Al'umma Tv

Al'umma Tv Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Al'umma Tv, Media/News Company, Gombe.

Kafar watsa labarai ta Al'umma Tv ta himmatu wajen baku damar faɗin albarkacin bakinku kamar yadda taken mu shine "Labaran Ku, Gaskiyar Mu" zaku iya tuntubar mu a 07015067942.

Mataimakin shugaban ƙaramar hukumar Akko, Hon. Habib Hassan Kumo (Gatan Akko), ya kaddamar da rabon kayan abinci ga al’u...
26/08/2025

Mataimakin shugaban ƙaramar hukumar Akko, Hon. Habib Hassan Kumo (Gatan Akko), ya kaddamar da rabon kayan abinci ga al’ummar ƙaramar hukumar Akko.

Taron kaddamarwar, wanda aka fara da mutanen da ke da buƙata ta musamman, ya gudana ne a ranar Litinin a garin Kumo, hedkwatar ƙaramar hukumar Akko.

Da yake jawabi, Hon. Habib Hassan Kumo ya bayyana godiyarsa ga samun damar tallafawa al’ummar sa, tare da jaddada cewa wannan ba shi ne karon farko da ake raba irin wannan kayan tallafi ba.

A nasu tsokaci, Alhaji Muhammad Seyoji, Galadiman Akko, da kuma Alhaji Marka, shugaban jam’iyyar APC a Akko, sun yaba da wannan mataki. Sun kuma yi kira ga sauran jagororin siyasa a yankin da su yi koyi da shi wajen tallafawa jama’a.

Shi ma Acrt. Usman Muhammad, wanda ke zama ko’odinetan hukumar raya shiyyar Arewa maso Gabas a Gombe, ya yi kira ga waɗanda s**a ci gajiyar tallafin da su yi amfani da shi yadda ya dace domin amfaninsu da na iyalansu.

Wasu daga cikin waɗanda s**a amfana da tallafin sun nuna farin ciki da godiya ga Mataimakin shugaban ƙaramar hukumar Akko bisa wannan taimako, inda s**a ce hakan zai rage musu ɗaura da talauci tare da inganta rayuwar yau da kullum.

Yau ce ranar Hausa ta Duniya, wace Karin magana ka sani na hausawa?
26/08/2025

Yau ce ranar Hausa ta Duniya, wace Karin magana ka sani na hausawa?

DA DUMI-DUMI: Gidauniyar Sheikh Professor Isa Ali Pantami  za ta kaddamar da shirin horar da gyaran waya karo na uku dom...
25/08/2025

DA DUMI-DUMI: Gidauniyar Sheikh Professor Isa Ali Pantami za ta kaddamar da shirin horar da gyaran waya karo na uku domin taimakawa matasa sama da dubu 10,000.

Gidauniyar Farfesa Isa Pantami ta yi farin cikin sanar da kaddamar da shirinta na horaswa karo na uku, inda za ta mayar da hankali a wannan karon kan koyar da gyaran waya.

An tsara wannan shiri ne domin karfafawa sama da mutane 10,000 da za su ci gajiyar tallafin, wadanda za'a dauki su daki-daki, daga lungu da sako na fadin jihar Gombe da ma fadin Najeriya, tare da dabarun samar da kudaden shiga da za su iya dogaro da kai da kasuwanci.

Ga Portal din https://professorisapantamifoundation.com.ng/ domin matasa da suke bukata suyi Apply, inda za'a rufe Portal din a ranar Lahadi, 31 ga wannan watan Agusta 2025, ana karfafawa matasa guiwa da suyi Apply da wuri.

Gidauniyar Professor Isa Ali Pantami Foundation ta gudanar da wasu muhimman ayyuka kamar haka;

- An biyawa dalibai kyautar tallafin karatu na JAMB su 1,300.

- An kashe fiye da Naira miliyan 18 a tallafin karatu ga wasu daliban jihar Gombe masu karamin karfi.

- An kashe sama da Naira miliyan 170 a rabon tallafin hidimar babbar Sallah.

- Rabo-rabon tallafin abincin Ramadan.

- Ziyarar asibitoti da tallafi na musamman ga majinyata.

- Da sauran manyan ayyukan taimako na boye da zahiri masu yawan gaske.

