ADZ Hausa Tv

ADZ Hausa Tv ku na iya tuntubar mu a 07015067942.

Kafar watsa labarai ta ADZ Hausa Tv mallakin Kamfanin ADZ DIGITAL SOLUTIONS ce wadda za ta kawo muku Labaran Duniya, Rahotanni, Nishadi, Ra'ayoyi acikin awa 24.

Da ake ta hayya-hayya akan IPhone 17 dinnan, ni fa 16 din ma na ke son samu 😭, bani da wani dogon buri, ko kyauta aka ba...
23/09/2025

Da ake ta hayya-hayya akan IPhone 17 dinnan, ni fa 16 din ma na ke son samu 😭, bani da wani dogon buri, ko kyauta aka bani 17 din ma siyarwa zan yi na sai fili.🤣 Inji Fauziyya D. Sulaiman

DA DUMI-DUMI: Jami'ar Jihar Gombe Zata Kafa Kwalejin Koyon Aikin Gona Da Haɗin Gwiwar Jami'ar Michigan Na Kasar Amurka.G...
23/09/2025

DA DUMI-DUMI: Jami'ar Jihar Gombe Zata Kafa Kwalejin Koyon Aikin Gona Da Haɗin Gwiwar Jami'ar Michigan Na Kasar Amurka.

Gwamnan jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, ya amince da rattaba hannu kan takardar hadin gwiwa tare da Jami’ar Jihar Michigan (Michigan State University), ta kasar Amurka, wannan yarjejeniya za ta share fagen kafa Kwalejin koyon Aikin Gona a Jami’a Mallakar Jihar Gombe (GSU).

Gwamnan ya jagoranci wata tawaga zuwa jami'ar ta Michigan dake ƙasar ta Amurka a wani bangare na ziyarar aiki da nufin zurfafa hadin gwiwar kasa da kasa a fannin bunkasa noma da bincike da kuma kware akan sanin mak**ar aiki.

In bamu manta ba, a watannin da s**a gabata gwamna Inuwa ya amince da ware Naira biliyan 1.1 don kaddamar da Kwalejin aikin gona a garin Malam Sidi dake karamar hukumar Kwami.

Tuni Hukumar Kula da Jami’o’i ta Kasa (NUC) ta ba da izinin kafa kwalejin a hukumance, inda ake sa ran za a fara shirye-shiryen karatu na zangon 2025/2026

Daga Haji Shehu
S. A. Media

Gwamnan Jihar Rivers, Siminalayi Fubara, a jiya Litinin ya gana da Shugaba Bola Ahmed Tinubu a fadar shugaban kasa da ke...
23/09/2025

Gwamnan Jihar Rivers, Siminalayi Fubara, a jiya Litinin ya gana da Shugaba Bola Ahmed Tinubu a fadar shugaban kasa da ke Abuja.

Wannan shi ne karo na farko da shugaban kasa ya gana da gwamnan Rivers tun bayan dawo da shi kujerarsa, bayan ayyana dokar ta baci a jihar.

Da ya ke zantawa da manema labarai bayan ganawarsa da shugaban kasa, Fubara ya ce ya je fadar shugaban kasa ne domin sanar da Shugaba Tinubu cewa ya koma bakin aikinsa a matsayin gwamnan Rivers.

Ya ƙara da cewa, Shugaba Tinubu ya ba shi shawara kan yadda zai tafiyar da mulki domin kaucewa sake samun rikici a jihar.

Fubara ya bayyana cewa yanzu ya na aiki tare da jagororinsa, kuma an samu dawowar zaman lafiya a jihar.

Ya ce: “Kun sani an janye dakatarwar ne da tsakar dare ranar 17, ni kuma na dawo ranar 19. Don haka, abin da ya dace shi ne in ga shugaban kasa domin na gaya masa cewa na dawo bakin aiki kuma na koma gudanar da aikina a matsayin gwamnan Jihar Rivers.”

Kan abin da s**a tattauna, ya ce: “Ganawa ce ta uba da ɗa, inda na gode masa, sannan na roke shi idan akwai wani abin da zai iya zama matsala, ya ja hankalina yadda ya dace don kada mu sake shiga wani hali da zai jawo rikici. Shi ne kawai.”

Fubara ya ce shugaban kasa ya kuma ba shi shawarwari kan matakan da zai ɗauka a gaba da kuma yadda za a tafiyar da lamura cikin hanya madaidaiciya don tabbatar da zaman lafiya a jihar.

