ABM Hausa News

ABM Hausa News Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from ABM Hausa News, Media/News Company, No. 10, Pantami Quarters Near, , Water Board, Gombe.

"Arewa Bridge Media (ABM) is a news agency that presents programs relating to current affairs in Hausa language, owned by ABM VIRTUAL PRODUCTIONS LTD."

🔗 Follow us on our other social media platforms:
👇 👇👇
https://linktr.ee/arewabrigemedia

"Tun da naga Atiku yana goyon bayan Arsenal hankali na ya kwanta. Don na san shi da Villa har abada" -Cewar Dan Bello Me...
08/05/2025

"Tun da naga Atiku yana goyon bayan Arsenal hankali na ya kwanta. Don na san shi da Villa har abada" -Cewar Dan Bello

Me kuke ganin yasa Ɗan Bello yafadi haka?

YANZU-YANZU: Gwamnan Jihar Kano, Injiniya Abba Kabir Yusuf, ya bayar da gudummawar Naira miliyan 15 domin ci gaba da jin...
06/05/2025

YANZU-YANZU: Gwamnan Jihar Kano, Injiniya Abba Kabir Yusuf, ya bayar da gudummawar Naira miliyan 15 domin ci gaba da jinyar Halisa Muhd, wata maras lafiya da ke fama da cutar daji (cancer).

Ba Ni Da Masaniya Akan Allon Da Aka Rubuta Katsina Ba Korafi, Domin Ba Da Yawuna Aka Kafe Shi Ba, Inji Gwamna Dikko Radd...
06/05/2025

Ba Ni Da Masaniya Akan Allon Da Aka Rubuta Katsina Ba Korafi, Domin Ba Da Yawuna Aka Kafe Shi Ba, Inji Gwamna Dikko Radda

Hukumomi sun tabbatar da faruwar lamarin kuma ana ci gaba da bincike. Al’ummar yankin na kira da a ƙara tsaro don hana s...
06/05/2025

Hukumomi sun tabbatar da faruwar lamarin kuma ana ci gaba da bincike. Al’ummar yankin na kira da a ƙara tsaro don hana sake faruwar irin haka.

INNALILLAHI WAINNA ILAIRRAJU'UN: Allah yayiwa Mahaifin jarumin fina-finan Hausa Daddy Hikima (Abale) ya rasuwa.
05/05/2025

INNALILLAHI WAINNA ILAIRRAJU'UN: Allah yayiwa Mahaifin jarumin fina-finan Hausa Daddy Hikima (Abale) ya rasuwa.

Tsakanin Rarara da Nazuru Sarkin Waka Waye Yafi biya Waka?
05/05/2025

Tsakanin Rarara da Nazuru Sarkin Waka Waye Yafi biya Waka?

Hukumar JAMB ta fitar da sakamakon jarabawar UTME ta shekarar 2025, inda aka bayyana cewa fiye da dalibai miliyan 1.5 da...
05/05/2025

Hukumar JAMB ta fitar da sakamakon jarabawar UTME ta shekarar 2025, inda aka bayyana cewa fiye da dalibai miliyan 1.5 daga cikin miliyan 1.7 da s**a rubuta jarabawar sun kasa samun maki 200. Wannan ya jawo damuwa kan irin ƙalubalen da ake fuskanta a fannin ilimi, tare da kira ga gwamnati da masu ruwa da tsaki su ɗauki matakan gyara.

Tsoffin ‘Yan Takarar Kansila na 2024 Sun Jaddada Go­yon Bayan Su ga Gwamnatin Inuwa Yahaya da APC a 2027A yammacin jiya ...
05/05/2025

Tsoffin ‘Yan Takarar Kansila na 2024 Sun Jaddada Go­yon Bayan Su ga Gwamnatin Inuwa Yahaya da APC a 2027

A yammacin jiya Lahadi, tsoffin ‘yan takarar kansiloli na shekarar 2024 sun gudanar da wani taro a cikin garin Gombe domin ƙarfafa zumunci da haɗa kai wajen fuskantar ƙalubale da matsalolin siyasa da s**a addabi mambobin jam’iyyar.