Wa yan nan suna daga cikin kokarin da Gidauniyar ta gudanar ga al'ummar jihar Gombe da Najeriya.

Kwalejin Kimiyya da Fasaha ta Tarayya dake Bali, Jihar Taraba, ta bayyana cewa ta karɓi aikace-aikace fiye da 4,489 daga...
24/08/2025

Kwalejin Kimiyya da Fasaha ta Tarayya dake Bali, Jihar Taraba, ta bayyana cewa ta karɓi aikace-aikace fiye da 4,489 daga ’yan Najeriya da s**a nemi guraben aiki guda 98 da aka buɗe a makarantar.

Wannan bayani ya fito ne daga bakin Shugaban Gudanarwa na makarantar, Dr. Mohammed Usman, yayin taron majalisar gudanarwar makarantar da aka gudanar ranar Asabar, 24 ga watan Agusta, 2025.

Shugaban Gudanarwar ya ce an fitar da sanarwar neman aikin ne a jaridun Daily Trust da Punch ranar 2 ga Yuli, 2025, inda aka ba wa masu sha’awa damar tura takardunsu har zuwa ranar 13 ga Agusta, 2025, lokacin da aka rufe karɓar takardun.

Ya bayyana cewa, a halin yanzu makarantar za ta fara tantancewa da fitar da jerin sunayen wadanda s**a yi fice domin a ci gaba da matakin gaba na tattace masu neman aikin. Ya ce duk wadanda aka zaɓa za a sanar da su ta hanyar adireshin da s**a bayar ko kuma ta lambobin wayar da aka rubuta a takardunsu.

Dr. Usman ya kuma jaddada cewa cunkoson masu neman aikin ya nuna irin yawan matasa da ke neman aikin gwamnati a kasar, yana mai kira ga gwamnati da ta ƙara samar da hanyoyin rage zaman banza da ƙirƙirar ayyuka masu yawa ga ’yan kasa.

Al’amarin ya sake jaddada ƙalubalen rashin aikin yi da ke fuskantar matasa a Najeriya, inda daruruwan dubban masu karatun boko ke fafutukar samun damar aiki a gwamnati ko kamfanoni masu zaman kansu.

Majalisar Malamai ta Kasa ta Kai Ziyara ga Shugaban IZALA Sheikh Bala Lau a AbujaMajalisar Malamai ta Kasa (Nigerian Cou...
23/08/2025

Majalisar Malamai ta Kasa ta Kai Ziyara ga Shugaban IZALA Sheikh Bala Lau a Abuja

Majalisar Malamai ta Kasa (Nigerian Council of Ulama) ta kai ziyara ga Shugaban kungiyar Izalatul Bid’ah wa Iqamatus Sunnah (IZALA), Sheikh Bala Lau, a ofishinsa da ke Abuja.

Wannan ziyara ta haɗa manyan malamai daga kungiyoyin addinin Musulunci daban-daban a fadin ƙasar. A cewar shugabannin tawagar, manufar ziyarar ita ce karfafa haɗin kai tsakanin al’ummar Musulmi, domin a samu fahimtar juna, da kuma haɗa ƙarfi da ƙarfi wajen tunkarar manufofin Musulunci a fannoni daban-daban na rayuwa.

Sun yi addu’ar Allah Ya ƙara haɗa kan malamai da al’ummar Musulmi baki ɗaya, tare da tabbatar da zaman lafiya da ci gaban ƙasa.

HOTUNA: Sababbin Titunan unguwar Tumfure da Gwamna Inuwa Yahaya, ya shimfiɗa ya kuma sanya musu Wuta mai amfani da haske...
22/08/2025

HOTUNA: Sababbin Titunan unguwar Tumfure da Gwamna Inuwa Yahaya, ya shimfiɗa ya kuma sanya musu Wuta mai amfani da hasken Rana (Solar)

Sheikh Adam Muhammad Albany, fitaccen malamin addinin Musulunci a Nijeriya, ya yi kira ga gwamnatocin jihohi musamman na...
22/08/2025

Sheikh Adam Muhammad Albany, fitaccen malamin addinin Musulunci a Nijeriya, ya yi kira ga gwamnatocin jihohi musamman na yankin Arewa maso yamma da su rungumi hanyar sulhu da ’yan bindiga domin kawo karshen matsalar satar mutane tare da tabbatar da zaman lafiya a ƙasar.