Ma'aikatar Muhalli da Sauyin Yanayi ta jihar Kano ta ci alwashin gyara ɗaukacin motocin kwashe shara da na sauran aiyuka...
23/09/2025

Ma'aikatar Muhalli da Sauyin Yanayi ta jihar Kano ta ci alwashin gyara ɗaukacin motocin kwashe shara da na sauran aiyuka da su ka lalace a ma'aikatar kula da shara ta jihar, REMASAB, kafin 2025 ta ƙare.

Kwamishinan Muhalli da Sauyin Yanayi Dakta Dahir Muhammad Hashim ne ya bada wannan tabbaci a ziyarar da ya kai ma'aikatar don duba yanayin da motocin aikin ke ciki a jiya Litinin.

A cewar Dakta Hashim, za a gyara motocin ne a karo na biyu na gyare-gyaren, inda ya baiyana cewa kamfanin Nigerian Trucks Manufacturing Company shi ne zai yi gyare-gyaren k**ar yadda ya yi a karon farko.

Kwamishinan ya ce wannan alkawari na nuna jajircewar gwamnati wajen ƙarfafa ayyukan kula da tsaftar muhalli a Kano da tabbatar da cewa hukumar na da dukkan kayan aiki da ake buƙata don sauke nauyin aikinta yadda ya k**ata.

"A yau na kai ziyarar aiki zuwa hukumar REMASAB inda na duba wasu daga cikin manyan motocin da s**a lalace waɗanda za a gyara a cikin zagaye na biyu na gyare-gyarenmu a kamfanin Nigerian Trucks Manufacturing Company.

" Wannan aikin yana cikin ƙoƙarinmu na ci gaba da farfaɗo da ayyukan wannan hukumar.

"Na tabbatar wa shugabanci da ma’aikatan REMASAB cewa duk sauran kayan aikin hukumar za a gyara su kuma su dawo cikin aiki kafin ƙarshen wannan shekara.

" Wannan alkawari na nuna jajircewarmu wajen ƙarfafa ayyukan kula da tsaftar muhalli a Kano da tabbatar da cewa hukumar tana da dukkan kayan aiki da ake buƙata don sauke nauyin aikinta yadda ya k**ata," in ji Dakta Hashim

Usman Dembele na ƙasar Faransa da ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Paris St Gamen ya lashe kyautar gwarzon ɗan ƙwallon ƙafa na d...
22/09/2025

Usman Dembele na ƙasar Faransa da ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Paris St Gamen ya lashe kyautar gwarzon ɗan ƙwallon ƙafa na duniya, wacce aka fi sani da Balon d'Or.

Dembele ya doke abokin burmin sa na kasar Spain da Barcelona, Lamine Yamal.

Dembele ya lashe kofuna hudu a PSG a kakar da ta gabata, sannan ya taka rawa gagaruma a gasar zakarun nahiyar Turai da PSG din ta kashe karo na farko a tarihin ƙungiyar.

Gwamnan jihar Yobe Mai Mala Buni ya samar da kabakin arziki na kayan abinci ga masu karamin karfi a daukacin kananan huk...
22/09/2025

Gwamnan jihar Yobe Mai Mala Buni ya samar da kabakin arziki na kayan abinci ga masu karamin karfi a daukacin kananan hukumomin jihar.

A karkashin shirin 2025 Governor Buni Food Basket Support Programme, Gwamnan ya gwangwaje al'ummar jihar da buhuna 50,000 na hatsi domin raba wa ga masu karamin karfi.

Gwamnan ya bayyana cewa wannan rabon na daga cikin shirin gwamnatin sa na inganta rayuwar mutanen Jihar Yobe musamman mabukata a dai-dai wannan lokacin da amfanin gona bai dawo gida ba.

Wannan taimakon ya biyo bayan gagarumin raban kayan noma da aka yi a gabanin daminar bana.

Kungiyoyin da s**a amfana sun haɗa da Malaman makarantun firamare 5,580, Ma’aikatan kiwon lafiya na karkara 1,780, Mutane masu bukata ta musamman 2,400, malaman Tsangaya 1,200, Kungiyar CAN, Miyetti Allah, kotal H**e da Kullen Allah 2,000.

Bugu da kari, Kananan Ma’aikatan gwamnati 4,000, Kananan Ma’aikatan asibitin koyarwa 600 sai Mutane masu ƙananan karfi a sassan jihar Yobe daga kananan hukumomi 25,500.