Taron ya samu halartar wasu daga cikin tsoffin ‘yan takarar da ba su samu nasara ba a zaɓen kananan hukumomi na 2024. Sun kuma jaddada aniyar su na ci gaba da ba da gudummawa ga gwamnatin H.E Muhammadu Inuwa Yahaya (Dan Majen Gombe), domin cikar wa’adin sa lafiya da kuma samun nasarar takararsa ta Sanata a 2027.

Sun yi kira ga sauran abokan tafiya da su haɗa kai domin ciyar da jam’iyyar APC gaba tare da fatan Allah ya kawo nasara mai albarka.

✍️
Gombe L.G.A Aspirant Councillors Forum 2020/2024
04-05-2025

Da me kake tuna Marigayi Alhaji Umaru Musa Yar'Adua, bayan shekaru 15 da rasuwarsa?
05/05/2025

Da me kake tuna Marigayi Alhaji Umaru Musa Yar'Adua, bayan shekaru 15 da rasuwarsa?

ALLAHU AKBAR: Marigayi Tsohon Shugaban kasar Najeriya Alhaji Ummaru Musa Yar Addu'a Ya Cika Shekara 15 Da Rasuwa.A yau, ...
05/05/2025

ALLAHU AKBAR: Marigayi Tsohon Shugaban kasar Najeriya Alhaji Ummaru Musa Yar Addu'a Ya Cika Shekara 15 Da Rasuwa.

A yau, 5 ga Mayu 2025, Najeriya na tuna da cika shekaru 15 da rasuwar tsohon shugaban ƙasa, Alhaji Umaru Musa Yar’Adua, wanda ya rasu a ranar 5 ga Mayu, 2010. An yi jana’izarsa a mahaifarsa Katsina, inda dubban mutane s**a halarta.

Yar’Adua, wanda ya kasance gwamna na jihar Katsina daga 1999 zuwa 2007 kafin ya zama shugaban ƙasa, ya shahara da gaskiya, adalci da son talakawa. A lokacin mulkinsa ya ƙaddamar da shirin sulhu a Neja Delta da kuma ajandar maki bakwai don cigaban ƙasa.

A yau, ana ci gaba da tuna shi da girmamawa daga 'yan Najeriya da dama, suna masa addu’a tare da yi masa fatan rahamar Allah.

Muna Addu'ar Ubangiji ya masa Rahama

Gwamna Uba Sani Ya Raba Motoci Ga Sarakuna 19 a Jihar KadunaA wani muhimmin mataki na tallafa wa shugabannin gargajiya a...
05/05/2025

Gwamna Uba Sani Ya Raba Motoci Ga Sarakuna 19 a Jihar Kaduna

A wani muhimmin mataki na tallafa wa shugabannin gargajiya a Jihar Kaduna, Gwamna Uba Sani ya raba motoci ga Sarakuna da Hakimai guda 19 a ranar 4 ga Mayu, 2025.

Wannan shiri ya kasance sakamakon haɗin gwiwa tsakanin Gwamnatin Jihar Kaduna, Ofishin Shugaban Majalisar Wakilai na Ƙasa da Hukumar Raya Ƙananan da Matsakaitan Masana’antu ta Najeriya (SMEDAN).

Gwamna Uba Sani ya bayyana godiyarsa ga Shugaban Majalisar Wakilai, Rt. Hon. Tajudeen Abbas, bisa tallafin da ya bayar domin ganin an sauƙaƙa matsalolin sufuri da ke addabar Sarakunansu. Ya bayyana cewa SMEDAN ta amsa kiran da aka yi da hannu biyu wajen kawo wannan sauƙi.

Hakazalika, Gwamnan ya yaba da gudunmawar Sarakunan gargajiya wajen ƙarfafa zaman lafiya da ci gaba a cikin jihar. Ya jaddada cewa gwamnati za ta ci gaba da kulawa da walwalar Sarakuna domin ƙara musu ƙwarewa da tasiri a ayyukansu na yau da kullum.

Address

No. 10, Pantami Quarters Near, , Water Board
Gombe

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when ABM Hausa News posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share