Sheikh Albany ya bayyana haka ne yayin gabatar da huɗubar Juma’a a masallacin Miyetti da ke Bolari, Gombe, a yau Juma’a.

Ya ƙara da cewa yin sulhu na ɗaya daga cikin hanyoyin da za su iya taimaka wa al’umma samun kwanciyar hankali da tsaro. Malamin ya kuma yi fatan gwamnoni za su ɗauki wannan shawara da muhimmanci, domin ceto rayuka da dukiyoyin jama’a, kamar yadda Annabi Muhammadu (S.A.W) ya gudanar da Sulhun Hudaibiya da Yahudawa domin tabbatar da zaman lafiya a lokacin.

Haka kuma, Sheikh Albany ya yaba wa ƙoƙarin Sheikh Yusuf Asadussuna, wanda ke jagorantar kwamitin sasanta rikice-rikicen da ke da nasaba da ’yan bindiga a wasu jihohi. Ya ce irin wannan ƙoƙari na da matuƙar tasiri wajen ganin an dawo da zaman lafiya a ƙasar.

Kungiyar AID Group of Hisbah Pantami Yamma, ƙarƙashin jagorancin Ibrahim Labaran, ta gudanar da jerin ayyukan Da’awah da...
21/08/2025

Kungiyar AID Group of Hisbah Pantami Yamma, ƙarƙashin jagorancin Ibrahim Labaran, ta gudanar da jerin ayyukan Da’awah da wayar da kai a kasuwanni daban-daban na unguwar Pantami Yamma, Gombe.

A yayin aikin, ƙungiyar ta fara ne a bakin kasuwar bypass inda s**a yi wa iyaye mata masu sayar da hatsi nasiha kan muhimmancin kiyaye lokutan sallah duk da tsananin harkokin kasuwanci.

Bayan nan kuma, sun ziyarci masu sana’ar sayar da nono, inda s**a ja hankalinsu kan guje wa almundahana da hada nono da ruwa, tare da tunasar da su muhimmancin gaskiya da amana.

Haka kuma, ƙungiyar ta yi wa matasan da ke harkar tono yashi wa’azi kan kaucewa haramun da kuma kiyaye ibada.

A wani bangare na ziyara, Hisbah ta tuntubi masu sana’ar kaji, inda s**a yi musu nasiha kan kula da tsafta, kyautata yanka, da kuma gujewa jefa kaji a cikin ruwan zafi kafin su mutu gaba ɗaya.

Bugu da ƙari, Hisbah ta yi taro da ’yan dako da masu mashin mai tayu uku (Jega), inda ta jaddada musu illar tukin ganganci, tare da tunatar da su muhimmancin kiyaye sallah a matsayinsu na matasa.

Shugaban kungiyar, Ibrahim Labaran, ya ce: “Lallai ayyukan Hisbah suna da faɗi, kuma In Sha Allahu, za mu ci gaba da gudanar da su domin amfanin al’umma.”

Hukumar Rabon Kuɗaɗen Ƙasa (FAAC) tare da Hukumar Ƙididdiga ta Ƙasa (NBS), ta bayyana cewa jihohin Arewa Maso Gabas sun ...
21/08/2025

Hukumar Rabon Kuɗaɗen Ƙasa (FAAC) tare da Hukumar Ƙididdiga ta Ƙasa (NBS), ta bayyana cewa jihohin Arewa Maso Gabas sun karɓi jimillar fiye da Naira biliyan 745 daga watan Janairu zuwa Yuni na shekarar 2025.

Rahoton ya nuna cewa jihar Borno ce ta fi karɓar kaso mafi girma da ₦161.91 biliyan, sai Bauchi da ₦132.87 biliyan, da kuma Adamawa wadda ta samu ₦128.81 biliyan.

Yobe ta karɓi ₦115.45 biliyan, yayin da Taraba ta samu ₦112.60 biliyan, sai kuma Gombe wadda ta karɓi mafi ƙaranci da ₦93.47 biliyan kacal.

