ABM Hausa News

ABM Hausa News Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from ABM Hausa News, Media/News Company, No. 10, Pantami Quarters Near, , Water Board, Gombe.

"Arewa Bridge Media (ABM) is a news agency that presents programs relating to current affairs in Hausa language, owned by ABM VIRTUAL PRODUCTIONS LTD."

🔗 Follow us on our other social media platforms:
👇 👇👇
https://linktr.ee/arewabrigemedia

TAKAITACCEN RAHOTO:Dan Majalisar Tarayya daga Jihar Kano, Hon. Alhassan Ado Doguwa, ya ce zaman Majalisar bai da amfani ...
25/11/2025

TAKAITACCEN RAHOTO:
Dan Majalisar Tarayya daga Jihar Kano, Hon. Alhassan Ado Doguwa, ya ce zaman Majalisar bai da amfani a yanzu, yana mai kira da a rufe zaman har sai an magance matsalar tsaro a Najeriya. Ya bayyana hakan ne a yau yayin zaman Majalisar Tarayya, inda ya jaddada cewa dole a ɗauki mataki mai ƙarfi domin kare rayukan ‘yan kasa.

DA DUMI-DUMI: Gwarazan dakarun Sojin Saman Najeriya sun fara gudanar da sintiri na awanni 24 babu dakatawa, bisa umarnin...
25/11/2025

DA DUMI-DUMI: Gwarazan dakarun Sojin Saman Najeriya sun fara gudanar da sintiri na awanni 24 babu dakatawa, bisa umarnin Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu. Wannan mataki na zuwa ne domin ƙara tsaurara tsaro, ganin yadda matsalar garkuwa da mutane ke ƙaruwa musamman a Jihar Kwara da wasu sassan ƙasar.

Shugaban ƙasar ya bayar da umarnin a tashi da jiragen yaki na musamman domin sa ido a dukkanin yankunan da aka fi samun barazana, tare da tabbatar da cewa ana ci gaba da sintiri a ko da yaushe don kare rayuka da dukiyoyin al’umma.

Tsayuwar Daka a Ibadan: Yadda Kauran Bauchi, Dauda Lawal da Makinde S**a Ceto Mutuncin Jam'iyyar PDPA babban taron da ja...
21/11/2025

Tsayuwar Daka a Ibadan: Yadda Kauran Bauchi, Dauda Lawal da Makinde S**a Ceto Mutuncin Jam'iyyar PDP

A babban taron da jam’iyyar PDP ta gudanar a Ibadan ranar Asabar da ta gabata, an ga wani sabon salo na shugabanci da jajircewa wanda ya tabbatarwa ‘yan Najeriya cewa PDP har yanzu tana da waɗanda za su tsaya tsayin daka domin kare darajarta.

A cikin waɗanda s**a fito fili wajen nuna wannan kwazo, akwai Kauran Bauchi, wanda ya jagoranci aikin gyara da tsaftace jam’iyya da tsantseni. Tsayuwarsa wajen korar masu tada zaune tsaye a ciki, musamman waɗanda ke aiki da boyayyun manufa don rusa jam’iyyar daga cikin gida, ya zama abin yabo da koyi. A gaskiya, Kauran Bauchi ya zama ginshiƙin da ya hana jam’iyyar durkushewa.

Baya ga haka, Gwamnan Zamfara Dr. Dauda Lawal ya nuna irin kishinsa ga dimokuraɗiyya. Goyon bayansa ga sahihin tsari da adalci a cikin jam’iyya ya karfafa gwiwar mambobi da magoya baya, ya tabbatar masu cewa PDP na da shugabanni da ba za su lamunci karya ko shisshigi ba.

A bangaren Seyi Makinde, Gwamnan jihar Oyo, ya ba da cikakken gudunmawa wajen tabbatar da cewa taron Ibadan ya kasance sahihi, kuma cikin tsarin da ya dace. Makinde ya tabbatar da cewa jam’iyya ta gudana bisa ka’ida, ba tare da batan batu ko rikice-rikice ba, aikin da ya kara tabbatar da cewa PDP jam’iyyar da take da ni’imar shugabanni masu hangen nesa.

A tare, waɗannan manyan shugabanni uku sun yi abin da ake kira ceto martabar PDP, tare da dawo da yarda da kwarin gwiwar jama’a. Sun nuna cewa jam’iyyar adawa ba ta mutu ba, kuma ba za ta mutu ba, muddin akwai shugabanni irin su Kauran Bauchi, Dr. Dauda Lawal da Seyi Makinde.

A Ibadan, PDP ta sake tsayawa kan kafafunta kuma hakan ya sake busawa dimokuraɗiyya a rai.

