashin lafiya (ICU) a wani asibiti da ke Landan a kasar Birtaniya.

Jaridar TheCable ta rawaito daga Empowered Newswire, wani makusancin tsohon shugaban ya bayyana cewa Buhari ya kamu da rashin lafiya ne a Landan yayin da ya je don duba lafiyarsa.

Rahoton ya ce an kwantar da Buhari a dakin ICU, amma daga bisani aka sallame shi makon da ya gabata.

Ko da ya ke ba a bayyana irin cutar da ke damunsa ba, rahotanni sun nuna cewa yana samun sauki a Landan, kuma ana sa ran zai dawo Najeriya da zarar ya warke gaba ɗaya.

Empowered Newswire ta kara da cewa, bisa bayanan da s**a samu daga wasu majiyoyi masu tushe, Mamman Daura – kawun Buhari kuma amintaccensa – shima yana samun sauki daga rashin lafiya a kasar Birtaniya.

Buhari bai halarci bikin cika shekaru 50 da kafuwar Kungiyar raya Tattalin Arzikin Kasashen Yammacin Afrika (ECOWAS) da aka gudanar a Legas ranar 28 ga Mayu ba.

A wata wasika da ya aika wa Shugaba Bola Tinubu, Buhari ya bayyana cewa rashin halartar sa taron ya samo asali ne daga tafiyarsa ta duba lafiya a Birtaniya.

Gamayyar Jagororin Siyasa a Najeriya Sun Kafa Sabuwar Hadaka Ta ADC Don Kalubalantar Bola Tinubu a 2027Jiga-jigan jam’iy...
02/07/2025

Gamayyar Jagororin Siyasa a Najeriya Sun Kafa Sabuwar Hadaka Ta ADC Don Kalubalantar Bola Tinubu a 2027

Jiga-jigan jam’iyyun adawa a Najeriya sun jingine ADA da SDP, sun kuma ayyana African Democratic Congress (ADC) a matsayin sabuwar jam’iyyar hadaka da za su yi amfani da ita wajen kalubalantar Shugaba Bola Ahmed Tinubu a zaben 2027 mai zuwa.

An nada Sanata David Mark a matsayin shugaban rikon kwarya, yayin da tsohon Gwamnan Osun, Ogbeni Rauf Aregbesola, ya zama Sakataren jam’iyyar.

Wannan mataki na nuna yadda ‘yan adawa ke kokarin hada kai domin karfafa gwiwa da samun nasara a babban zaben da ke tafe.

Shin kuna ganin wannan sabuwar hadaka zata iya samun nasara a Zaben 2027?

Wani asibitin mai suna Best Choice ya yi ragin kaso 50 na kuɗaɗen ayyukansu na yau da kullum, wanda s**a haɗa da kudin g...
01/07/2025

Wani asibitin mai suna Best Choice ya yi ragin kaso 50 na kuɗaɗen ayyukansu na yau da kullum, wanda s**a haɗa da kudin ganin likita kudin Gado da sauran ayyukan su, shi kuma bude Fayal ya zama kyauta ne yanzu haka.

Hakan na kunshe ne Cikin wata tattaunawa da shugaban asibitin Alh Auwal Muhd Lawal yayi da Jaridar Alfijir Labarai a yau Talata.

Lawal yace bayan korafe-korafe da kiraye-kirayen da jama a suke ta yiwa asibitin hukumar gudanarwar sun yi kwakkwaran bincike har s**a gano yadda wasu suke kasa zama har lokacin da ya dace likita ya sallamesu yayi suke tafiya, sannan wasu kuma tun daga bude fayil suke kasawa duk da yadda suke kaunar zuwa asibitin, wannan dalilin ne yasa s**a ɗauki wannan matakin domin farantawa al’umma duk da irin kuɗaɗen da suke kashewa ga tsadar komai ga kuma yadda ake bawa asibitin cikakkiyar kulawa.

A baya muna buɗe fayil na mutum daya akan dubu 20, shi kuma na iyali dubu 40 yanzu haka ya koma kyauta.

Shi kuma ganin likita dubu 10 ne, amma yanzu ya koma dubu 5. Kudin gado dubu 70 ne, amma yanzu mun mai dashi dubu 35 babban dakin, akwai na dubu 50, ya koma dubu 25, dakin dubu 25, ya koma dubu 12,500, sai ɓangaren masu awo shine daga dubu 150,000 ya koma dubu 80, haihuwa itama daga dubu 150,000 ta koma dubu 80, sai CS daga dubu dari 6, ya dawo dubu dari 3, haka sauran gwaje-gwajen ma duk suma haka zasu koma domin a kara kyautatawa al’umma, Allah ya kare mu da lafiya baki daya ameen.

A karshe a madadina da iyalaina da maaikatana Muna mika ta’aziyyarmu ga iyalan Marigayi Alh Aminu Dantata da gwamnatin Kano da al’ummar Kano da Afrika baki ɗaya.

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour Party a zaben 2023, Peter Obi, ya tabbatar wa magoya bayansa cewa zai tsay...
01/07/2025

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour Party a zaben 2023, Peter Obi, ya tabbatar wa magoya bayansa cewa zai tsaya takarar shugaban kasa a zaben shekarar 2027, kuma ba zai yi fiye da wa’adi guda ba idan ya ci zabe.

Mista Obi ya bayyana hakan ne a cikin wata sanarwa da mai magana da yawun Peter Obi Media Reports, Ibrahim Umar, ya fitar a ranar Litinin a Abuja.

Jaridar Daily Nigerian Hausa ta ruwaito cewar Tsohon dan takarar shugaban kasar ya tabbatar da cewa yana cikin tattaunawar kafa kawancen jam’iyyu, yana mai cewa burinsa shi ne ceton Najeriya daga halin da ta tsinci kanta.

“Ban taba shiga wata tattaunawa kan hadin gwiwar tikitin takara da kowa ba, har da Atiku,” inji shi.

“Idan za a samu wata yarjejeniya da za ta takaita wa’adin mulkina zuwa shekaru hudu, zan yarda da ita, kuma zan bar ofis ranar 28 ga Mayu, 2031.

“Idan kawancen ba ya magana ne kan dakatar da kashe-kashen da ake yi a Benue da Zamfara, dawo da tattalin arzikinmu, farfado da masana’antunmu, da ciyar da ‘yan Najeriya, to ku cire ni a ciki,” inji shi.

Obi ya yi alkawarin kawo kwanciyar hankali a kasar nan cikin shekaru biyu da fara mulkinsa.

Dangane da halin da jam’iyyar Labour Party ke ciki, Obi ya ce suna aiki tukuru domin samun sahalewar INEC ga shugabancin Nenadi Usman bisa hukuncin Kotun Koli.

Address

Gombe

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Al'umma Tv posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share