A cewar rahoton, waɗannan kuɗaɗen sun haɗa da rabon jihohi tare da hukumomin kananan hukumomin da ke ƙarƙashinsu.

Ana ganin wannan bayanin a matsayin wani ɓangare na shirin gwamnatin tarayya na Renewed Hope, domin tabbatar da gaskiya da wayar da kan jama’a kan yadda ake rarraba kuɗaɗen ƙasa.

Haka kuma, an shawarci al’umma da su ci gaba da sa idon yadda gwamnatocin jihohi ke amfani da kuɗaɗen domin inganta rayuwar jama’a.

TARON SHAN SHAYI: Ƙungiyar wakilan kafafen yaɗa labarai, ƙarƙashin Ƙungiyar ‘Yan Jarida ta Ƙasa (NUJ), reshen Jihar Kano...
21/08/2025

TARON SHAN SHAYI: Ƙungiyar wakilan kafafen yaɗa labarai, ƙarƙashin Ƙungiyar ‘Yan Jarida ta Ƙasa (NUJ), reshen Jihar Kano, ta gabatar da wani kwarya kwayar walima mai taken “Tea Break” domin ƙarfafa haɗin kai da zumunci a tsakanin membobinta.

Gwamnatin Jihar Kano ta taya Hafiz Sanusi Bukhari Idris murnar samun matsayi na uku a rukuni na Qirā’āt a gasar Qur’ani ...
21/08/2025

Gwamnatin Jihar Kano ta taya Hafiz Sanusi Bukhari Idris murnar samun matsayi na uku a rukuni na Qirā’āt a gasar Qur’ani ta King Abdulazeez International Qur’an Competition da aka gudanar a ƙasar Saudiyya.

A cikin wata sanarwa da Kwamishinan Yaɗa Labarai da Harkokin Cikin Gida, Kwamared Ibrahim Abdullahi Waiya, ya fitar a madadin Gwamna Abba Kabir Yusuf da al’ummar Kano, gwamnati ta bayyana wannan nasara a matsayin abin alfahari ga kansa da iyalinsa, da kuma girmamawa ga jihar Kano, Najeriya baki ɗaya, da al’ummar Musulmi.

Sanarwar ta nuna cewa wannan nasara ta sake haskaka sunan jihar Kano da Najeriya a idon duniya, tare da tabbatar da dogon tarihin ƙwarewar ilimin Qur’ani da Kano ta shahara da shi.

Gwamnatin ta yi addu’ar Allah ya ci gaba da jagorantar rayuwarsa tare da ba shi kariya, da kuma kara ɗaukaka shi wajen bauta wa addinin Musulunci da ɗan Adam gaba ɗaya.

Gwamnatin Amurka ta ce sabon mafi ƙarancin albashin Najeriya na N70,000 ba zai iya fitar da ma’aikata daga talauci ba sa...
21/08/2025

Gwamnatin Amurka ta ce sabon mafi ƙarancin albashin Najeriya na N70,000 ba zai iya fitar da ma’aikata daga talauci ba saboda tsananin matsin tattalin arziki da kuma faduwar darajar Naira.

A cikin rahoton hakkokin dan adam na 2024 da aka fitar a ranar 12 ga Agusta 2025, Ma’aikatar Harkokin Wajen Amurka ta nuna cewa albashin wanda darajarsa ta kai kusan dala $47.90 a wata, ya ragu ƙwarai saboda raguwar Naira fiye da N1,500 a kan kowace dala.

Rahoton ya kuma ce duk da an ninka albashin daga na baya, jihohi da dama ba sa aiwatar da shi saboda ƙarancin kuɗi, yayin da yawancin kamfanoni ƙanana da ke da ƙasa da ma’aikata 25 ba su cikin kariyar dokar.

Har ila yau, an bayyana cewa kashi 70–80% na ma’aikatan Najeriya suna cikin kasuwar da ba ta hukuma ba, inda dokokin albashi da aiki ba sa aiki yadda ya kamata.

Rahoton ya yi gargadi cewa ƙarancin masu sa ido kan aiki na barin miliyoyin ma’aikata cikin haɗarin cin zarafi da rashin samun albashi mai inganci.

Address

Gombe

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Al'umma Tv posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share