INEC Tayi Watsi Da Buƙatar Masu Yiwa PDP Zagon Kasa, Ta Tabbatar Da Damagun a Matsayin Shugaban Jam'iyyar Daga Jimoh Ism...
19/11/2025

INEC Tayi Watsi Da Buƙatar Masu Yiwa PDP Zagon Kasa, Ta Tabbatar Da Damagun a Matsayin Shugaban Jam'iyyar

Daga Jimoh Isma'il Adetunji

Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC) ta tabbatar da cewa Kwamitin Gudanarwa na Ƙasa (NWC) na jam’iyyar PDP ƙarƙashin jagorancin shugaban jam’iyya na ƙasa Kabiru Tanimu Turaki (SAN) ita ce hukuma ɗaya tilo da ta dace a doka.

INEC ta ƙi yarda da takardar bogi da wasu korarru Mohammed Abdulrahman da Samuel Anyanwu s**a aika suna kiran a dage zaben fidda gwani na gwamnan Jihar Ekiti, matakin da ya fallasa yunƙurinsu na rugujewa jam’iyyar adawa ta ƙasa ta hanyar karya doka da son zuciya.

INEC ta jaddada cewa wannan takardar da waɗannan haramtattun shugabanni s**a turo a ranar 6 ga Nuwamba, 2025, ba ta da wani inganci. Su kansu sun yi ikirarin shugabanci ne bisa ƙarya, inda s**a jingina dalilan karya na wai “matsalolin shirye-shirye” domin su kawo tangarda ga zaɓen ranar 8 ga Nuwamba.

Hukumar ta bayyana a fili cewa kawai sa hannun shugaban jam’iyya na ƙasa da sakataren ƙasa na halastattaccen NWC ne ake karɓa a hukumance.

Matakin INEC ya yi daidai da hukuncin da jam’iyyar PDP ta yanke tun farko na dakatar da Anyanwu, Abdulrahman da wasu abokan aikinsu a ranar 1 ga Nuwamba, 2025 saboda aikata laifukan karya tsarin jam’iyya, wanda ya sabawa sassan 57(3), 58(1)(a)(b)(c)(h), da 59(1) na kundin tsarin PDP (2017 da aka gyara).

Wadannan hukunci an tabbatar da su ne a babban taron jam’iyyar da aka yi a Ibadan a ranar 15 ga Nuwamba, 2025, inda aka zaɓi Barrister Tanimu Turaki a matsayin sabon shugaban jam’iyya na ƙasa, tare da tsige manyan masu tada fitina ciki har da Anyanwu, Abdulrahman, Nyesom Wike da Ayo Fayose saboda aikata manyan laifuka na tafka ayyukan adawa da jam’iyyar, ƙirƙiro bangarori, da amfani da kotu wajen rugujewa jam’iyya.

Gamayyar Kungiyoyin Arewacin Najeriya Ta Soki Shirye-shiryen Zanga-zangar Neman Sakin Nnamdi KanuKungiyar Gamayyar Kungi...
19/10/2025

Gamayyar Kungiyoyin Arewacin Najeriya Ta Soki Shirye-shiryen Zanga-zangar Neman Sakin Nnamdi Kanu

Kungiyar Gamayyar Kungiyoyin Arewacin Najeriya (CNG) ta bayyana adawa da s**a mai tsanani kan shirin gudanar da zanga-zangar neman a saki shugaban ƙungiyar IPOB da aka haramta, Nnamdi Kanu.

CNG ta ce wannan yunkuri da wasu shugabannin siyasa da na al’ada na kabilar Igbo, da masu kiran kansu ‘yan gwagwarmaya kamar Omoyele Sowore, ke jagoranta tare da wasu ‘yan Arewa marasa kishin ƙasa wani makirci ne na yi wa ƙasa karan tsaye da barazana ga zaman lafiya da doka.

Kungiyar ta bayyana cewa Nnamdi Kanu da IPOB sun haifar da mutuwar fiye da mutane 1,200 ciki har da jami’an tsaro sama da 400, sun ƙone ofisoshin ‘yan sanda fiye da 100, kuma sun jawo asarar dukiya da ta haura ₦450 biliyan a Kudu maso Gabas.

CNG ta tunatar da cewa tun daga 2016 Kanu ya kasance mai yada ƙiyayya, tashin hankali da rarrabuwar kai ta hanyar IPOB da rundunarsa ta ESN, inda aka kashe ‘yan Arewa da dama, aka lalata kasuwanci, tare da hana zaman lafiya.

Kungiyar ta kuma yi kira ga gwamnatin tarayya ta tabbatar da shari’ar Kanu ta tafi yadda doka ta tanada ba tare da matsin lamba na siyasa ba, tare da bukatar jami’an tsaro su hana duk wata zanga-zangar da zata kawo tashin hankali.

CNG ta gargadi ‘yan siyasa da masu daukar nauyin zanga-zangar da cewa za a bincike su, tare da kira ga Shugaba Bola Ahmed Tinubu da kada ya bari a yi masa barazana wajen yin doka bisa ra’ayi ko jin kai.