Gwamnatin jihar Gombe ta bayyana cewa za ta gurfanar da iyaye da masu kula da yara da s**a gaza tura su makaranta.Kwamis...
22/09/2025

Gwamnatin jihar Gombe ta bayyana cewa za ta gurfanar da iyaye da masu kula da yara da s**a gaza tura su makaranta.

Kwamishinan ilimi na jihar, ya ce matakin na daga cikin kudirin gwamnati na tabbatar da cewa kowane yaro na da damar samun ilimi, musamman a matakin farko da na sakandare.

Gwamnatin ta yi kira ga al'umma da su bada hadin kai wajen ganin an kawar da yawan yara da ke yawo ba tare da shiga makaranta ba.

DA DUMI-DUMI: Jami'an tsaro sun k**a matasa 3 masu shekaru 18 zuwa 22 da bindinga pistol a jihar Gombe.Rundunar ’yan san...
22/09/2025

DA DUMI-DUMI: Jami'an tsaro sun k**a matasa 3 masu shekaru 18 zuwa 22 da bindinga pistol a jihar Gombe.

Rundunar ’yan sanda ta jihar Gombe ta ce ta cafke wasu da ake zargi da aikata laifuka daban-daban ciki har da mallakar bindiga ba bisa ka’ida ba, sata da kuma fashin shanu.

A wata sanarwa da mai magana da yawun rundunar, DSP Buhari Abdullahi ya fitar, rundunar ta ce ta samu nasarar ne sak**akon samun bayanai daga jama’a da kuma aikin sintiri da jami’an ta ke gudanarwa a fadin jihar.

A cewar sanarwar:

A ranar 19 ga Satumba, jami’an tsaro sun cafke wasu matasa uku a unguwar Doma, bayan an k**a su da bindiga kirar pistol a hannunsu. Ana ci gaba da bincike a kansu.

Haka kuma, a ranar 18 ga Satumba, jami’an Operation Hattara sun damke wasu mutane hudu da ake zargi da satar sandunan ƙarfe 226 a Bauchi Road. Rundunar ta ce wadanda aka k**a sun amsa laifinsu.

A Bomala, Akko LGA, an cafke wani mutum mai suna Tukur Mohammed da ake zargi da satar babur, inda ya ce ya yi laifin tare da abokin sa wanda ya tsere.

Haka zalika, a Balanga LGA, wani saurayi mai suna Abubakar Auwal ya shiga hannu bayan ya amsa cewa shi da abokin aikinsa sun saci babur daga wani gida a Dassa Village.

Rundunar ta kuma ce an kwato shanu biyu da aka sace daga kauyen Talasse bayan an bi sawun su har zuwa wani kauye inda aka samu bas mai lamba ABUJA ABC 884 TU cike da igiyoyi da kayan da ake zargin na sata.

Kwamishinan ’yan sanda na jihar, CP Bello Yahaya, ya yaba wa jami’an rundunar bisa jajircewar su, tare da bukatar jama’a su ci gaba da bayar da bayanai domin dakile aikata laifuka a jihar.

Matasan da su ka yi fashi a Legas sun fada hannun ƴansanda a Kano Rundunar ƴansanda ta Jihar Kano ta ce ta cafke wasu ma...
22/09/2025

Matasan da su ka yi fashi a Legas sun fada hannun ƴansanda a Kano

Rundunar ƴansanda ta Jihar Kano ta ce ta cafke wasu matasa biyu da ake zargi da hannu a wani aika-aika na fashi da makami da kuma yunkurin kisa da ya faru a Bera Estate, Chevron, a jihar Legas.

A cewar rundunar, dakarunta na musamman sun k**a mutanen ne a ranar 11 ga Satumba, 2025, a unguwar Na’ibawa, bisa sahihan bayanan sirri da su ka samu.

Waɗanda aka k**a da sun haɗa da Mathew Adewole, mai shekaru 25, daga unguwar Na’ibawa da kuma Mukhtar Muhammad, mai shekaru 31, dan unguwar Unguwa Uku, Kano.

‘Yansanda sun ce Adewole ya amsa laifin kai hari kan wani mazaunin Bera Estate da aka bayyana da suna Lil-Kesh a ranar 19 ga Agusta, 2025.

A yayin harin, Lil-Kesh ya samu mummunan rauni a wuyansa yayin harin, amma daga bisani ya mutu, sannan ana zargin matasan da tilasta wa wanda aka kai wa harin ya aika Naira miliyan 2 da dubu 120 daga asusunsa ta waya zuwa asusun Mukhtar Muhammad.

