22/09/2025
Matasan da su ka yi fashi a Legas sun fada hannun ƴansanda a Kano
Rundunar ƴansanda ta Jihar Kano ta ce ta cafke wasu matasa biyu da ake zargi da hannu a wani aika-aika na fashi da makami da kuma yunkurin kisa da ya faru a Bera Estate, Chevron, a jihar Legas.
A cewar rundunar, dakarunta na musamman sun k**a mutanen ne a ranar 11 ga Satumba, 2025, a unguwar Na’ibawa, bisa sahihan bayanan sirri da su ka samu.
Waɗanda aka k**a da sun haɗa da Mathew Adewole, mai shekaru 25, daga unguwar Na’ibawa da kuma Mukhtar Muhammad, mai shekaru 31, dan unguwar Unguwa Uku, Kano.
‘Yansanda sun ce Adewole ya amsa laifin kai hari kan wani mazaunin Bera Estate da aka bayyana da suna Lil-Kesh a ranar 19 ga Agusta, 2025.
A yayin harin, Lil-Kesh ya samu mummunan rauni a wuyansa yayin harin, amma daga bisani ya mutu, sannan ana zargin matasan da tilasta wa wanda aka kai wa harin ya aika Naira miliyan 2 da dubu 120 daga asusunsa ta waya zuwa asusun Mukhtar Muhammad.
Mai magana da yawun rundunar, SP Abdullahi Haruna Kiyawa, a cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Asabar, ya ce wannan nasara ta samu ne sak**akon ingantaccen tsarin binciken sirri da haɗin gwiwa da al’umma, bisa umarnin Sufeto Janar na ‘Yan Sanda, Kayode Adeolu Egbetokun.
Ya ƙara da cewa an riga an mika waɗanda ake zargin ga Rundunar ‘Yan Sanda ta Jihar Lagos don ci gaba da bincike da kuma gurfanar da su a kotu.