25/02/2026
Ina Ka Ke Lokacin Da El-Rufai Ke Gallazawa Mutane Da Sace Dukiyar Al'ummar Jihar Kaduna ~ KVU Ta Caccaki Atiku Abubakar
Ƙungiyar Kaduna Voices United (KVU), wadda ta yi fice wajen tabbatar da anyi gaskiya, riƙon amana da adalci a harkokin mulki, ta yi martani kan kalaman da Atiku Abubakar da yayi dangane da tsare tsohon gwamnan Kaduna State, Nasir El-Rufai.
KVU ta bayyana cewa duk da cewa damuwa kan lafiyar El-Rufai abu ne mai muhimmanci, akwai tambaya kan dalilin da ya sa irin wannan ƙwazo wajen neman gaskiya da rikon amana bai bayyana ba a lokacin da yake kan mulki, lokacin da ake ta zarge-zargen sa da cin hanci, tauye haƙƙin jama’a da kuma amfani da iko wajen tsoratar da masu adawa. A cewarsu, nuna damuwa yanzu kaɗai na iya zama misali na son zuciya da rashin daidaito a siyasa.
Ƙungiyar ta jaddada cewa El-Rufai na fuskantar tuhume-tuhume masu tsanani daga Department of State Services (DSS), wanda ya shigar da ƙara uku a Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja. Tuhume-tuhumen sun shafi zargin sa da yin satar bayanan waya ba bisa ƙa’ida ba, rashin kai rahoton bayanan da aka ce ya samu, da kuma jefa tsaron ƙasa cikin haɗari, zarge-zargen da s**a samo asali daga wata hira da ya yi a tashar Arise TV inda ya yi iƙirarin samun damar sauraron wayoyin mai bawa shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro.
Haka kuma, yana ƙarƙashin bincike daga Economic and Financial Crimes Commission (EFCC) kan zargin karkatar da kuɗaɗen jama’a da s**a kai kimanin naira biliyan 432, ciki har da kuɗaɗen da ake alaƙantawa da wasu manyan ayyuka kamar na layin dogo na Kaduna. Bugu da ƙari, Independent Corrupt Practices and Other Related Offences Commission (ICPC) na bincike kan zargin cin zarafin ofis da kuma take dokokin saye da bayar da kwangila.
KVU ta bayyana cewa waɗannan zarge-zarge ba ƙananan batutuwa ba ne, domin sun shafi tsaron ƙasa, dukiyar jama’a, da kuma amincewar al’umma ga shugabanci. Don haka, ƙungiyar ta yi gargadin cewa yunƙurin wanke El-Rufai daga waɗannan matsaloli kafin kammala bincike da shari’a zai iya tauye tsarin dimokuraɗiyya da ƙa’idar cewa babu wanda ya fi ƙarfin doka.
A ƙarshe, ƙungiyar ta buƙaci gwamnatin tarayya ta tabbatar da bin doka da oda wajen tsarewa da shari’ar El-Rufai, tare da bayyana gaskiya game da halin da yake ciki. Sun kuma yi kira ga shugabannin siyasa da su guji nuna son kai, su fifita gaskiya da adalci sama da alaƙar siyasa, domin tabbatar da cewa Najeriya ta samu shugabanci mai tsafta da rikon amana.
Sa hannun
Yusuf Dama'i
Secretary KVU