A ƙarshe, CNG ta jaddada cewa sakin Nnamdi Kanu ba zai kawo zaman lafiya ba, sai dai ya kara dagula ƙasa da karya tsarin shari’a. Ƙasar da ba ta mutunta doka ba, ba za ta samu zaman lafiya ba.

Sa hannu:
Comrade Jamilu Aliyu Charanchi
Koodineta Na Ƙasa, CNG
Abuja, Najeriya

Al'umma A Jihar Imo Sun Yiwa El'rufai Tofin Alatsine, Sun Yi Watsi Da Shi Tare Da Nuna Ƙyma Da Irin SiyasarsaDaga Abdul-...
09/09/2025

Al'umma A Jihar Imo Sun Yiwa El'rufai Tofin Alatsine, Sun Yi Watsi Da Shi Tare Da Nuna Ƙyma Da Irin Siyasarsa

Daga Abdul-Azeez Suleiman

Nasir El-Rufai, tsohon gwamnan Kaduna, ya gamu da zanga-zangar ƙin karɓarsa a Owerri, Jihar Imo, lokacin da ya halarci Taron Odenigbo 2025 a Assumpta Cathedral. Jama’a sun fito da kwalaye da ƙorafe-ƙorafe, suna zarginsa da kalaman wariya kan kabilar Igbo a baya.

Wannan martani bai tsaya kan shi kaɗai ba, ya kuma fito da tsohuwar matsalar rashin haɗin kai, raunin Yaƙin Basasa, da kuma gajiyar jama’a ga shugabannin da ake ganin sun rabu da halin rayuwar talakawa.

Masu zanga-zangar har sun yi kira ga a tsawatar wa Peter Obi saboda kusancinsa da shi, abin da ya nuna cewa kowane ɗan siyasa na iya fuskantar tambaya muddin yana da alaƙa da mutanen da ake kallon masu raba kan ƙasa.

Zanga-zangar ta zama alamar cewa jama’a na da ƙarfi wajen kalubalantar manyan ‘yan siyasa, musamman a wannan zamani na kafafen sada zumunta. Darasin da ke ciki shi ne shugabanni su daina rarrabuwar kawuna, su rungumi tattaunawa, su girmama tarihi, domin kawai haka za a samu haɗin kan ƙasa mai bambance-bambance.

Jama’a Sun Yi Masa Watsi, Sun Nuna Ƙiyayya da Siyasar Rarrabuwar irin ta El'rufai, sun kuma shawarci Peter Obi da ya gaggauta nesanta kansa da El'rufai don tsira da mutuncinsa.

"Tun da naga Atiku yana goyon bayan Arsenal hankali na ya kwanta. Don na san shi da Villa har abada" -Cewar Dan Bello Me...
08/05/2025

"Tun da naga Atiku yana goyon bayan Arsenal hankali na ya kwanta. Don na san shi da Villa har abada" -Cewar Dan Bello

Me kuke ganin yasa Ɗan Bello yafadi haka?

YANZU-YANZU: Gwamnan Jihar Kano, Injiniya Abba Kabir Yusuf, ya bayar da gudummawar Naira miliyan 15 domin ci gaba da jin...
06/05/2025

YANZU-YANZU: Gwamnan Jihar Kano, Injiniya Abba Kabir Yusuf, ya bayar da gudummawar Naira miliyan 15 domin ci gaba da jinyar Halisa Muhd, wata maras lafiya da ke fama da cutar daji (cancer).

Ba Ni Da Masaniya Akan Allon Da Aka Rubuta Katsina Ba Korafi, Domin Ba Da Yawuna Aka Kafe Shi Ba, Inji Gwamna Dikko Radd...
06/05/2025

Ba Ni Da Masaniya Akan Allon Da Aka Rubuta Katsina Ba Korafi, Domin Ba Da Yawuna Aka Kafe Shi Ba, Inji Gwamna Dikko Radda

Hukumomi sun tabbatar da faruwar lamarin kuma ana ci gaba da bincike. Al’ummar yankin na kira da a ƙara tsaro don hana s...
06/05/2025

Hukumomi sun tabbatar da faruwar lamarin kuma ana ci gaba da bincike. Al’ummar yankin na kira da a ƙara tsaro don hana sake faruwar irin haka.

INNALILLAHI WAINNA ILAIRRAJU'UN: Allah yayiwa Mahaifin jarumin fina-finan Hausa Daddy Hikima (Abale) ya rasuwa.
05/05/2025

INNALILLAHI WAINNA ILAIRRAJU'UN: Allah yayiwa Mahaifin jarumin fina-finan Hausa Daddy Hikima (Abale) ya rasuwa.

Tsakanin Rarara da Nazuru Sarkin Waka Waye Yafi biya Waka?
05/05/2025

Tsakanin Rarara da Nazuru Sarkin Waka Waye Yafi biya Waka?

Address

No. 10, Pantami Quarters Near, , Water Board
Gombe

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when ABM Hausa News posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share