Mai magana da yawun rundunar, SP Abdullahi Haruna Kiyawa, a cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Asabar, ya ce wannan nasara ta samu ne sak**akon ingantaccen tsarin binciken sirri da haɗin gwiwa da al’umma, bisa umarnin Sufeto Janar na ‘Yan Sanda, Kayode Adeolu Egbetokun.

Ya ƙara da cewa an riga an mika waɗanda ake zargin ga Rundunar ‘Yan Sanda ta Jihar Lagos don ci gaba da bincike da kuma gurfanar da su a kotu.

An Nada Ganduje A Matsayin Khaldimul Islam Na Kasa Baki DayaHadakar kungiyoyin Alarammomi da Mahaddata ne s**a yi masa n...
21/09/2025

An Nada Ganduje A Matsayin Khaldimul Islam Na Kasa Baki Daya

Hadakar kungiyoyin Alarammomi da Mahaddata ne s**a yi masa nadin a yau Lahadi.

Ma’aikatar Muhalli da Sauyin Yanayi, karkashin jagorancin Kwamishina Dahir M. Hashim, ta ɗauki wani mataki na ci gaba wa...
21/09/2025

Ma’aikatar Muhalli da Sauyin Yanayi, karkashin jagorancin Kwamishina Dahir M. Hashim, ta ɗauki wani mataki na ci gaba wajen karfafawa al’umma da kuma farfado da muhalli.

A ranar 9 ga Satumba, 2025, a Dawakin Tofa, ma'aikatar ta raba jimillar bishiyar mangwaro guda 3,000 masu yalwar ƴaƴa ga matan karkara

A wata sanarwa da ma'aikatar ta fitar, an ƙaddamar da shirin ne karkashin jagorancin Anas Ibrahim Danmaliki, shugaban ƙaramar hukumar Dawakin-Tofa.

Ma'aikatar ta ce an ƙaddamar da wannan shiri ne domin inganta lafiyar abinci a cikin gida, ƙara samun kudin shiga ga iyali, da kuma ƙarfafa juriya ga sauyin yanayi, tare da bayar da gudunmawa wajen farfado da muhalli a duk fadin jihar.

Ma'aikata ta ce za cimma muradun shirin ta hanyar baiwa mata kayan da za su iya ci gaba da amfani da su, inda ta ƙara tabbatar da alkawuranta na gina al’ummomi masu lafiya da kuma samar da jihar Kano mai cike da koren ganyaye.

Ta ce matan da su ka amfana da shirin sun nuna farin cikinsu da murna tare da alkawarin amfana da shirin ta hanyar da ya dace.

TA LEƘO TA KOMA:Jami’ar European-American ta fitar da sanarwa da ta ke barranta kan ta da digirin girmamawa da aka baiwa...
21/09/2025

TA LEƘO TA KOMA:

Jami’ar European-American ta fitar da sanarwa da ta ke barranta kan ta da digirin girmamawa da aka baiwa shahararren mawaki, Dauda Kahutu Rarara ba, inda ta ce ba da izinin ta kuma ba ta yarjewa kowa ya bada digiri ga mawaƙin ba.

A wani taro da aka shirya a otal din Nicon Luxury a Abuja a jiya Asabar, wanda gwamnan jihar Katsina, Dikko Radda, ya halarta tare da wasu manyan baki, an baiwa Rarara wannan digiri na girmamawa ta hannun wasu mutane da s**a nuna kansu a matsayin wakilan jami’ar.

Amma a cikin wata sanarwa da ta wallafa a shafin ta na yanar gizo, muhukuntan jami’ar sun nisanta kan su da Rarara da kuma jami’an da s**a nuna kansu a matsayin wakilan jami’ar.

"Jami’ar ba ta ba da izinin gudanar da wani bikin kammala karatu a wannan wuri a yau ba, kuma wannan taron an shirya shi ne ta hanyar damfara ba tare da sanin jami’ar ba ko amincewarta.

" Wadanda s**a shirya wannan taron sun yaudari wasu mutane cewa su ne wakilan Jami’ar European-American, amma wannan ba gaskiya ba ne, kuma ba su da wani hurumin yin hakan ko karbar kudi a madadin jami’ar," in ji sanarwar.

Address

Gombe

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when ADZ Hausa Tv posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share